< Job 31 >

1 J'avais fait accord avec mes yeux; comment aurais-je donc arrêté mes regards sur une vierge?
“Na yi alkawari da idanuna kada su dubi budurwa da muguwar sha’awa.
2 Et quelle [serait] la portion [que] Dieu [m'aurait envoyée] d'en haut, et quel eût été l'héritage que le Tout-puissant m'eût [envoyé] des hauts lieux?
Gama mene ne rabon mutum daga Allah a sama, gādonsa daga Maɗaukaki a sama?
3 La perdition n'est-elle pas pour l'injuste, et les accidents étranges pour les ouvriers d'iniquité?
Ba masifa ba ne domin mugaye, hallaka kuma ga waɗanda suka yi ba daidai ba?
4 N'a-t-il pas vu lui-même mes voies, et n'a-t-il pas compté toutes mes démarches?
Bai ga hanyoyina ba ne bai ƙirga kowace takawata ba?
5 Si j'ai marché dans le mensonge, et si mon pied s'est hâté à tromper,
“In da na yi tafiya cikin rashin gaskiya ko kuma ƙafata ta yi sauri zuwa yin ƙarya,
6 Qu'on me pèse dans des balances justes, et Dieu connaîtra mon intégrité.
Bari Allah yă auna a kan ma’auni na gaskiya zai kuma san cewa ni marar laifi ne.
7 Si mes pas se sont détournés du [droit] chemin, et si mon cœur a marché après mes yeux, et si quelque tache s'est attachée à mes mains,
In takawata ta kauce daga hanya, in zuciyata ta bi abin da idanuna ke so, ko kuma in hannuwana suna da laifi;
8 Que je sème, et qu'un autre mange [ce que j'aurai semé]; et que tout ce que j'aurai fait produire, soit déraciné!
bari waɗansu su ci abin da na shuka, kuma bari a tuge amfanin gonata.
9 Si mon cœur a été séduit après quelque femme, et si j'ai demeuré en embûche à la porte de mon prochain,
“In sha’awar mace ya shiga mini zuciya, ko kuma na laɓe a ƙofar maƙwabcina,
10 Que ma femme soit déshonorée par un autre, et qu'elle soit prostituée à d'autres!
sai matata ta niƙa hatsin wani kuma waɗansu maza su kwana da ita.
11 Vu que c'est une méchanceté préméditée, une de ces iniquités qui sont toutes jugées.
Gama wannan zai zama abin kunya, zunubin da za a yi shari’a a kai.
12 Car c'est un feu qui dévore jusqu'à consumer, et qui aurait déraciné tout mon revenu.
Wuta ce take ƙuna har ta hallakar; za tă cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus.
13 Si j'ai refusé de faire droit à mon serviteur ou à ma servante, quand ils ont contesté avec moi;
“In da na danne wa bayina maza da mata hakkinsu, sa’ad da suke da damuwa da ni,
14 Car qu'eussé-je fait, quand le [Dieu] Fort se fût levé? et quand il m'en eût demandé compte, que lui aurais-je répondu?
me zan yi lokacin da Allah ya tuhume ni? Me zan ce lokacin da ya tambaye ni?
15 Celui qui m'a formé dans le ventre, ne les a-t-il pas faits aussi? et ne nous a-t-il pas tous formés de la même manière dans la matrice?
Shi wanda ya yi ni a cikin uwata ba shi ne ya yi su ba? Ba shi ne ya yi mu a cikin uwayenmu ba?
16 Si j'ai refusé aux pauvres ce qu'ils ont désiré; si j'ai fait consumer les yeux de la veuve;
“In na hana wa matalauta abin da suke so, ko kuma in sa idanun gwauruwa su yi nauyi don kuka,
17 Si j'ai mangé seul mes morceaux, et si l'orphelin n'en a point mangé;
in na ajiye burodina don kaina kaɗai, ban kuwa ba wa marayu abinci sa’ad da suke jin yunwa,
18 (Car dès ma jeunesse il a été élevé avec moi, comme [chez son père], et dès le ventre de ma mère j'ai conduit l'orphelin.)
amma tun suna tasowa na lura da su, kamar yadda mahaifi zai lura da ɗa, kuma tun da aka haife ni ina lura da gwauruwa.
19 Si j'ai vu un homme périr faute d'être vêtu, et le pauvre faute de couverture;
In da na ga wani yana mutuwa don rashin sutura, ko wani mai bukata da ba shi da riga,
20 Si ses reins ne m'ont point béni, et s'il n'a pas été échauffé de la laine de mes agneaux;
kuma zuciyarsa ba tă gode mini ba don na yi masa sutura da gashin tumakina,
21 Si j'ai levé la main contre l'orphelin, quand j'ai vu à la porte, que je pouvais l'aider;
in na ɗaga hannuna don in cuci maraya, domin na san in na faɗa za a ji ni a wurin masu shari’a,
22 Que l'os de mon épaule tombe et que mon bras soit cassé, et séparé de l'os auquel il est joint!
bari hannuna yă guntule daga kafaɗata, bari yă tsinke daga inda aka haɗa shi.
23 Car j'ai eu frayeur de l'orage du [Dieu] Fort, et je ne saurais [subsister] devant sa majesté.
Gama ina jin tsoron hallaka daga Allah, kuma domin tsoron ɗaukakarsa ba zan iya yin waɗannan abubuwa ba.
24 Si j'ai mis mon espérance en l'or, et si j'ai dit au fin or: Tu es ma confiance;
“In na dogara ga zinariya ko kuma na ce wa zallan zinariya, ‘Gare ki nake dogara,’
25 Si je me suis réjoui de ce que mes biens étaient multipliés, et de ce que ma main en avait trouvé abondamment;
in na yi fahariya don yawan dukiyata, arzikin da hannuwana suka samu.
26 Si j'ai regardé le soleil lorsqu'il brillait le plus, et la lune marchant noblement;
In na dubi rana cikin haskenta, ko kuma wata yana tafiyarsa,
27 Et si mon cœur a été séduit en secret, et si ma main a baisé ma bouche;
zuciyata ta jarrabtu gare su a ɓoye, hannuna kuma ya sumbace su.
28 (Ce qui est aussi une iniquité toute jugée; car j'eusse renié le Dieu d'en haut.)
Waɗannan ma za su zama zunubin da za a shari’anta ke nan don zai zama na yi wa Allah na sama rashin aminci.
29 Si je me suis réjoui du malheur de celui qui me haïssait; si j'ai sauté de joie quand il lui est arrivé du mal.
“In na yi murna domin mugun abu ya faru da maƙiyina; ko kuma domin wahala ta same shi,
30 Je n'ai pas même permis à ma langue de pécher, en demandant sa mort avec imprécation.
ban bar bakina yă yi zunubi ta wurin la’anta shi ba,
31 Et les gens de ma maison n'ont point dit: Qui nous donnera de sa chair? nous n'en saurions être rassasiés.
in mutanen gidana ba su taɓa cewa, ‘Wane ne bai ƙoshi da naman Ayuba ba?’
32 L'étranger n'a point passé la nuit dehors; j'ai ouvert ma porte au passant.
Ba baƙon da ya taɓa kwana a titi, gama koyaushe ƙofata tana buɗe domin matafiya,
33 Si j'ai caché mon péché comme Adam, pour couvrir mon iniquité en me flattant.
in na ɓoye zunubina yadda mutane suke yi, ta wurin ɓoye laifina a cikin zuciyata,
34 Quoique je pusse me faire craindre à une grande multitude, toutefois le moindre qui fût dans les familles m'inspirait de la crainte, et je me tenais dans le silence, et ne sortais point de la porte.
domin ina tsoron taron mutane kuma ina tsoron wulaƙancin da dangina za su yi mini, sai na yi shiru kuma ban fita waje ba.
35 Ô! s'il y avait quelqu'un qui voulût m'entendre. Tout mon désir est que le Tout-puissant me réponde, et que ma partie adverse fasse un écrit [contre moi].
(“Kash, da ina da wanda zai ji ni! Na sa hannu ga abin da na faɗa don kāre kaina, bari Maɗaukaki yă amsa mini; bari mai tuhumata da laifi yă yi ƙarata a rubuce.
36 Si je ne le porte sur mon épaule, et si je ne l'attache comme une couronne.
Ba shakka sai in ɗora a kafaɗata, zan aza a kaina kamar rawani.
37 Je lui raconterais tous mes pas, je m'approcherais de lui comme d'un Prince.
Zan ba shi lissafin duk abin da na taɓa yi; zan zo gabansa kamar ɗan sarki.)
38 Si ma terre crie contre moi, et si ses sillons pleurent;
“In ƙasata tana kuka da ni kunyoyinta duk sun cika da hawaye,
39 Si j'ai mangé son fruit sans argent; si j'ai tourmenté l'esprit de ceux qui la possédaient.
in na kwashe amfaninta ban biya ba ko kuma na kashe masu ita,
40 Qu'elle me produise des épines au lieu de blé, et de l'ivraie au lieu d'orge. C'est ici la fin des paroles de Job.
bari ƙaya ta fito a maimakon alkama ciyawa kuma a maimakon sha’ir.” Maganar Ayuba ta ƙare.

< Job 31 >