< Job 12 >

1 Mais Job répondit, et dit:
Sai Ayuba ya amsa,
2 Vraiment, êtes-vous tout un peuple; et la sagesse mourra-t-elle avec vous?
“Ba shakka ku ne mutanen nan, hikima za tă mutu tare da ku!
3 J'ai du bon sens aussi bien que vous, et je ne vous suis point inférieur; et qui [est-ce qui ne sait] de telles choses?
Amma ni ma ina da hankali kamar ku; ba ku fi ni ba. Wane ne bai san duk waɗannan abubuwan ba?
4 Je suis un homme qui est en risée à son ami, [mais] qui invoquera Dieu, et Dieu lui répondra. On se moque d'un homme qui est juste et droit.
“Na zama abin dariya ga abokaina, ko da yake na yi kira ga Allah ya kuwa amsa mini, duk da haka suka yi mini riya ko da yake ni mai adalci ne kuma marar laifi!
5 Celui dont les pieds sont tout prêts à glisser, est selon la pensée de celui qui est à son aise, un flambeau dont on ne tient plus de compte.
Mutanen da ba su da damuwa suna jin daɗin ganin waɗanda suke dab da fāɗuwa.
6 Ce sont les tentes des voleurs [qui] prospèrent, et ceux-là sont assurés qui irritent le [Dieu] Fort, et ils sont ceux à qui Dieu remet tout entre les mains.
Amma wurin zaman’yan fashi yana nan ba mai damunsu, waɗanda kuma suke saɓa wa Allah suna zamansu lafiya, har ma da masu ɗaukar allahnsu a hannuwansu.
7 Et, en effet, je te prie, interroge les bêtes, et [chacune d'elles] t'enseignera; ou les oiseaux des cieux, et ils te le déclareront;
“Amma ka tambayi dabbobi, za su kuma koya maka, ko kuma tsuntsayen sararin sama kuma za su gaya maka.
8 Ou parle à la terre, et elle t'enseignera; même les poissons de la mer te le raconteront;
Ko ka yi magana da duniya, za tă kuma koya maka, ko kuma ka bar kifin teku su sanar da kai.
9 Qui est-ce qui ne sait toutes ces choses, [et] que c'est la main de l'Eternel qui a fait cela?
Wane ne cikin waɗannan bai san cewa hannun Ubangiji ne ya yi wannan ba?
10 [Car c'est lui] en la main duquel est l'âme de tout ce qui vit, et l'esprit de toute chair humaine.
Ran kowace halitta yana a hannunsa, haka kuma numfashin dukan’yan adam.
11 L'oreille ne discerne-t-elle pas les discours, ainsi que le palais savoure les viandes?
Ko kunne ba ya gwada kalmomi kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci?
12 La sagesse est dans les vieillards, et l'intelligence [est le fruit] d'une longue vie.
Ko ba a wurin tsofaffi ake samun hikima ba? Ba tsawon rai yana kawo ganewa ba?
13 Mais en lui est la sagesse et la force; à lui appartient le conseil et l'intelligence.
“Allah ne mai iko da kuma hikima, shawara da ganewa nasa ne.
14 Voilà, il démolira, et on ne rebâtira point; s'il ferme sur quelqu'un, on n'ouvrira point.
Abin da ya rushe ba a iya ginawa ba; in ya kulle mutum ba a iya buɗe shi a sake shi ba.
15 Voilà, il retiendra les eaux, et tout deviendra sec; il les lâchera, et elles renverseront la terre.
Idan ya hana ruwan sama, za a yi fări; in kuma ya saki ruwa za a yi ambaliya.
16 En lui est la force et l'intelligence; à lui est celui qui s'égare, et celui qui le fait égarer.
Shi ne mai ƙarfi da kuma mai nasara; mai ruɗi da wanda aka ruɗa, duk nasa ne.
17 Il emmène dépouillés les conseillers, et il met hors du sens les juges.
Yakan sa mashawarta su zama marasa hikima yă kuma sa wawaye su zama masu shari’a.
18 Il détache la ceinture des Rois, et il serre leurs reins de sangles.
Yana cire sarƙar da sarakuna suka ɗaura yă kuma ɗaura musu wata tsumma a kwankwaso.
19 Il emmène nus ceux qui sont en autorité, et il renverse les forts.
Yakan ƙasƙantar da firistoci yă kuma tumɓuke masu ikon da aka kafa tun da daɗewa.
20 Il ôte la parole à ceux qui sont les plus assurés en leurs discours, et il prive de sens les anciens.
Yana sa amintattun mashawarta su yi shiru yakan kawar da hikimar dattawa.
21 Il répand le mépris sur les principaux; il rend lâche la ceinture des forts.
Yakan sa masu iko su ji kunya yă kuma ƙwace ƙarfin masu ƙarfi.
22 Il met en évidence les choses qui étaient cachées dans les ténèbres, et il produit en lumière l'ombre de la mort.
Yana buɗe abubuwan da suke cikin duhu yă kuma kawo haske a wuraren da ba haske;
23 Il multiplie les nations, et les fait périr; il répand çà et là les nations, et puis il les ramène.
yana sa al’ummai su zama manya, sai kuma yă hallaka su; yana sa al’ummai su ƙasaita, yă kuma watsar da su.
24 Il ôte le cœur aux Chefs des peuples de la terre, et les fait errer dans les déserts où il n'y a point de chemin.
Yana hana shugabannin duniya ganewa; Ya bar su su yi ta makuwa, su ruɗe, su ɓata.
25 Ils vont à tâtons dans les ténèbres, sans aucune clarté, et il les fait chanceler comme des gens ivres.
Suna lallube cikin duhu ba haske; yă sa su yi ta tangaɗi kamar bugaggu.

< Job 12 >