< Jérémie 14 >

1 La parole de l'Eternel, qui fut [adressée] à Jérémie, sur ce que [les pluies avaient été] retenues.
Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya game da fări cewa,
2 La Judée a mené deuil, et ses portes sont en un pitoyable état. Ils sont tous en deuil [gisant] par terre, et le cri de Jérusalem est monté [au ciel].
“Yahuda tana makoki biranenta suna fama; suna kuka saboda ƙasar, kuka kuma tana tasowa daga Urushalima.
3 Et les personnes distinguées ont envoyé à l'eau les moindres d'entre eux; ils sont venus aux lieux creux, ils n'y ont point trouvé d'eau, et ils s'en sont retournés leurs vaisseaux vides; ils ont été rendus honteux et confus, et ils ont couvert leur tête.
Manyan mutane suna aika bayinsu su ɗebo ruwa a maɓulɓulai amma babu ruwa. Suka dawo da tulunansu haka nan; da kunya da kuma ƙasƙanci, da kawunansu a rufe.
4 Parce que la terre s'est crevassée à cause qu'il n'y a point eu de pluie au pays; les laboureurs ont été rendus honteux, [et] ils ont couvert leur tête.
Ƙasa ta tsattsage saboda babu ruwan sama a ƙasar; manoma sun sha kunya suka kuma rufe kawunansu.
5 Même la biche a fait son faon au champ et l'a abandonné, parce qu'il n'y a point d'herbe.
Har barewa a kurmi ma ta gudu ta bar’ya’yan da ta haihu sababbi saboda babu ciyawa.
6 Et les ânes sauvages se sont tenus sur les lieux élevés, ils ont attiré l'air comme des dragons; leurs yeux sont consumés, parce qu'il n'y a point d'herbe.
Jakan jeji suna tsaye a kan tuddai suna haki kamar diloli; idanunsu sun kāsa gani saboda rashin makiyaya.”
7 Eternel, si nos iniquités rendent témoignage contre nous, agis à cause de ton Nom, car nos rébellions sont multipliées; c'est contre toi que nous avons péché.
Ko da yake zunubanmu suna ba da shaida a kanmu, Ya Ubangiji, ka yi wani abu saboda sunanka. Gama jan bayanmu ya yi yawa; mun yi maka zunubi.
8 Toi qui es l'attente d'Israël, [et] son libérateur au temps de la détresse, pourquoi serais-tu en la terre comme un étranger, et comme un voyageur qui se détourne pour passer la nuit?
Ya kai, Sa Zuciyar Isra’ila, Mai Cetonsa a lokutan wahala, me ya sa kake yi kamar baƙo a ƙasar, kamar matafiyi wanda yake shirya wuri don yă kwana gari ya waye ya wuce?
9 Pourquoi serais-tu comme un homme étonné, et comme un homme fort qui ne peut délivrer? Or tu es au milieu de nous, ô Eternel! et ton Nom est réclamé sur nous; ne nous abandonne point.
Me ya sa kake yi kamar mutumin da aka far masa kwasam ba zato, kamar jarumi marar ƙarfin ceto? Kana a cikinmu, ya Ubangiji, da sunanka ake kiranmu; kada ka yashe mu!
10 L'Eternel a dit ainsi à ce peuple, parce qu'ils ont aimé à aller ainsi çà et là, et qu'ils n'ont point retenu leurs pieds, l'Eternel n'a point pris plaisir en eux, il se souviendra maintenant de leurs iniquités, et il punira leurs péchés.
Ga abin da Ubangiji ya ce game da wannan mutane, “Suna son yawace-yawace ƙwarai; ba sa hana ƙafafunsu yawo. Saboda haka Ubangiji bai yarda da su ba; yanzu zai tuna da muguntarsu zai kuma hukunta su saboda zunubansu.”
11 Puis l'Eternel me dit: ne fais point de requête en faveur de ce peuple.
Sa’an nan Ubangiji ya ce mini, “Kada ka yi addu’a domin zaman lafiyar mutanen nan.
12 Quand ils jeûneront, je n'exaucerai point leur cri, et quand ils offriront des holocaustes et des oblations, je n'y prendrai point de plaisir; mais je les consumerai par l'épée, et par la famine, et par la mortalité.
Ko da yake suna azumi, ba zan saurari kukansu ba, ko da yake suna miƙa hadayun ƙonawa da hadayun gari, ba zan yarda da su ba. A maimako zan hallaka su da takobi, yunwa da annoba.”
13 Et je dis: ah! ah! Seigneur Eternel! voici, les Prophètes leur disent: vous ne verrez point l'épée, et vous n'aurez point de famine, mais je vous donnerai une paix assurée en ce lieu-ci.
Amma na ce, “A, Ubangiji Mai Iko Duka, annabawa sun riƙa ce musu, ‘Ba za ku ga takobi ko ku yi fama da yunwa ba. A maimako, zan ba ku madawwamiyar salama.’”
14 Et l'Eternel me dit: ce n'est que mensonge ce que ces prophètes prophétisent en mon Nom; je ne les ai point envoyés, je ne leur ai point donné de charge, et je ne leur ai point parlé; ils vous prophétisent des visions de mensonge, des divinations de néant, et des tromperies de leur cœur.
Sai Ubangiji ya ce mini, “Annabawa suna ta annabcin ƙarya da sunana. Ban aike su ba, ban kuma naɗa su ba, ban yi musu magana ba. Suna muku annabci wahayin ƙarya, suna muku duba marar amfani, suna bautar gumaka suna kuma bayyana tunanin kansu ne.
15 C'est pourquoi, ainsi a dit l'Eternel touchant les prophètes qui prophétisent en mon Nom, et que je n'ai point envoyés, et qui disent: l'épée ni la famine ne sera point en ce pays; ces prophètes-là seront consumés par l'épée et par la famine.
Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce game da annabawan da suke annabci da sunana. Ban aike su ba, duk da haka suna cewa, ‘Babu takobi ko yunwar da zai taɓa wannan ƙasa.’ Waɗannan annabawa takobi da yunwa za su hallaka su.
16 Et le peuple auquel ils ont prophétisé sera jeté par les rues de Jérusalem à cause de la famine et de l'épée; et il n'y aura personne qui les ensevelisse, tant eux que leurs femmes, leurs fils et leurs filles, et je répandrai sur eux leur méchanceté.
Mutanen da suke musu annabcin kuwa za a kore su zuwa titunan Urushalima saboda yunwa da kuma takobi. Babu wanda zai binne su, ko ya binne matansu, ko’ya’yansu maza da mata. Zan aukar musu da masifar da ya dace da su.
17 Tu leur diras donc cette parole-ci: que mes yeux se fondent en larmes nuit et jour, et qu'ils ne cessent point; car la vierge, fille de mon peuple, a été fort maltraitée, la plaie [en] est fort douloureuse.
“Ka yi musu wannan magana, “‘Bari idanuna su yi ta zub da hawaye dare da rana kada su daina; saboda’yata budurwa, mutanena, sun sha wahalar babban rauni, an yi musu bugu mai ragargazawa.
18 Si je sors aux champs, voici les gens morts par l'épée; et si j'entre en la ville, voici les langueurs de la faim; même le Prophète et le Sacrificateur ont couru par le pays, et ils ne savent où ils en sont.
In na shiga cikin ƙasar, na ga waɗanda takobi ya kashe; in na shiga cikin birni, na ga waɗanda suke fama da yunwa. Da Annabi da firist duk sun tafi ƙasar da ba su sani ba.’”
19 Aurais-tu entièrement rejeté Juda? et ton âme aurait-elle Sion en dédain? Pourquoi nous as-tu frappés tellement qu'il n'y a point de guérison? on attend la paix, et il n'y a rien de bon; et le temps de la guérison, et voici le trouble.
Ka ƙi Yahuda ɗungum ke nan? Kana ƙyamar Sihiyona ne? Me ya sa ka buge mu don kada mu warke? Mun sa zuciya ga salama babu abin alherin da ya zo, mun sa rai ga lokacin warkarwa amma sai ga razana.
20 Eternel, nous reconnaissons notre méchanceté, [et] l'iniquité de nos pères; car nous avons péché contre toi.
Ya Ubangiji, mun gane da muguntarmu da kuma laifin kakanninmu; tabbatacce mun yi maka zunubi.
21 Ne nous rejette point à cause de ton Nom, et n'expose point à opprobre le trône de ta gloire; souviens-toi de ton alliance avec nous, [et] ne la romps point.
Saboda sunanka kada ka ƙi mu; kada ka ƙasƙantar da kursiyoyinka mai ɗaukaka. Ka tuna da alkawarinka da mu kada ka tā da shi.
22 Parmi les vanités des nations y en a-t-il qui fassent pleuvoir, et les cieux donnent-ils la menue pluie? N'est-ce pas toi qui le fais, ô Eternel notre Dieu? C'est pourquoi nous nous attendrons à toi; car c'est toi qui as fait toutes ces choses.
Akwai wani daga cikin gumaka marasa amfani na al’ummai da ya kawo ruwan sama? Sararin sama kansu sukan yi yayyafi? A’a, kai ne, ya Ubangiji Allahnmu. Saboda haka sa zuciyarmu tana a kanka, gama kai ne kake yi wannan duka.

< Jérémie 14 >