< Isaïe 30 >

1 Malheur aux enfants revêches, dit l'Eternel, qui prennent conseil, et non pas de moi; et qui se forgent des idoles, où mon esprit n'est point, afin d'ajouter péché sur péché.
“Kaiton’ya’ya masu tayarwa,” in ji Ubangiji, “ga waɗanda suke ƙulle-ƙullen da ba nawa ba, suna yin yarjejjeniya, amma ba ta Ruhuna ba, suna jibga zunubi a kan zunubi;
2 Qui sans avoir interrogé ma bouche marchent pour descendre en Egypte, afin de se fortifier de la force de Pharaon, et se retirer sous l'ombre d'Egypte.
waɗanda suka gangara zuwa Masar ba tare da sun nemi shawarata; waɗanda suke neman taimakon kāriyar Fir’auna, don neman inuwar mafakar Masar.
3 Car la force de Pharaon vous tournera à honte, et la retraite sous l'ombre d'Egypte [vous tournera] à confusion.
Amma kāriyar Fir’auna za tă zama muku abin kunya, inuwar Masar za tă jawo muku kunya.
4 Car les principaux de son peuple ont été à Tsohan, et ses messagers sont parvenus jusques à Hanès.
Ko da yake suna da shugabanni a Zowan kuma jakadunsu sun iso Hanes,
5 Tous seront rendus honteux par un peuple qui ne leur profitera de rien, ils n'en recevront aucun secours ni aucun avantage, mais il sera leur honte, et leur opprobre.
kowa zai sha kunya saboda mutanen da ba su da amfani gare su, waɗanda ba sa taimako ko amfani, sai dai jawo kunya da da-na-sani.”
6 Les bêtes seront chargées pour aller au Midi; ils porteront leurs richesses sur les dos des ânons, et leurs trésors sur la bosse des chameaux, vers le peuple qui ne leur profitera point, au pays de détresse et d'angoisse, d'où viennent le vieux lion, et le lion, la vipère, et le serpent brûlant qui vole.
Allah ya faɗa game da dabbobin Negeb cewa, Ta cikin ƙasa mai wahala da mai hatsari inda zakoki da zakanya, inda macizai masu dafi da macizai masu tashi sama suke, jakadu na ɗaukan arzikinsu a kan jakuna, dukiyarsu a kan raƙuma, zuwa ƙasan nan marar riba,
7 Car le secours que les Egyptiens leur donneront ne sera que vanité, et qu'un néant; c'est pourquoi j'ai crié ceci; leur force est de se tenir tranquilles.
zuwa Masar, wadda taimakonta marar amfani ne. Saboda haka na yi mata laƙabi Rahab Marar Yin Kome.
8 Entre [donc] maintenant, et l'écris en leur présence sur une table, et rédige-le par écrit dans un livre, afin que cela demeure pour le temps à venir, à perpétuité, à jamais;
Tafi yanzu, ka rubuta musu a kan allo, ka rubuta shi a kan littafi, cewa kwanaki suna zuwa zai zama madawwamin shaida.
9 Que c'est ici un peuple rebelle, des enfants menteurs, des enfants qui ne veulent point écouter la Loi de l'Eternel;
Waɗannan mutane masu tawaye,’ya’ya masu ruɗu,’ya’yan da ba sa niyya su saurara ga umarnan Ubangiji.
10 Qui ont dit aux Voyants; ne voyez point; et à ceux qui voient [des visions]; ne voyez point de visions de justice, mais dites-nous des choses agréables, voyez [des visions] trompeuses.
Sukan ce wa masu gani, “Kada ku ƙara ganin wahayi!” Ga annabawa kuwa sukan ce, “Kada ku ƙara ba mu wahayin abin da yake daidai! Faɗa mana abubuwan da muke so mu ji ne kawai, ku yi annabcin abin da zai ruɗe mu.
11 Retirez-vous du chemin, détournez-vous du sentier, faites cesser le Saint d'Israël de devant nous.
Ku bar wannan hanya, ku tashi daga wannan hanya, ku kuma daina kalubalantarmu da Mai Tsarkin nan na Isra’ila!”
12 C'est pourquoi ainsi a dit le Saint d'Israël; parce que vous avez rejeté cette parole, et que vous vous êtes confiés en l'oppression, et en vos moyens obliques, et que vous vous êtes appuyés sur ces choses;
Saboda haka, ga abin da Mai Tsarkin nan na Isra’ila yake cewa, “Saboda haka kun ƙi wannan saƙo, kuka dogara ga aikin kama-karya kuka kuma dogara ga yin ruɗu,
13 A cause de cela cette iniquité vous sera comme la fente d'une muraille qui s'en va tomber, faisant ventre jusques au haut, de laquelle la ruine vient soudainement, et en un moment.
wannan zunubi zai zama muku kamar bango mai tsayi, tsagagge da yake kuma fāɗuwa, da zai rushe nan da nan, ba tsammani.
14 Il la brisera donc comme on brise une bouteille d'un potier de terre qui est cassée, laquelle on n'épargne point, et des pièces de laquelle ne se trouverait pas un têt pour prendre du feu du foyer, ou pour puiser de l'eau d'une fosse.
Zai rushe kucu-kucu kamar tukunyar yumɓu, ya ragargaje ƙaf har cikin gutsattsarinsa ba za a sami ko ɗan katanga don ɗiba garwashin wuta ko a ɗiba ruwa daga tanki ba.”
15 Car ainsi avait dit le Seigneur, l'Eternel, le Saint d'Israël; en vous tenant tranquilles et en repos vous serez délivrés, votre force sera en vous tenant en repos et en espérance; mais vous ne l'avez point agréé.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya faɗa, “Cikin tuba da hutu ne kaɗai cetonku yake, cikin shiru da dogara gare ni ne za ku sami ƙarfinku, amma ba za ku sami ko ɗaya a cikinsu ba.
16 Et vous avez dit; non, mais nous nous enfuirons sur des chevaux; à cause de cela vous vous enfuirez. Et [vous avez dit]; nous monterons sur [des chevaux] légers; à cause de cela ceux qui vous poursuivront seront légers.
Kun ce, ‘A’a, za mu gudu a kan dawakai.’ Saboda haka za ku gudu! Kun ce, ‘Za mu hau dawakai masu sauri mu gudu.’ Saboda haka masu fafararku za su fi ku gudu!
17 Mille d'entre vous s'enfuiront à la menace d'un seul; vous vous enfuirez à la menace de cinq; jusqu'à ce que vous soyez abandonnés comme un arbre tout ébranché au sommet d'une montagne, et comme un étendard sur un coteau.
Dubu za su gudu don barazanar mutum guda; da jin barazanar mutane biyar dukanku za ku yi ta gudu sai an bar ku kamar sandar tuta a kan dutse, kamar tuta a kan tudu.”
18 Et cependant l'Eternel attend pour vous faire grâce, et ainsi il sera exalté en ayant pitié de vous; car l'Eternel est le Dieu de jugement; ô que bienheureux sont tous ceux qui se confient en lui!
Duk da haka Ubangiji yana marmari ya yi muku alheri; ya tashi don yă nuna muku jinƙai. Gama Ubangiji Allah ne mai aikata gaskiya. Masu albarka ne dukanku waɗanda suke dogara gare shi!
19 Car le peuple demeurera dans Sion, et dans Jérusalem; tu ne pleureras point; certes il te fera grâce sitôt qu'il aura ouï ton cri; sitôt qu'il t'aura ouï, il t'exaucera.
Ya mutanen Sihiyona, waɗanda suke zama a Urushalima, ba za ku ƙara kuka ba. Zai zama mai alheri sa’ad da kuka yi kukan neman taimako! Da zarar ya ji, zai amsa muku.
20 Le Seigneur vous donnera du pain de détresse, et de l'eau d'angoisse, mais tes Docteurs ne s'envoleront plus, et tes yeux verront tes Docteurs.
Ko da yake Ubangiji yakan ba da abincin azaba da ruwan wahala, ba za a ƙara ɓoye malamanku ba; da idanunku za ku gan su.
21 Et tes oreilles entendront la parole de celui qui sera derrière toi, disant; c'est ici le chemin, marchez-y; soit que vous tiriez à droite, soit que vous tiriez à gauche.
Ko kun juye dama ko hagu, kunnuwanku za su ji murya a bayanku tana cewa, “Ga hanya; ku yi tafiya a kai.”
22 Et vous tiendrez pour souillés les chapiteaux des images taillées, faites de l'argent d'un chacun de vous, et les ornements faits de l'or fondu d'un chacun de vous; tu les jetteras au loin, comme un sang impur; et tu diras; videz-le dehors.
Sa’an nan za ku ƙazantar da gumakanku da kuka dalaye da zinariya; za ku zubar da su kamar rigar al’adar mace ku kuma ce musu, “Ku ɓace mana da gani!”
23 Et il donnera la pluie sur tes semailles, quand tu auras semé en la terre; et le grain du revenu de la terre sera abondant, et bien nourri; en ce jour-là ton bétail paîtra dans une campagne spacieuse.
Zai kuma aiko muku da ruwan sama don shuki a ƙasa, kuma abincin da zai fito daga gona zai zama mai albarka da kuma mai yawa. A wannan rana shanu za su yi kiwo a wadatacciyar makiyaya.
24 Et les bœufs et les ânes qui labourent la terre mangeront le pur fourrage de ce qui aura été vanné avec la pelle et le van.
Shanunku da jakunanku da suke huɗar gonakinku za su ci harawa mafi kyau, wanda an sheƙe shi da babban cokali mai yatsu da kuma babban cokali.
25 Et il y aura des ruisseaux d'eaux courantes sur toute haute montagne, et sur tout coteau haut élevé, au jour de la grande tuerie, quand les tours tomberont.
A ranar babban kisa, sa’ad da hasumiyoyi za su fāɗi, rafuffukan ruwa za su malalo a kan kowane dutse da kowane tudu mai tsawo.
26 Et la lumière de la lune sera comme la lumière du soleil; et la lumière du soleil sera sept fois aussi grande, comme [si c'était] la lumière de sept jours, au jour que l'Eternel aura bandé la froissure de son peuple, et qu'il aura guéri la blessure de sa plaie.
Wata zai yi haske kamar rana, kuma hasken rana zai ma yi sau bakwai na haskenta, kamar hasken cikakku ranaku bakwai, sa’ad da Ubangiji zai ɗaura raunukan mutanensa ya kuma warkar da raunukan da ya yi musu.
27 Voici, le Nom de l'Eternel vient de loin, sa colère est ardente, et une pesante charge; ses lèvres sont remplies d'indignation, et sa langue est comme un feu dévorant.
Duba, Sunan Ubangiji yana zuwa daga nesa, tare da fushi mai ƙuna da kuma baƙin hayaƙi; leɓunansa sun cika da fushi, harshensa kuma wuta ce mai cinyewa.
28 Et son Esprit est comme un torrent débordé, qui atteint jusques au milieu du cou, pour disperser les nations, d'une telle dispersion, qu'elles seront réduites à néant; et il est [comme] une bride aux mâchoires des peuples, qui les fera aller à travers champs.
Numfashinsa kamar raƙuman ruwa masu gudu yana tashi har zuwa wuya. Yakan tankaɗe al’ummai cikin lariyar hallaka; yakan sa a muƙamuƙan mutane linzamin da zai jagorance su su kauce.
29 Vous aurez un cantique tel que celui de la nuit en laquelle on se prépare à célébrer une fête solennelle; et vous aurez une allégresse de cœur telle qu'a celui qui marche avec la flûte, pour venir en la montagne de l'Eternel, vers le rocher d'Israël.
Za ku kuma rera kamar a daren da kuke shagalin biki mai tsarki; zukatanku za su yi farin ciki kamar sa’ad da mutane sukan haura da busa zuwa dutsen Ubangiji, zuwa Dutse na Isra’ila.
30 Et l'Eternel fera entendre sa voix, pleine de majesté, et il fera voir où aura assené son bras dans l'indignation de sa colère, avec une flamme de feu dévorant, avec éclat, tempête, et pierres de grêle.
Ubangiji zai sa mutane su ji muryarsa mai daraja ya kuma sa su ga hannunsa na saukowa tare da fushi mai ƙuna da kuma wuta mai cinyewa, gizagizai za su ɓarke, za a yi hadarin tsawa da ƙanƙara.
31 Car l'Assyrien, qui frappait du bâton, sera effrayé par la voix de l'Eternel.
Muryar Ubangiji za tă firgita Assuriya da sandar mulkinsa zai kashe su.
32 Et partout ou passera le bâton enfoncé dont l'Eternel l'aura assené, et par lequel il aura combattu dans les batailles à bras élevé, [on y entendra des] tambours et des harpes.
Kowane bugun da Ubangiji zai yi musu da bulalarsa na hukunci zai zama kiɗi ga ganguna da garaya, yayinda yake yaƙi da su da naushin hannunsa.
33 Car Topheth est déjà préparée, et même elle est apprêtée pour le Roi; il l'a faite profonde et large; son bûcher c'est du feu, et force bois; le souffle de l'Eternel l'allumant comme un torrent de soufre.
An riga an shirya wurin ƙonawa; an shirya shi saboda sarki. An haƙa ramin wutarsa da zurfi da kuma fāɗi, da isashen wuta da itacen wuta; numfashin Ubangiji, yana kamar kibiritu mai ƙuna, da aka sa masa wuta.

< Isaïe 30 >