< Ézéchiel 5 >

1 Davantage toi, fils d'homme, prends-toi un couteau tranchant; prends-toi un rasoir de barbier; et fais-le passer sur ta tête, et sur ta barbe; puis tu prendras une balance à peser, et tu partageras ce [que tu auras rasé].
“Yanzu, ɗan mutum, ka ɗauki takobi mai kaifi ka kuma yi amfani da shi kamar rezan mai aski don askin kanka da gemunka. Sa’an nan ka ɗauki ma’auni ka kuma raba gashin.
2 Tu [en] brûleras une troisième partie dans le feu, au milieu de la ville, lorsque les jours du siège s'accompliront, et tu en prendras une autre troisième partie, [et] tu frapperas de l'épée à l'entour; et tu disperseras au vent l'autre troisième partie; car je tirerai l'épée après eux.
Sa’ad da kwanakin ƙawanyarka sun ƙare, sai ka ƙone kashi ɗaya bisa uku na gashin da wuta a cikin birnin. Ka ɗauki kashi ɗaya bisa uku ka yayyanka shi da takobi kewaye da birnin. Ka kuma watsar da kashi ɗaya bisa uku a iska. Gama zan fafare su da takobin da aka zāre.
3 Et tu en prendras de là quelque petit nombre, et les serreras aux pans de ton manteau.
Amma ka ɗibi gashi kaɗan ka daure a shafin rigarka.
4 Et de ceux-là, tu en prendras encore, et les jetteras au milieu du feu, et les brûleras au feu; [et] il en sortira du feu contre toute la maison d'Israël.
Har yanzu, ka ɗibi kaɗan na waɗannan ka zuba su cikin wuta su kuma ƙone. Wuta zai bazu daga nan zuwa dukan gidan Isra’ila.
5 Ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: c'est ici cette Jérusalem que j'avais placée au milieu des nations et des pays qui sont autour d'elle.
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce Urushalima ce wannan, wadda na kafa a tsakiyar al’ummai, da ƙasashe kewaye da ita a ko’ina.
6 Elle a changé mes ordonnances en une méchanceté pire que celle des nations, et mes statuts en une méchanceté pire que celle des pays qui sont autour d'elle; car ils ont rejeté mes ordonnances, et n'ont point marché dans mes statuts.
Duk da haka cikin muguntarta ta yi tayarwa a kan dokokina da ƙa’idodina fiye da al’ummai da ƙasashe kewaye da ita. Ta ƙi dokokina ba tă kuwa bi ƙa’idodina ba.
7 C'est pourquoi le Seigneur l'Eternel a dit ainsi: parce que vous avez multiplié [vos méchancetés] plus que les nations qui [sont] autour de vous, [et] que vous n'avez point marché dans mes statuts, et n'avez point observé mes ordonnances, et que vous n'avez pas même fait selon les ordonnances des nations qui sont autour de vous;
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce kin yi ƙin ji fiye da al’umman da suke kewaye da ke ba ki kuma bi ƙa’idodina ko ki kiyaye dokokina ba. Ba ki ma dace da matsayin al’umman da suke kewaye da ke ba.
8 A cause de cela le Seigneur l'Eternel dit ainsi: voici, j'[en veux] à toi, oui moi-même, et j'exécuterai au milieu de toi mes jugements, devant les yeux des nations.
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce Ni kaina ina gāba da ke, Urushalima, kuma zan hukunta ki a gaban al’ummai.
9 Et je ferai en toi, à cause de toutes tes abominations, des choses que je ne fis jamais, et telles que je n'en ferai jamais de semblables.
Saboda dukan gumakan banƙyamarki, zan yi abin da ban taɓa yi ba, ba kuwa zan ƙara yinsa ba.
10 Les pères mangeront leurs enfants au milieu de toi, et les enfants mangeront leurs pères; et j'exécuterai [mes] jugements sur toi, et je disperserai à tous vents tout ce qui restera de toi.
Saboda haka a cikinki ubanni za su ci’ya’yansu,’ya’ya kuma za su ci ubanninsu. Zan hukunta ki zan kuma watsar da dukan waɗanda suke tsira da suke naki a iska.
11 Et je suis vivant, dit le Seigneur l'Eternel, parce que tu as souillé mon Sanctuaire par toutes tes infamies, et par toutes tes abominations, moi-même je te raserai, et mon œil ne t'épargnera point, et je n'en aurai point de compassion.
Saboda haka muddin ina a raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, domin kin ƙazantar da wuri mai tsarkina da dukan mugayen siffofinki da kuma ayyukanki masu banƙyama, ni kaina zan janye alherina; ba zan ji tausayinki ko in haƙura da ke ba.
12 Une troisième partie d'entre vous mourra de mortalité, et sera consumée par la famine au milieu de toi; et une troisième partie tombera par l'épée autour de toi; et je disperserai à tous vents l'autre troisième partie, et je tirerai l'épée après eux.
Kashi ɗaya bisa uku na mutanenki za su mutu da annoba ko su mutu da yunwa a cikinki; kashi ɗaya bisa uku takobi ne zai kashe su a waje da katangarki; kashi ɗaya bisa uku kuma zan watsar a iska in kuma fafare su da takobin da aka zāre.
13 Car ma colère sera portée à son comble, et je ferai reposer ma fureur sur eux, et je me satisferai; et ils sauront que moi l'Eternel j'ai parlé dans ma jalousie, quand j'aurai consommé ma fureur sur eux.
“Sa’an nan ne fushina zai huce hasalata a kanki kuma ta lafa, in kuma wartsake. Kuma sa’ad da na zuba fushina a kansu, a sa’an nan ne za su san cewa Ni Ubangiji na yi magana a cikin fushin kishina a kansu.
14 Je te mettrai en désert et en opprobre parmi les nations qui sont autour de toi, tellement que tous les passants le verront.
“Zan mai da ki kufai da kuma abin dariya a cikin al’ummai kewaye da ke, a gaban dukan waɗanda suke wucewa.
15 Et tu seras en opprobre, en ignominie, en instruction, et en étonnement aux nations qui sont autour de toi, quand j'aurai exécuté mes jugements sur toi, avec colère, avec fureur, et par des châtiments pleins de fureur; moi l'Eternel j'ai parlé.
Za ki zama abin dariya da abin ba’a, kashedi da abin banrazana ga al’ummai kewaye da ke sa’ad da na hukunta ki cikin fushi da cikin hasala da kuma tsawatawa mai zafi. Ni Ubangiji na faɗa.
16 Après que j'aurai décoché sur eux les mauvaises flèches de la famine, qui seront mortelles, lesquelles je décocherai pour vous détruire, encore j'augmenterai la famine sur vous, et je vous romprai le bâton du pain.
Sa’ad da na harbe ki da mugayen kibiyoyina da kuma kibiyoyi masu hallakarwa na yunwa, zan yi harbi don in kashe ki. Zan kawo ƙarin yunwa a kanki in kuma yanke tanadin abincinki.
17 Je vous enverrai la famine, et des bêtes nuisibles, qui te priveront d'enfants; et la mortalité et le sang passeront parmi toi, et je ferai venir l'épée sur toi; moi l'Eternel j'ai parlé.
Zan aika da yunwa da namun jeji a kanki, za su kuma bar ku ba’ya’ya. Annoba da zub da jini za su ratsa cikinki, zan kuma kawo takobi a kanki. Ni Ubangiji na faɗa.”

< Ézéchiel 5 >