< Ézéchiel 28 >

1 La parole de l'Eternel me fut encore [adressée], en disant:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Fils d'homme, dis au conducteur de Tyr: ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: parce que ton cœur s'est élevé et que tu as dit: je suis le [Dieu] Fort, et je suis assis dans le siège de Dieu, au cœur de la mer, quoique tu sois un homme, et non le [Dieu] Fort, et parce que tu as élevé ton cœur comme si tu étais un Dieu.
“Ɗan mutum, ka faɗa wa mai mulkin Taya cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Cikin alfarmar zuciyarka ka ce, “Ni allah ne; ina zama a kan kursiyin allah a tsakiyar tekuna.” Amma kai mutum ne ba allah ba, ko da yake ka ɗauka kana da hikima kamar allah.
3 Voici, tu es plus sage que Daniel, rien de caché ne t'a été rendu obscur.
Ka fi Daniyel hikima ne? Ba asirin da yake ɓoye a gare ka?
4 Tu t'es acquis de la puissance par ta sagesse et par ta prudence; et tu as assemblé de l'or et de l'argent dans tes trésors.
Ta wurin hikimarka da ganewarka ka sami dukiya wa kanka ka kuma tara zinariya da azurfa cikin wuraren ajiyarka.
5 Tu as multiplié ta puissance par la grandeur de ta sagesse dans ton commerce, puis ton cœur s'est élevé à cause de ta puissance.
Ta wurin dabararka mai girma cikin kasuwanci ka ƙara dukiyarka, kuma saboda dukiyarka zuciyarka ta cika da alfarma.
6 C'est pourquoi le Seigneur l'Eternel dit ainsi: parce que tu as élevé ton cœur, comme si tu étais un Dieu:
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Domin ka ɗauka kai mai hikima ne, mai hikima kamar allah,
7 A cause de cela voici, je m'en vais faire venir contre toi des étrangers les plus terribles d'entre les nations, qui tireront leurs épées sur la beauté de ta sagesse, et souilleront ton lustre.
zan kawo baƙi a kanka, waɗanda suka fi mugunta cikin sauran al’ummai; za su zāre takubansu a kan kyakkyawar hikimarka su kuma ɓarke darajarka mai walƙiya.
8 Ils te feront descendre en la fosse, et tu mourras au cœur de la mer, de la mort des blessés à mort.
Za su jefar da kai cikin rami, za ka kuwa yi muguwar mutuwa a tsakiyar tekuna.
9 Iras-tu disant devant celui qui te tuera, je suis Dieu? vu que tu [te trouveras] homme, et non le [Dieu] Fort, dans la main de celui qui te blessera mortellement.
Za ka iya ce yanzu, “Ni allah ne,” a gaban waɗanda suka kashe ka? Za ka zama mutum kurum, ba allah ba, a hannuwan waɗanda suka kashe ka.
10 Tu mourras de la mort des incirconcis par la main des étrangers; car j'ai parlé, dit le Seigneur l'Eternel.
Za ka yi mutuwar marar kaciya a hannuwan baƙi. Na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
11 La parole de l'Eternel me fut encore [adressée], en disant:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
12 Fils d'homme, prononce à haute voix une complainte sur le Roi de Tyr, et lui dis: ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: toi à qui rien ne manque, plein de sagesse, et parfait en beauté;
“Ɗan mutum, ka yi makoki domin sarkin Taya ka kuma ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ka kasance hatimin cikakke, cike da hikima da cikakke a kyau.
13 Tu as été en Héden le jardin de Dieu; ta couverture était de pierres précieuses de toutes sortes, de Sardoine, de Topaze, de Jaspe, de Chrysolithe, d'Onyx, de Béryl, de Saphir, d'Escarboucle, d'Emeraude, et d'or; ce que savaient faire tes tambours et tes flûtes [a été] chez toi; ils ont été tous prêts au jour que tu fus créé.
Ka kasance a Eden, a lambun Allah; aka yi maka ado da kowane dutse mai daraja, yakutu, tofaz, da zumurrudu, kirisolit, onis da yasfa, saffaya, turkuwoyis da beril. Tsare-tsare da shirye-shiryenka an yi su da zinariya ne; a ranar da aka halicce ka an shirya su.
14 Tu [as été] un Chérubin, oint pour servir de protection; je t'avais établi, [et] tu as été dans la sainte montagne de Dieu; tu as marché entre les pierres éclatantes.
An shafe ka kamar kerub mai tsaro, gama haka na naɗa ka. Kana a tsattsarkan dutsen Allah; ka yi tafiya a tsakiyar duwatsun wuta.
15 Tu as été parfait en tes voies dès le jour que tu fus créé, jusqu'à ce que la perversité a été trouvée en toi.
Ka kasance marar laifi cikin dukan hanyoyinka daga ranar da aka halicce ka sai da aka sami mugunta a cikinka.
16 Selon la grandeur de ton trafic on a rempli le milieu de toi de violence, et tu as péché; c'est pourquoi je te jetterai comme une chose souillée hors de la montagne de Dieu, et je te détruirai d'entre les pierres éclatantes, ô Chérubin! qui sers de protection.
Ta wurin yawan kasuwancinka ka cika da rikici, ka kuma yi zunubi. Saboda haka na kore ka da kunya daga dutsen Allah, na kore ka, ya kerub mai tsaro, daga cikin duwatsun wuta.
17 Ton cœur s'est élevé à cause de ta beauté, tu as perdu ta sagesse à cause de ton éclat; je t'ai jeté par terre, je t'ai mis en spectacle aux Rois, afin qu'ils te regardent.
Zuciyarka ta cika da alfarma saboda kyanka, ka kuma lalace hikimarka saboda darajarka. Saboda haka na jefar da kai zuwa ƙasa; na sa ka zama abin kallo a gaban sarakuna.
18 Tu as profané tes Sanctuaires par la multitude de tes iniquités, en usant mal de ton trafic; et j'ai fait sortir du milieu de toi un feu qui t'a consumé, et je t'ai réduit en cendre sur la terre, en la présence de tous ceux qui te voient.
Ta wurin yawan zunubanka da kasuwancinka na cuta ka ƙazantar da wuri mai tsarkinka. Saboda haka na sa wuta ta fito daga cikinka, ta cinye ka, na maishe ka toka a bisa ƙasa a kan idon dukan waɗanda suke kallonka.
19 Tous ceux qui te connaissent entre les peuples ont été désolés à cause de toi; tu es cause qu'on est tout étonné de ce que tu ne seras plus à jamais.
Dukan al’umman da suka san ka sun giggice saboda masifar da ta auko maka; ka zo ga mummunar ƙarshe ba za ka ƙara kasancewa ba har abada.’”
20 Puis la parole de l'Eternel me fut [adressée], en disant:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
21 Fils d'homme, tourne ta face vers Sidon, et prophétise contre elle.
“Ɗan mutum, ka fuskanci Sidon; ka yi annabci a kanta
22 Et dis: ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: voici j'en veux à toi, Sidon, et je serai glorifié au milieu de toi; et on saura que je suis l'Eternel, quand j'aurai exercé des jugements contre elle, et que j'y aurai été sanctifié.
ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ina gāba da ke, ya Sidon, zan sami ɗaukaka a cikinki. Za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na zartar da hukunci a kanta na kuma nuna kaina mai tsarki a cikinta.
23 J'enverrai donc dans elle la mortalité, et le sang dans ses places, et les blessés à mort tomberont au milieu d'elle par l'épée qui viendra de toutes parts sur elle; et ils sauront que je suis l'Eternel.
Zan aika da annoba a kanta in kuma sa jini ya zuba a titunanta. Kisassu za su fāɗi a cikinta, da takobi yana gāba da ita a kowane gefe. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.
24 Et elle ne sera plus une ronce piquante à la maison d'Israël, ni une épine causant plus de douleur qu'aucun de ceux qui sont autour d'eux, et qui les pillent; et ils sauront que je suis le Seigneur l'Eternel.
“‘Mutanen Isra’ila ba za su ƙara kasance da mugayen maƙwabta waɗanda za su zama sarƙaƙƙiya masu zafi da ƙaya mai tsini ba. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
25 Ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: quand j'aurai rassemblé la maison d'Israël d'entre les peuples parmi lesquels ils auront été dispersés, je serai sanctifié en eux, les nations le voyant, et ils habiteront sur leur terre que j'ai donnée à mon serviteur Jacob.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa sa’ad da na tattara mutanen Isra’ila daga al’ummai inda suke a warwatse, zan nuna kaina mai tsarki a cikinsu a idon al’ummai. Sa’an nan za su zauna a ƙasarsu, wadda na ba wa bawana Yaƙub.
26 Ils y habiteront en sûreté, ils bâtiront des maisons, ils planteront des vignes; ils [y] habiteront, dis-je, en sûreté, lorsque j'aurai exercé des jugements contre ceux qui les auront pillés de toutes parts; et ils sauront que je suis l'Eternel leur Dieu.
Za su zauna a can lafiya su kuma gina gidaje su nome gonakin inabi; za su zauna lafiya sa’ad da zan zartar da hukunci a kan dukan maƙwabtansu da suka wulaƙanta su. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu.’”

< Ézéchiel 28 >