< Proverbes 24 >

1 Ne porte point d'envie aux hommes malins, et ne désire point d'être avec eux.
Kada ka yi ƙyashin mugaye, kada ka yi sha’awar ƙungiyarsu;
2 Car leur cœur pense à piller, et leurs lèvres parlent de nuire.
gama leɓunansu suna maganar tā-da-na-zaune-tsaye ne.
3 La maison sera bâtie par la sagesse, et sera affermie par l'intelligence.
Ta wurin hikima ce ake gina gida, kuma ta wurin fahimi ake kafa ta;
4 Et par la science les cabinets seront remplis de tous les biens précieux et agréables.
ta wurin sani ɗakunanta sukan cika da kyawawan kayayyaki masu daraja.
5 L'homme sage [est accompagné] de force, et l'homme qui a de l'intelligence renforce la puissance.
Mutum mai hikima yana da iko sosai, kuma mutum mai sani yakan ƙaru da ƙarfi;
6 Car par la prudence tu feras la guerre avantageusement, et la délivrance consiste dans le nombre des conseillers.
don yin yaƙi kana bukatar bishewa, kuma don ka yi nasara kana bukatar mashawarta masu yawa.
7 Il n'y a point de sagesse qui ne soit trop haute pour le fou; il n'ouvrira point sa bouche à la porte.
Hikima ta yi wa wawa nisa ƙwarai a cikin taro a ƙofar gari ba shi da ta cewa.
8 Celui qui pense à faire mal, on l'appellera, Songe-malice.
Duk mai ƙulla mugunta za a ɗauka shi mai kuta hargitsi ne.
9 Le discours de la folie n'est que péché, et le moqueur est en abomination à l'homme.
Makircin wawa zunubi ne, mutane kuma sukan yi ƙyamar mai ba’a.
10 Si tu as perdu courage dans la calamité, ta force s'est diminuée.
In ba ka da ƙarfi a lokacin wahala, ka tabbatar kai marar ƙarfi ne sosai!
11 Si tu te retiens pour ne délivrer point ceux qui sont traînés à la mort, et qui sont sur le point d'être tués,
Ka kuɓutar da waɗanda ake ja zuwa inda za a kashe su; ka riƙe waɗanda suke tangaɗi zuwa wajen yanka.
12 Parce que tu diras: Voici, nous n'en avons rien su; celui qui pèse les cœurs ne l'entendra-t-il point? et celui qui garde ton âme, ne le saura-t-il point? et ne rendra-t-il point à chacun selon son œuvre?
In kuka ce, “Ai, ba mu san wani abu a kai wannan ba,” shi da yake awon ba shi da zuciyar ganewa ne? Shi da yake tsare ranka bai sani ba ne? Ba zai sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya aikata ba?
13 Mon fils, mange le miel, car il est bon; et le rayon de miel, car il est doux à ton palais.
Ka sha zuma, ɗana, ka sha zuma gama tana da kyau; zuma daga kaki yana da zaƙi a harshenka.
14 Ainsi sera à ton âme la connaissance de la sagesse, quand tu l'auras trouvée; et il y aura une [bonne] issue, et ton attente ne sera point retranchée.
Ka kuma san cewa hikima tana da zaƙi ga rai; in ka same ta, akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
15 Méchant, n'épie point le domicile du juste, et ne détruis point son gîte.
Kada ka kwanta kana fako kamar ɗan iska don ƙwace gidan adali, kada ka ƙwace masa wurin zama;
16 Car le juste tombera sept fois, et sera relevé; mais les méchants tombent dans le mal.
gama ko da adali ya fāɗi sau bakwai, yakan tashi kuma, amma bala’i kan kwantar da mugaye.
17 Quand ton ennemi sera tombé, ne t'en réjouis point; et quand il sera renversé, que ton cœur ne s'en égaye point;
Kada ka yi dariya sa’ad da abokin gāba ya fāɗi; sa’ad da ya yi tuntuɓe, kada ka yi farin ciki,
18 De peur que l'Eternel ne [le] voie, et que cela ne lui déplaise, tellement qu'il détourne de dessus lui sa colère [sur toi.]
in ba haka ba in Ubangiji ya gani ba zai amince ba ya kuma juye fushinsa daga gare shi.
19 Ne te dépite point à cause des gens malins; ne porte point d'envie aux méchants;
Kada ka ji tsoro saboda masu mugunta ko ka yi ƙyashin mugaye,
20 Car il n'y aura point de [bonne] issue pour le méchant, et la lampe des méchants sera éteinte.
gama mugu ba shi da zuciya ta nan gaba, kuma fitilar mugaye za tă mutu.
21 Mon fils, crains l'Eternel, et le Roi; et ne te mêle point avec des gens remuants.
Ka ji tsoron Ubangiji da kuma sarki, ɗana, kuma kada ka haɗa kai da masu tayarwa,
22 Car leur calamité s'élèvera tout d'un coup; et qui sait l'inconvénient qui arrivera à ces deux-là?
gama za a tura waɗannan biyu zuwa hallaka nan da nan, kuma wa ya sani irin bala’in da za su iya kawowa?
23 Ces choses aussi sont pour les sages. Il n'est pas bon d'avoir égard à l'apparence des personnes en jugement.
Waɗannan ma maganganun masu hikima ne, Nunan sonkai a shari’a ba shi da kyau.
24 Celui qui dit au méchant: Tu es juste, les peuples le maudiront, et les nations l'auront en détestation.
Duk wanda ya ce wa mai laifi, “Ba ka da laifi”, mutane za su la’ance shi al’umma kuma za tă ce ba a san shi ba.
25 Mais pour ceux qui le reprennent, ils en retireront de la satisfaction, et la bénédiction que les biens accompagnent se répandra sur eux.
Amma zai zama da lafiya ga duk waɗanda suka hukunta masu laifi, kuma babban albarka zai zo a kansu.
26 Celui qui répond avec justesse fait plaisir [à celui qui l'écoute.]
Amsa da take ta gaskiya tana kamar sumba a leɓuna.
27 Range ton ouvrage dehors, et l'apprête au champ qui est à toi, et puis bâtis ta maison.
Ka gama aikinka ka kuma shirya gonakinka; bayan haka, ka gina gidanka.
28 Ne sois point témoin contre ton prochain, sans qu'il en soit besoin; car voudrais-tu t'en faire croire par tes lèvres?
Kada ka ba da shaida a kan maƙwabcinka ba tare da isashen dalili ba, ko ka yi amfani da leɓunanka ka yi ruɗu.
29 Ne dis point: comme il m'a fait, ainsi lui ferai-je; je rendrai à cet homme selon ce qu'il m'a fait.
Kada ka ce, “Zan yi masa kamar yadda ya yi mini; zan rama abin da wannan mutum ya yi mini.”
30 J'ai passé près du champ de l'homme paresseux, et près de la vigne de l'homme dépourvu de sens;
Na wuce cikin gonar rago, na wuce cikin gonar inabin mutumin da ba shi da azanci;
31 Et voilà, tout y était monté en chardons, et les orties avaient couvert le dessus, et sa cloison de pierres était démolie.
ƙayayyuwa sun yi girma ko’ina, ciyayi sun rufe ƙasar, katangar duwatsu duk ta rushe.
32 Et ayant vu cela, je le mis dans mon cœur, je le regardai, j'en reçus de l'instruction.
Na yi tunani a zuciyata na kuwa koyi darasi daga abin da na gani.
33 Un peu de dormir, un peu de sommeil, un peu de ploiement de bras pour demeurer couché,
Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi, ɗan naɗin hannuwa don a huta,
34 Et ta pauvreté viendra [comme] un passant; et ta disette, comme un soldat.
sai talauci ya shigo maka kamar’yan fashi rashi kuma ya zo maka kamar mai hari.

< Proverbes 24 >