< Jérémie 37 >

1 Or le Roi Sédécias, fils de Josias, régna en la place de Chonja fils de Jéhojakim, et il fut établi pour Roi sur le pays de Juda par Nébucadnetsar Roi de Babylone.
Nebukadnezzar sarkin Babilon ya naɗa Zedekiya ɗan Yosiya sarkin Yahuda; ya yi mulki a madadin Yehohiyacin ɗan Yehohiyakim.
2 Mais il n'obéit point, ni lui, ni ses serviteurs, ni le peuple du pays, aux paroles de l'Eternel, qu'il avait prononcées par le moyen de Jérémie le Prophète.
Shi da masu yin masa hidima da mutanen ƙasar ba su kula da maganar da Ubangiji ya yi ta wurin Irmiya annabi ba.
3 Toutefois le Roi Sédécias envoya Jéhucal fils de Sélemja, et Sophonie fils de Mahaséja Sacrificateur, vers Jérémie le Prophète, pour lui dire: fais, je te prie, requête pour nous à l'Eternel notre Dieu;
Sai sarki Zedekiya ya aiki Yehukal ɗan Shelemiya tare da firist nan Zefaniya ɗan Ma’asehiya da wannan saƙo cewa, “Ina roƙonka ka yi addu’a ga Ubangiji Allahnmu saboda mu.”
4 (Car Jérémie allait et venait parmi le peuple, parce qu'on ne l'avait pas encore mis en prison.)
To, fa, Irmiya ya sami’yancin kai da kawowa a cikin mutane, gama ba a riga an sa shi a kurkuku ba.
5 Alors l'armée de Pharaon sortit d'Egypte, et quand les Caldéens, qui assiégeaient Jérusalem, en ouïrent les nouvelles, ils se retirèrent de devant Jérusalem.
Sojojin Fir’auna suka fita daga Masar, sa’ad da Babiloniyawa waɗanda suke ƙawanya wa Urushalima suka ji labari game da su, sai suka janye daga Urushalima.
6 Et la parole de l'Eternel fut [adressée] à Jérémie le Prophète, en disant:
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya annabi cewa,
7 Ainsi a dit l'Eternel, le Dieu d'Israël: vous direz ainsi au Roi de Juda, qui vous a envoyés pour m'interroger: voici, l'armée de Pharaon, qui est sortie à votre secours, s'en va retourner en son pays d'Egypte.
“Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa ka faɗa wa sarkin Yahuda, wanda ya aika a neme ni cewa, ‘Sojojin Fir’aunan da suka fito su taimake ka, za su koma ƙasarsu, Masar.
8 Et les Caldéens reviendront, et combattront contre cette ville, et la prendront, et la brûleront au feu.
Sa’an nan Babiloniyawa za su koma su yaƙi wannan birni su ci ta su kuma ƙone shi.’
9 Ainsi a dit l'Eternel: ne vous abusez point vous-mêmes, en disant: les Caldéens se retireront certainement de nous; car ils ne s'en retireront point.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, kada ku ruɗe kanku, kuna tsammani, ‘Tabbatacce Babiloniyawa sun bar mu.’ Ba za su bari ba!
10 Même quand vous auriez battu toute l'armée des Caldéens qui combattent contre vous, et qu'il n'y aurait de reste entre eux que des gens percés de blessures, ils se relèveront pourtant chacun dans sa tente, et brûleront cette ville au feu.
Ko da a ce za ku ci dukan sojojin Babiloniyawan da suke yaƙi da ku har raunana ne kawai aka bari a tentunansu, za su fito su ƙone wannan birni.”
11 Or il arriva que quand l'armée des Caldéens se fut retirée de devant Jérusalem, à cause de l'armée de Pharaon;
Bayan sojojin Babiloniyawa suka janye daga Urushalima saboda sojojin Fir’auna,
12 Jérémie sortit de Jérusalem pour s'en aller au pays de Benjamin, se glissant hors de là à travers le peuple.
sai Irmiya ya bar birnin don yă je yankin Benyamin ya sami rabon mallaka a cikin mutane a can.
13 Mais quand il fut à la porte de Benjamin, il y avait là un capitaine de la garde, duquel le nom était Jireija, fils de Sélemja, fils de Hanania, qui saisit Jérémie le Prophète, en [lui] disant: Tu te vas rendre aux Caldéens.
Amma sa’ad da ya kai Ƙofar Benyamin, sai hafsa mai tsaro, wanda ake kira Iriya ɗan Shelemiya, ɗan Hananiya, ya kama shi ya kuma ce, “Kana gudu daga Babiloniyawa ne!”
14 Et Jérémie répondit: cela n'est point; je ne vais point me rendre aux Caldéens; mais il ne l'écouta point, et Jireija prit Jérémie, et l'amena vers les principaux.
Sai Irmiya ya ce, “Ba gaskiya ba ce, ba na gudu daga Babiloniyawa.” Amma Iriya bai saurare shi ba; a maimako, ya kama Irmiya ya kawo shi wurin fadawa.
15 Et les principaux se mirent en colère contre Jérémie, et le battirent, et le mirent en prison dans la maison de Jéhonathan le Secrétaire, car ils en avaient fait un lieu de prison.
Suka yi fushi da Irmiya suka sa aka yi masa dūka aka kuma jefa shi cikin kurkuku a gidan Yonatan magatakarda, gama an mai da gidansa ya zama kurkuku.
16 Et ainsi Jérémie entra dans la fosse, et dans les cachots; et Jérémie y demeura plusieurs jours.
Aka sa Irmiya a can cikin kurkuku, inda ya kasance kwanaki masu yawa.
17 Mais le Roi Sédécias y envoya, et l'en tira, et il l'interrogea en secret dans sa maison, et lui dit: y a-t-il quelque parole de par l'Eternel? Et Jérémie répondit: il y en a; et lui dit: tu seras livré entre les mains du Roi de Babylone.
Sa’an nan Sarki Zedekiya ya aika a kawo shi aka kuma kawo shi fada, inda ya tambaye shi a kaɗaice ya ce, “Akwai wata magana daga Ubangiji?” Irmiya ya amsa ya ce, “I, za a ba da kai ga sarkin Babilon.”
18 Puis Jérémie dit au Roi Sédécias: quelle faute ai-je commise contre toi, et envers tes serviteurs, et envers ce peuple, pour m'avoir mis en prison?
Sai Irmiya ya ce wa Sarki Zedekiya, “Wane laifi na yi maka ko fadawanka ko kuwa wannan mutane, da ka sa aka jefa ni cikin kurkuku?
19 Mais où sont vos Prophètes qui vous prophétisaient, en disant: le Roi de Babylone ne reviendra point contre vous, ni contre ce pays?
Ina annabawanka waɗanda suka yi maka annabci suna cewa, ‘Sarkin Babilon ba zai yaƙe ka ko wannan ƙasa ba’?
20 Or écoute maintenant, je te prie, ô Roi mon Seigneur! et que maintenant ma supplication soit reçue devant ta face, et ne me renvoie point dans la maison de Jéhonathan le Secrétaire, de peur que je n'y meure.
Amma yanzu, ranka yă daɗe, sarkina, ka saurara. Bari in kawo kukata a gabanka. Kada ka mai da ni gidan Yonatan magatakarda, in ba haka zan mutu a can.”
21 C'est pourquoi le Roi Sédécias commanda qu'on gardât Jérémie dans la cour de la prison, et qu'on lui donnât tous les jours un pain de la place des boulangers, jusqu’à ce que tout le pain de la ville fût consumé. Ainsi Jérémie demeura dans la cour de la prison.
Sarki Zedekiya ya yi umarni a ajiye Irmiya a sansanin matsara a kuma ba shi burodi daga titin masu gashin burodi kowace rana sai duka burodi a birnin ya ƙare. Saboda haka Irmiya ya zauna a sansanin matsara.

< Jérémie 37 >