< Ézéchiel 31 >

1 Il arriva aussi en la onzième année, au premier jour du troisième mois, que la parole de l'Eternel me fut [adressée], en disant:
A shekara ta goma sha ɗaya, a wata na uku a rana ta farko, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Fils d'homme, dis à Pharaon Roi d'Egypte, et à la multitude de son peuple: A qui ressembles-tu dans ta grandeur?
“Ɗan mutum, faɗa wa Fir’auna sarkin Masar da jama’arsa cewa, “‘Da wa za a kwatanta girmanka?
3 Voici, le Roi d'Assyrie a été tel qu'est un cèdre au Liban, ayant de belles branches, et des rameaux qui faisaient une grande ombre, et qui étaient d'une grande hauteur; sa cime a été fort touffue.
Ka dubi Assuriya, ta taɓa zama kamar al’ul a Lebanon da rassa masu kyau suna inuwartar da kurmi; ya yi tsayi ainun kansa ya kai cikin gizagizai.
4 Les eaux l'ont fait croître, l'abîme l'a fait monter fort haut, ses fleuves ont coulé autour de ses plantes, et il a envoyé les conduits de ses eaux vers tous les arbres des champs.
Ruwa ya sa ya yi girma, zurfafan maɓulɓulai sun sa ya yi tsayi; rafuffuka suna gudu kewaye da tushensa yana aika da rafuffukansa zuwa dukan itatuwan kurmi.
5 C'est pourquoi sa hauteur s'est élevée par dessus tous les [autres] arbres des champs, ses branches ont été multipliées, et ses rameaux sont devenus longs par les grandes eaux, lorsqu'il poussait ses branches.
Saboda haka ya yi tsayi fiye da sauran itatuwan kurmi; rassansa suka ƙaru suka yi tsayi, suka bazu saboda yalwar ruwaye.
6 Tous les oiseaux des cieux ont fait leurs nids dans ses branches, et toutes les bêtes des champs ont fait leurs petits sous ses rameaux, et toutes les grandes nations ont habité sous son ombre.
Dukan tsuntsayen sararin sama suka yi sheƙa a rassansa, dukan namun jeji suka haihu a ƙarƙashin rassansa; dukan al’ummai suka zauna a inuwarsa.
7 Il était donc devenu beau dans sa grandeur, [et] dans l'étendue de ses branches, parce que sa racine était sur de grandes eaux.
Yana da girma a kyau, da dogayen rassansa da ya baza, gama saiwoyinsa sun nutse can ƙasa har cikin yalwar ruwaye.
8 Les cèdres qui étaient au Jardin de Dieu ne lui ôtaient rien de son lustre; les sapins n'étaient point pareils à ses branches, et les châtaigniers n'égalaient point [l'étendue] de ses rameaux; tous les arbres qui étaient au Jardin de Dieu n'ont point été pareils à lui en sa beauté.
Al’ul a cikin lambun Allah ba su kai shi ba, balle itatuwan kasharina su kai rassansa, ko itatuwan durumi su kai rassansa, ko itace a lambun Allah ya kai kyansa.
9 Je l'avais fait beau dans la multitude de ses rameaux, tellement que tous les arbres d'Héden, qui étaient au Jardin de Dieu, lui portaient envie.
Na sa ya yi kyau da yalwar rassa, abin ƙyashi na dukan itatuwan Eden a lambun Allah.
10 C'est pourquoi le Seigneur l'Eternel dit ainsi: parce que tu t'es élevé en hauteur, [comme celui-là], qui avait sa cime toute touffue, a élevé son cœur dans sa hauteur;
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin ya yi tsayi, kansa kuma ya kai cikin gizagizai, kuma domin ya yi fariya saboda tsayinsa,
11 Et je l'ai livré entre les mains du [plus] fort d'entre les nations, qui l'a traité comme il fallait, [et] je l'ai chassé à cause de sa méchanceté.
na miƙa shi ga mai mulkin al’ummai, don yă sāka masa gwargwadon muguntarsa. Na jefar da shi a gefe,
12 Et les étrangers les plus terribles d'entre les nations l'ont coupé, et l'ont laissé là, et ses branches sont tombées sur les montagnes, et sur toutes les vallées; et ses rameaux se sont rompus dans tous les cours [des eaux] de la terre, et tous les peuples de la terre se sont retirés de dessous son ombre, et l'ont laissé là.
kuma baƙi mafi mugunta na al’ummai suka sare shi suka bar shi. Rassansa sun fāɗi a kan duwatsun da suke cikin dukan kwaruruka; rassansa kuma sun kakkarye, sun fāɗi a cikin dukan magudanan ruwa na ƙasa. Dukan al’umman duniya suka fito daga ƙarƙashin inuwarsa suka bar shi.
13 Tous les oiseaux des cieux se sont tenus sur ses ruines, et toutes les bêtes des champs se sont retirées vers ses rameaux.
Dukan tsuntsaye sararin sama suka zauna a itacen da ya fāɗi, dukan namun jeji kuma suna cikin rassansa.
14 C'est pourquoi aucun arbre arrosé d'eaux ne s'élève de sa hauteur, et ne produit de cime touffue, et les plus forts d'entre eux, même de tous ceux qui hument l'eau, ne subsistent point dans leur hauteur; car eux tous sont livrés à la mort dans la terre basse parmi les enfants des hommes, avec ceux qui descendent en la fosse.
Saboda haka ba wani daga cikin itatuwan da suke kusa da ruwan da zai taɓa yin fariyar tsawonsa, har kawunansu su kai cikin gizagizai. Ba wani daga cikin itatuwan da ya sha ruwa sosai da zai taɓa yi wannan tsayi; duk an bashe su ga mutuwa, zuwa can ƙasa, a cikin matattu, tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
15 Ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: le jour qu'il descendit au sépulcre, je fis mener deuil [sur lui], je couvris l'abîme devant lui, et j'empêchai ses fleuves de couler, et les grosses eaux furent retenues; je fis que le Liban fut en deuil à cause de lui, et tous les arbres des champs en furent fatigués. (Sheol h7585)
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar da aka yi ƙasa da shi zuwa kabari na rufe zurfafa maɓulɓulai da makoki dominsa; na janye rafuffukansa, aka kuma hana yalwan ruwansa. Saboda shi na rufe Lebanon da baƙin ciki, dukan itatuwan kurmi suka bushe. (Sheol h7585)
16 J'ébranlai les nations par le bruit de sa ruine, quand je le fis descendre au sépulcre, avec ceux qui descendent dans la fosse; et tous les arbres d'Héden, l'élite et le meilleur du Liban, tous humant l'eau, furent rendus contents au bas de la terre. (Sheol h7585)
Na sa al’ummai suka yi rawar jiki da jin ƙarar fāɗuwarsa sa’ad da na yi ƙasa da shi zuwa kabari tare da waɗanda suka gangara rami. Sai dukan itatuwan Eden, zaɓaɓɓu da kuma mafi kyau na Lebanon, dukan itatuwan da aka yi musu banruwa, sun ta’azantu a ƙarƙashin ƙasa. (Sheol h7585)
17 Eux aussi sont descendus avec lui au sépulcre, vers ceux qui ont été tués par l'épée, et son bras, [c'est-à-dire], ceux qui habitaient sous son ombre parmi les nations, [y sont aussi descendus]. (Sheol h7585)
Waɗanda suka zauna a inuwarsa, dukan masu tarayyarsa a cikin al’ummai, su ma sun gangara zuwa kabari tare da shi, sun haɗu da waɗanda aka kashe da takobi. (Sheol h7585)
18 A qui donc as-tu ressemblé en gloire et en grandeur entre les arbres d'Héden? et pourtant tu seras jeté bas avec les arbres d'Héden dans les lieux profonds de la terre, tu seras gisant au milieu des incirconcis, avec ceux qui ont été tués par l'épée. C'est ici Pharaon, et toute la multitude de son peuple, dit le Seigneur l'Eternel.
“‘Da wa cikin itatuwan Eden za a kwatanta da kai cikin girma da daraja? Duk da haka kai ma, za a yi ƙasa da kai tare da itatuwan Eden zuwa ƙarƙashin ƙasa; za ka kwanta a cikin marasa kaciya, tare da waɗanda aka kashe da takobi. “‘Fir’auna ke nan da dukan jama’arsa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”

< Ézéchiel 31 >