< Isaïe 8 >

1 Et l'Eternel me dit; Prends-toi un grand rouleau, et y écris avec une touche, en grosses lettres; QU'ON SE DEPECHE DE BUTINER; IL HATE LE PILLAGE.
Ubangiji ya ce mini, “Ka ɗauki naɗaɗɗen littafi mai girma ka yi rubutu a kai da alƙalami kurum, Maher-Shalal-Hash-Baz.
2 De quoi je pris avec moi des fidèles témoins, [savoir] Urie le Sacrificateur, et Zacharie fils de Jébéréchia.
Zan kuma kira Uriya firist da Zakariya ɗan Yeberekiya su zama mini amintattun shaidu.”
3 Puis je m'approchai de la Prophétesse, laquelle conçut, et enfanta un fils; et l'Eternel me dit; appelle son nom Mahersalal-has-baz.
Sa’an nan na tafi na yi jima’i da annabiya, ta kuwa yi ciki ta haifi ɗa. Ubangiji kuma ya ce mini, “Raɗa masa suna, Maher-Shalal-Hash-Baz.
4 Car avant que l'enfant sache crier, mon père! et ma mère! on enlèvera la puissance de Damas, et le butin de Samarie, devant le Roi d'Assur.
Kafin yaron yă san yadda zai ce ‘Babana’ ko ‘Mamana,’ sarkin Assuriya zai kwashe arzikin Damaskus da ganimar Samariya.”
5 Et l'Eternel continua encore de me parler, en disant;
Ubangiji ya sāke yi mini magana ya ce,
6 Parce que ce peuple a rejeté les eaux de Siloé qui vont doucement, et qu'il s'est réjoui de Retsin, et du fils de Rémalja;
“Domin wannan jama’a ta ƙi natsattsen ruwan rafin Shilowa suka yi ta farin ciki a kan Rezin ɗan Remaliya,
7 Pour cette cause, voici, le Seigneur s'en va faire venir sur eux les eaux du fleuve, fortes, et grosses, [savoir] le Roi d'Assur, et toute sa gloire, et ce [fleuve] montera par-dessus tous ses courants d'eau, et ira par-dessus tous ses bords.
saboda haka Ubangiji yana shirin yă kawo musu rigyawar ruwan Kogi, wato, sarkin Assuriya da dukan sojojinsa. Zai cika dukan gaɓoɓinsa, yă kuma malala har zuwa bakin kogi.
8 Et il traversera en Juda, et se débordera, et passera tellement qu'il atteindra jusqu'au cou; et les étendues de ses ailes rempliront la largeur de ton pays, ô Emmanuel!
Yă yi ta malala har zuwa cikin Yahuda, yă shafe ta, yana ratsa ta ciki har yă kai kafaɗa. Fikafikansa da ya buɗe za su rufe fāɗin ƙasarka, Ya Immanuwel!”
9 Peuples, alliez-vous, et soyez froissés; et prêtez l'oreille, vous tous qui êtes d'un pays éloigné; équipez-vous, et soyez froissés; équipez-vous, et soyez froissés.
Ku yi kururuwar yaƙi, ku ƙasashe, ku kuma ji tsoro! Ku saurara, dukanku manisantan ƙasashe. Ku shirya don yaƙi, ku kuma ji tsoro!
10 Prenez conseil, et il sera dissipé; dites la parole, et elle n'aura point d'effet, parce que le [Dieu] Fort est avec nous.
Ku ƙirƙiro dabarunku, amma ba za su yi nasara ba; ku ƙulla shirye-shiryenku, amma ba za su yi amfani ba, gama Allah yana tare da mu.
11 Car ainsi m'a dit l'Eternel avec une main forte, et il m'a instruit de n'aller point par le chemin de ce peuple-ci, en [me] disant;
Ubangiji ya yi mini magana da hannunsa mai ƙarfi a kaina, yana yi mini gargaɗi kada in bi hanyar waɗannan mutane. Ya ce,
12 Ne dites point, Conjuration, toutes les fois que ce peuple dit, Conjuration; et ne craignez point ce qu'il craint, et ne vous en épouvantez point.
“Kada ka kira wani abu makirci game da kome da waɗannan mutane suke kira makirci; kada ji tsoron abin da suke tsoro, kada kuma ka firgita game da shi.
13 Sanctifiez l'Eternel des armées, lui-même; et qu'il soit votre crainte, et votre épouvantement.
Ubangiji Maɗaukaki shi ne za ka ɗauka a matsayi mai tsarki, shi ne wanda za ka ji tsoro, shi ne za ka yi rawar jiki a gabansa,
14 Et il [vous] sera pour sanctuaire; mais il sera une pierre d'achoppement, et un rocher de trébuchement aux deux maisons d'Israël; en piége et en filets aux habitants de Jérusalem.
zai kuwa kasance a wuri mai tsarki; amma ga dukan gidajen Isra’ila zai zama dutsen da zai sa mutane su yi tuntuɓe dutse kuma da zai sa su fāɗi. Ga dukan mutanen Urushalima kuma zai zama tarko da raga.
15 Et plusieurs d'entr'eux trébucheront, et tomberont, et seront froissés, et seront enlacés, et seront pris.
Yawancinsu za su yi tuntuɓe; za su fāɗi a kuwa ragargaza su, za a sa musu tarko a kuma kama su.”
16 Empaquette le Témoignage, cachette la Loi parmi mes disciples.
Ɗaura shaidar nan ta gargadi ka kuma yimƙe umarnin Allah a cikin almajiraina.
17 J'attendrai donc l'Eternel, qui cache sa face de la maison de Jacob, et je m'attendrai à lui.
Zan saurari Ubangiji, wanda ya ɓoye fuskarsa daga gidan Yaƙub. Zan dogara gare shi.
18 Me voici, avec les enfants que l'Eternel m'a donnés pour être un signe et un miracle en Israël, de par l'Eternel des armées, qui habite en la montagne de Sion.
Ga ni, da yaran da Ubangiji ya ba ni. Mu alamu ne da shaidu a cikin Isra’ila daga Ubangiji Maɗaukaki, wanda yake zama a Dutsen Sihiyona.
19 Que s'ils vous disent; enquérez vous des esprits de Python, et des diseurs de bonne aventure, qui gazouillent et grommellent; [répondez]; le peuple ne s'enquerra-t-il point de son Dieu? [aller] pour les vivants aux morts!
Sa’ad da mutane suka ce muku ku nemi shawarar’yan bori da masu sihiri, waɗanda suke shaƙe murya har ba a jin abin da suke faɗi, bai kamata mutane su nemi shawara daga Allahnsu ba? Me zai sa ku nemi shawara daga matattu a madadin masu rai?
20 A la Loi, et au Témoignage. Que s'ils ne parlent selon cette parole-ci, certainement il n'y aura point de lumière pour lui.
Nemi umarnin Allah da kuma shaidar jan kunne. Duk wanda bai yi magana bisa ga wannan kalma ba, ba su da amfani.
21 Et il sera errant sur la terre, étant endurci et affamé; et il arrivera que dans sa faim il se dépitera, et maudira son Roi et son Dieu; et il regardera en haut;
Cikin matsuwa da yunwa, za su yi ta kai komo ko’ina a ƙasar; sa’ad da suka ji yunwa, za su yi fushi su tā da idanu sama, su zagi sarkinsu da Allahnsu.
22 Puis il regardera vers la terre, et voilà la détresse, et les ténèbres, une effrayante angoisse, et il sera enfoncé dans l'obscurité.
Sa’an nan za su zura wa ƙasa idanu, abin da za su gani kawai shi ne matsuwa da duhu da kuma abin banrazana, za a kuma jefa su cikin baƙin duhu.

< Isaïe 8 >