< Lévitique 6 >

1 L'Eternel parla aussi à Moïse, en disant:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Quand quelque personne aura péché, et aura commis un crime contre l'Eternel, en mentant à son prochain pour un dépôt, ou pour une chose qu'on aura mise entre ses mains, soit qu'il l'ait ravie, soit qu'il ait trompé son prochain.
“In wani ya yi zunubi bai kuma yi aminci ga Ubangiji ba, wato, ta wurin yin wa abokin zamansa karya game da ajiyar da abokin ya ba shi amana, ko a kan wani alkawarin da suka yi wa juna, ko kuwa a kan yă cuci abokin,
3 Ou s'il a trouvé quelque chose perdue, et qu'il mente à ce sujet; ou s'il jure faussement sur quelqu'une de toutes les choses qu'il arrive à l'homme de faire, en péchant à leur égard;
ko kuma idan ya sami abin da ya ɓace amma ya yi ƙarya cewa bai samu ba. Ko ya yi rantsuwar ƙarya a kan duk irin abubuwan da akan aikata na laifi,
4 S'il arrive donc qu'il ait péché, et qu'il soit trouvé coupable, il rendra la chose qu'il aura ravie, ou ce qu'il aura usurpé par tromperie, ou le dépôt qui lui aura été donné en garde, ou la chose perdue qu'il aura trouvée;
sa’ad da mutum ya yi irin laifin nan, ya kuwa tabbata mai laifi ne, to, sai yă komar da abin da ya ƙwace, ko abin da ya samu ta hanyar zalunci, ko abin da aka ba shi ajiya, ko abin da ya tsinta.
5 Ou tout ce dont il aura juré faussement; il restituera le principal, et il ajoutera un cinquième par dessus à celui-là qui il appartenait; il le donnera le jour qu'il aura été déclaré coupable.
Zai mai da abin da ya yi rantsuwar ƙarya a kai. Zai mayar wa mai abin da abinsa a yadda yake, har yă ƙara kashi ashirin bisa ɗari na abin. A ranar da zai yi hadaya don laifinsa, a ranar ce zai mayar wa mai abin da abinsa.
6 Et il amènera pour l'Eternel au Sacrificateur [la victime de] son péché, [savoir] un bélier sans tare, [pris] du troupeau, avec l'estimation que tu feras de la faute.
A matsayin hakki kuwa, dole yă kawo wa firist, wato, ga Ubangiji, hadaya rago marar lahani kuma wanda aka kimanta tamaninsa daga garke don laifinsa.
7 Et le Sacrificateur fera propitiation pour lui devant l'Eternel; et il lui sera pardonné, pour tout ce qu'il aura fait en quoi il se sera rendu coupable.
Ta haka firist zai yi kafara dominsa a gaban Ubangiji, za a kuwa gafarta masa irin laifin da ya yi.”
8 L'Eternel parla aussi à Moïse, en disant:
Ubangiji ya ce wa Musa,
9 Commande à Aaron et à ses fils, et leur dis: C'est ici la Loi de l'holocauste; l'holocauste [demeurera] sur le feu qui est sur l'autel, toute la nuit jusqu'au matin, et le feu de l'autel y sera tenu allumé.
“Ka ba Haruna da’ya’yansa maza wannan umarni, ‘Waɗannan su ne ƙa’idodi don hadaya ta ƙonawa. Hadaya ta ƙonawa za tă kasance a bagade dukan dare, sai da safe, kuma dole a bar wutar tă yi ta ci a bisa bagaden.
10 Et le Sacrificateur, vêtu de sa robe de lin, mettra ses caleçons de lin sur sa chair, et il lèvera les cendres après que le feu aura consumé l'holocauste sur l'autel; puis il les mettra près de l'autel.
Sa’an nan firist zai sa rigunarsa ta lilin da kuma rigar lilin da ake sa a ciki, sa’an nan yă kwashe tokan hadaya ta ƙonawa da wuta da ta ci a kan bagaden, yă sa kusa da bagaden.
11 Alors il dépouillera ses vêtements, et s'étant vêtu d'autres habits, il transportera les cendres hors du camp, en un lieu net.
Sa’an nan yă tuɓe waɗannan rigunan yă sa waɗansu, sa’an nan yă ɗauki tokar yă kai waje da sansani zuwa inda yake da tsabta.
12 Et quant au feu qui est sur l'autel, on l'y tiendra allumé, [et] on ne le laissera point éteindre. Le Sacrificateur allumera du bois au feu tous les matins, il arrangera l'holocauste sur le bois, et y fera fumer les graisses des offrandes de prospérités.
Dole a bar wutar da take bisa bagaden tă yi ta ci; kada tă mutu. Kowace safiya firist zai ƙara itacen wuta, yă shirya hadaya ta ƙonawa a bisa wutar yă kuma ƙone kitsen hadaya ta salama a kansa.
13 On tiendra le feu continuellement allumé sur l'autel, [et] on ne le laissera point éteindre.
Dole a bar wutar tă ci gaba da ci a bisa bagade; kada tă mutu.
14 Et c'est ici la Loi de l'offrande du gâteau; les fils d'Aaron l'offriront devant l'Eternel sur l'autel.
“‘Waɗannan su ne ƙa’idodi domin hadaya ta gari.’Ya’yan Haruna za su kawo ta a gaban Ubangiji, a gaban bagaden.
15 Et on lèvera une poignée de la fleur de farine du gâteau, et de son huile, avec tout l'encens qui est sur le gâteau, et on le fera fumer en bonne odeur sur l'autel pour mémorial à l'Eternel.
Firist zai ɗiba garin hadayar mai laushin wanda aka zuba masa mai da kuma turare cike da tafin hannu. Zai ƙona wannan a bisa bagaden, hadaya ce mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji don tunawa.
16 Et Aaron et ses fils mangeront ce qui en restera; on le mangera sans levain dans un lieu saint, on le mangera dans le parvis du Tabernacle d'assignation.
Haruna da’ya’yansa maza za su ci sauran, amma za a ci shi ba tare da yisti ba a tsattsarkan wuri; za su ci shi a harabar Tentin Sujada.
17 On n'en cuira point qui soit fait avec du levain; je leur ai donné cela pour leur portion d'entre mes offrandes faites par feu; c'est une chose très-sainte, comme [la victime pour] le péché, et [la victime pour] le délit.
Ba za a toya shi da yisti ba; na ba su yă zama rabonsu daga cikin hadayun da ake ƙonawa da wuta, abu ne mafi tsarki, kamar hadaya don zunubi da laifi.
18 Tout mâle d'entre les fils d'Aaron en mangera; c'est une ordonnance perpétuelle en vos âges touchant les offrandes faites par feu à l'Eternel; quiconque les touchera sera sanctifié.
Kowane ɗa namiji cikin zuriyar Haruna zai iya cinsa. Wannan rabonsa ne na kullum na hadayar da aka yi ga Ubangiji da wuta. Wannan madawwamiyar doka ce cikin zamananku duka. Duk abin da ya taɓa hadayun zai tsarkaka.’”
19 L'Eternel parla aussi à Moïse, en disant:
Ubangiji ya kuma ce wa Musa,
20 C'est ici l'offrande d'Aaron et de ses fils, laquelle ils offriront à l'Eternel le jour qu'il sera oint, [savoir] la dixième partie d'un Epha de fine farine, pour offrande perpétuelle; une moitié le matin, [et] l'autre moitié le soir.
“Wannan ne hadayar da Haruna da’ya’yansa maza za su kawo ga Ubangiji a ranar da za a naɗa su firistoci, humushin garwan gari mai laushi a matsayin hadaya ta gari na kullum, rabinsa da safe, rabinsa kuma da yamma.
21 Elle sera apprêtée sur une plaque avec de l'huile, tu l'apporteras ainsi rissolée, et tu offriras les pièces cuites du gâteau en bonne odeur à l'Eternel.
A shirya shi da mai a kwanon tuya, a kawo shi kwaɓaɓɓe sosai, a miƙa shi hadaya ta gari dunƙule-dunƙule don ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji.
22 Et le Sacrificateur d'entre ses fils qui [sera] oint en sa place, fera cela par ordonnance perpétuelle; on le fera fumer tout entier à l'Eternel.
Duk wanda aka naɗa daga’ya’yan Haruna yă zama firist a madadinsa, shi ne zai miƙa wannan hadayar ga Ubangiji. Zai ƙone hadayar ƙurmus. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ce har abada.
23 Et tout le gâteau du Sacrificateur sera consumé, sans en manger.
Kowace hadaya ta gari ta firist, za a ƙone ta ƙurmus, ba za a ci ba.”
24 L'Eternel parla aussi à Moïse, en disant:
Ubangiji ya ce wa Musa,
25 Parle à Aaron et à ses fils, et leur dis: C'est ici la Loi [de la victime pour] le péché; [la victime] pour le péché sera égorgée devant l'Eternel, dans le [même] lieu où l'holocauste sera égorgé; [car] c'est une chose très-sainte.
“Faɗa wa Haruna da’ya’yansa maza, ‘Waɗannan su ne ƙa’idodi domin hadaya don zunubi. Za a yanka hadaya don zunubi a gaban Ubangiji a inda ake yankan hadaya ta ƙonawa; dole tă kasance mai tsarki.
26 Le Sacrificateur qui offrira [la victime] pour le péché, la mangera; elle se mangera dans un lieu saint, dans le parvis du Tabernacle d'assignation.
Firist da ya miƙa ta zai ci, za a ci ta a tsattsarkan wuri, a harabar Tentin Sujada.
27 Quiconque touchera sa chair sera saint, et s'il en rejaillit quelque sang sur le vêtement, ce sur quoi le sang sera tombé sera lavé dans le lieu saint.
Duk abin da ya taɓa wani sashe na naman, zai zama da tsarki, kuma in wani jini ya ɗiga a riga, dole ka wanke shi a tsattsarkan wuri.
28 Et le vaisseau de terre dans lequel on l'aura fait bouillir, sera cassé; mais si on l'a fait bouillir dans un vaisseau d'airain, il sera écuré, et lavé dans l'eau.
Dole a farfashe tukunyar lakar da aka dafa naman a ciki; amma in an dafa a tukunyar tagulla, sai a kankare tukunyar, a kuma ɗauraye da ruwa.
29 Tout mâle d'entre les Sacrificateurs en mangera; c'est une chose très-sainte.
Kowane namiji a iyalin firistoci zai iya ci; gama abu ne mafi tsarki.
30 Nulle [victime pour] le péché dont on portera du sang dans le Tabernacle d'assignation, pour faire la propitiation dans le Sanctuaire, ne sera mangée, mais elle sera brûlée au feu.
Amma duk wata hadaya don zunubi wadda aka kawo jininta cikin Tentin Sujada don a yi kafara a Wuri Mai Tsarki, ba za a ci ba. A maimako haka za a ƙone ta ɗungum.

< Lévitique 6 >