< Jérémie 7 >

1 La parole fut [adressée] à Jérémie par l'Eternel, en disant:
Maganar da ta zo wa Irmiya ke nan daga Ubangiji.
2 Tiens-toi debout à la porte de la maison de l'Eternel, et y crie cette parole, et dis: vous tous hommes de Juda qui entrez par ces portes, pour vous prosterner devant l'Eternel, écoutez la parole de l'Eternel;
“Ka tsaya a ƙofar gidan Ubangiji, a can kuwa ka yi shelar wannan saƙo. “‘Ku ji maganar Ubangiji, dukanku mutanen Yahuda waɗanda suke shiga ta waɗannan ƙofofi don yin sujada ga Ubangiji.
3 Ainsi a dit l'Eternel des armées, le Dieu d'Israël: corrigez votre vie et vos actions, et je vous ferai habiter en ce lieu-ci.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allahna Isra’ila, yana cewa ku gyara hanyoyinku da ayyukanku, zan kuwa bar ku ku zauna a wannan wuri.
4 Ne vous fiez point sur des paroles trompeuses, en disant: c'est ici le Temple de l'Eternel, le Temple de l'Eternel, le Temple de l'Eternel.
Kada ku dogara ga maganganun nan na ruɗarwa cewa, “Wannan shi ne haikalin Ubangiji, haikalin Ubangiji, haikalin Ubangiji!”
5 Mais corrigez sérieusement votre conduite et vos actions, et appliquez-vous à faire droit à ceux qui plaident l'un contre l'autre.
In dai kuka canja hanyoyinku da ayyukanku kuma kuna aikata adalci da junanku,
6 Et ne faites point de tort à l'étranger, ni à l'orphelin, ni à la veuve; et ne répandez point en ce lieu-ci le sang innocent, et ne marchez point après les dieux étrangers, à votre ruine.
in ba ku zalunci baƙo, maraya ko gwauruwa ba kuma in ba ku zub da jinin marar laifi a wannan wuri ba, in kuma ba ku bi waɗansu alloli da za su cuce ku ba,
7 Et je vous ferai habiter depuis un siècle jusqu’à l'autre siècle en ce lieu-ci, au pays que j'ai donné à vos pères.
to, zan bar ku ku zauna a wannan wuri, a ƙasar da na ba kakanninku har abada abadin.
8 Voici, vous vous fiez sur des paroles trompeuses, sans aucun profit.
Amma ga shi, kuna dogara ga maganganu na ruɗami marasa amfani.
9 Ne dérobez-vous pas? ne tuez-vous pas? ne commettez-vous pas adultère? ne jurez-vous pas faussement? ne faites-vous pas des encensements à Bahal? n'allez-vous pas après les dieux étrangers, que vous ne connaissez point?
“‘Za ku yi sata da kisa, ku yi zina da rantsuwar ƙarya, kuna ƙone turare wa Ba’al kuna kuma bin waɗansu allolin da ba ku sani ba,
10 Toutefois vous venez, et vous vous présentez devant moi dans cette maison, sur laquelle mon Nom est réclamé, et vous dites: nous avons été délivrés pour faire toutes ces abominations.
sa’an nan ku zo ku tsaya a gabana a wannan gida, wanda ake kira da Sunana, kuna cewa, “An cece mu,” mun dace mu aikata waɗannan abubuwa banƙyama?
11 Cette maison, sur laquelle mon Nom est réclamé devant vos yeux, n'est-elle pas devenue une caverne de brigands? et voici, moi-même je l'ai vu, dit l'Eternel.
Wannan gidan da ake kira da Sunana ya zama kogon’yan fashi ne a gare ku? Amma ina kallo! In ji Ubangiji.
12 Mais allez maintenant à mon lieu, qui était à Silo, là où j'avais placé mon Nom dès le commencement, et regardez ce que je lui ai fait, à cause de la malice de mon peuple d'Israël.
“‘Yanzu ku fita zuwa Shilo inda na fara maishe shi wurin zama don Sunana, ku ga abin da na yi masa saboda muguntar mutanen Isra’ila.
13 Maintenant donc, parce que vous faites toutes ces choses, dit l'Eternel, et que je vous ai parlé, me levant dès le matin, et parlant, et que vous n'avez point écouté; je vous ai appelés, et vous n'avez point répondu:
Yayinda kuke yin dukan waɗannan abubuwa, in ji Ubangiji, na yi muku magana sau da sau, amma ba ku ji ba; na kira ku, amma ba ku amsa ba.
14 Je ferai à cette maison, sur laquelle mon Nom est réclamé, et sur laquelle vous vous fiez, et à ce lieu que je vous ai donné à vous et à vos pères, comme j'ai fait à Silo.
Saboda haka, abin da na yi wa Shilo shi ne yanzu zan yi wa gidan da ake kira da Sunana, haikalin da kuka dogara a kai, wurin da na ba ku da kuma kakanninku.
15 Et je vous chasserai de devant ma face, comme j'ai chassé tous vos frères, avec toute la postérité d'Ephraïm.
Zan kore ku daga gabana, kamar yadda na yi ga dukan’yan’uwanku, mutanen Efraim.’
16 Toi donc ne prie point pour ce peuple, et ne jette point de cri, et ne fais point de requête pour eux, et n'intercède point envers moi; car je ne t'exaucerai point.
“Saboda haka kada ka yi addu’a don wannan mutane ko ka yi wani kuka ko roƙo dominsu, gama ba zan ji ka ba.
17 Ne vois-tu pas ce qu'ils font dans les villes de Juda, et dans les rues de Jérusalem?
Ba ka gani abin da suke yi a biranen Yahuda da kuma a titunan Urushalima?
18 Les fils amassent le bois, et les pères allument le feu, et les femmes pétrissent la pâte pour faire des gâteaux à la Reine des cieux; et pour faire des aspersions aux dieux étrangers, afin de m'irriter.
Yara sukan tara itace, iyaye suka hura wuta, mata kuma sukan kwaɓa kullu don su yi wa Sarauniyar Sama waina. Sukan miƙa hadayun sha ga waɗansu alloli don su tsokane ni in yi fushi.
19 Ce qu'ils m'irritent est-il contre moi? dit l'Eternel. N'est-ce pas contre eux-mêmes, à la confusion de leurs faces?
Amma ni ne suke tsokana? In ji Ubangiji Ashe, ba kansu ne suke cuta, suna kunyata kansu ba?
20 C'est pourquoi ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: voici, ma colère et ma fureur vont fondre sur ce lieu-ci, sur les hommes et sur les bêtes, sur les arbres des champs, et sur le fruit de la terre, ma colère s'embrasera, et ne s'éteindra point.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa fushina da hasalata za su kwarara a wannan wuri, a kan mutum da dabba, a kan itatuwan fili da a kan amfanin gona, za su yi ta kuna, ba kuwa za a kashe ba.
21 Ainsi a dit l'Eternel des armées, le Dieu d'Israël: ajoutez vos holocaustes à vos sacrifices, et mangez-en la chair.
“‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa ci gaba, ku ƙara hadayun ƙonawarku da sauran sadakoki ku kuma yi ta cin naman!
22 Car je n'ai point parlé avec vos pères, et je ne leur ai point donné de commandement touchant les holocaustes et les sacrifices, au jour que je les fis sortir du pays d'Egypte.
Gama sa’ad da na fitar da kakanninku daga Masar na kuma yi musu magana, ban ba su dokoki kawai game da hadayun ƙonawa da sadakoki ba,
23 Mais voici ce que je leur ai commandé, disant: écoutez ma voix, et je serai votre Dieu, et vous serez mon peuple; et marchez dans toutes les voies que je vous ai ordonnées, afin que vous soyez heureux.
amma na ba su wannan umarni cewa ku yi mini biyayya, zan kuwa zama Allahnku ku kuma ku zama mutanena. Ku yi tafiya cikin dukan hanyoyin da na umarce ku, don ku zauna lafiya.
24 Mais ils n'ont point écouté, et n'ont point incliné leur oreille; mais ils ont suivi [d'autres] conseils, et la dureté de leur cœur mauvais, ils se sont éloignés et ne sont point retournés jusques à moi.
Amma ba su saurara ba, ba su kuwa kula ba; a maimako, suka bi shawarar kansu da ta taurare muguwar zukatansu. Su ja da baya a maimakon yin gaba.
25 Depuis le jour que vos pères sont sortis du pays d'Egypte, jusqu’à aujourd'hui, je vous ai envoyé tous mes serviteurs Prophètes, me levant [chaque] jour dès le matin, et les envoyant.
Daga lokacin da kakanninku suka bar Masar har yă zuwa yau, kullum na yi ta aikan bayina annabawa.
26 Mais ils ne m'ont point écouté, et ils n'ont point incliné leur oreille, mais ils ont raidi leur cou; ils ont fait pis que leurs pères.
Amma ba su saurare ni ba, ba su kula ba. Sai suka taurare zukatansu suka aikata mugun abu fiye da na kakanninsu.’
27 Tu leur diras donc toutes ces paroles, mais ils ne t'écouteront point; et tu crieras après eux, mais ils ne te répondront point.
“Sa’ad da ka faɗa musu wannan duka, ba za su saurare ka ba; sa’ad da ka kira su, ba za su amsa ba.
28 C'est pourquoi tu leur diras: [c'est] ici la nation qui n'a point écouté la voix de l'Eternel son Dieu, et qui n'a point reçu d'instruction; la fidélité est périe, et elle a été retranchée de leur bouche.
Saboda haka ka faɗa musu cewa, ‘Wannan ce al’ummar da ba tă yi biyayya ga Ubangiji Allahnta ba, ba kuwa ta karɓi gyara ba. Gaskiya ta ƙare; ta ɓace gaba ɗaya daga leɓunansu.
29 Tonds ta chevelure, [ô Jérusalem!] et [la] jette au loin, et prononce à haute voix ta complainte sur les lieux élevés; car l'Eternel a rejeté et abandonné la génération contre laquelle il est fort courroucé.
“‘Ku aske gashin kanku ku zubar; ku yi makoki a filayen tuddai, gama Ubangiji ya ƙi’yan zamanin nan ya kuma rabu da su saboda fushin da suka ba shi.
30 Parce que les enfants de Juda ont fait ce qui me déplaît, dit l'Eternel, ils ont mis leurs abominations dans cette maison, sur laquelle mon Nom est invoqué, afin de la souiller.
“‘Mutanen Yahuda sun yi mugunta a gabana, in ji Ubangiji. Sun kafa gumakansu masu banƙyama a gidan da ake kira da Sunana suka ƙazantar da shi.
31 Et ils ont bâti les hauts lieux de Topheth, qui [est] dans la vallée du fils de Hinnom, pour brûler leurs fils et leurs filles au feu, ce que je n'ai pas commandé, et à quoi je n'ai jamais pensé.
Sun gida masujadan Tofet a Kwarin Ben Hinnom don miƙa’ya’yansu maza da mata a wuta, abin da ban yi umarni ba, ba kuwa yi tunaninsa ba.
32 C'est pourquoi voici, les jours viennent, dit l'Eternel, qu'elle ne sera plus appelée Topheth, ni la vallée du fils de Hinnom, mais la vallée de la tuerie, et on ensevelira [les morts] à Topheth, à cause qu'il n'y aura plus [d'autre] lieu.
Saboda haka ku yi hankali, kwanaki suna zuwa in ji Ubangiji, sa’ad da mutane ba za su ƙara kira wurin Tofet ko Kwarin Ben Hinnom ba, amma Kwarin Kisa, gama za su binne matattu a Tofet sai har ba sauran wuri.
33 Et les corps morts de ce peuple seront pour viande aux oiseaux des cieux, et aux bêtes de la terre, sans qu'il y ait personne qui les effarouche.
Sa’an nan gawawwakin wannan mutane za su zama abinci ga tsuntsayen sama da kuma namun jeji, ba za a kuwa sami wani da zai kore su ba.
34 Je ferai aussi cesser des villes de Juda, et des rues de Jérusalem, la voix de joie, et la voix d'allégresse, la voix de l'époux, et la voix de l'épouse, car le pays sera mis en désolation.
Zan kawo ƙarshen muryar murna da farin ciki da muryar amarya da ango a garuruwan Yahuda da kuma a titunan Urushalima, gama ƙasar za tă zama kufai.

< Jérémie 7 >