< Psaumes 119 >

1 ALEPH. Bienheureux [sont] ceux qui sont intègres en leur voie, qui marchent en la Loi de l'Eternel.
Albarka ta tabbata ga waɗanda rayuwarsu ba ta da abin zargi, waɗanda suke tafiya bisa ga dokar Ubangiji.
2 Bienheureux sont ceux qui gardent ses témoignages, et qui le cherchent de tout leur cœur;
Albarka ta tabbata ga waɗanda suke kiyaye ƙa’idodinsa suke kuma nemansa da dukan zuciyarsu.
3 Qui aussi ne font point d'iniquité, [et] qui marchent dans ses voies.
Ba sa yin wani abin da ba daidai ba; suna tafiya a hanyoyinsa.
4 Tu as donné tes commandements afin qu'on les garde soigneusement.
Ka shimfiɗa farillan da dole a yi biyayya da su.
5 Qu'il te plaise, ô Dieu! que mes voies soient bien dressées, pour garder tes statuts.
Kash, da a ce hanyoyina tsayayyu ne a yin biyayya da ƙa’idodinka mana!
6 Et je ne rougirai point de honte, quand je regarderai à tous tes commandements.
Da ba zan sha kunya ba sa’ad da na lura da dukan umarnanka.
7 Je te célébrerai avec droiture de cœur, quand j'aurai appris les ordonnances de ta justice.
Zan yabe ka da zuciya ta gaskiya yayinda nake koyon dokokinka masu adalci.
8 Je veux garder tes statuts; ne me délaisse point entièrement.
Zan yi biyayya da ƙa’idodinka; kada ka yashe ni ɗungum.
9 BETH. Par quel moyen le jeune homme rendra-t-il pure sa voie? Ce sera en y prenant garde selon ta parole.
Yaya matashi zai kiyaye hanyarsa da tsabta? Sai ta yin rayuwa bisa ga maganarka.
10 Je t'ai recherché de tout mon cœur, ne me fais point fourvoyer de tes commandements.
Na neme ka da dukan zuciyata; kada ka bar ni in kauce daga umarnanka.
11 J'ai serré ta parole dans mon cœur, afin que je ne pèche point contre toi.
Na ɓoye maganarka a cikin zuciyata don kada in yi maka zunubi.
12 Eternel! tu es béni; enseigne-moi tes statuts.
Yabo ya tabbata gare ka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
13 J'ai raconté de mes lèvres toutes les ordonnances de ta bouche.
Da leɓunana na ba da labarin dukan dokokin da suka fito bakinka.
14 Je me suis réjoui dans le chemin de tes témoignages, comme si j'eusse eu toutes les richesses du monde.
Na yi farin ciki da bin farillanka yadda mutum yakan yi farin ciki da arziki mai yawa.
15 Je m'entretiendrai de tes commandements, et je regarderai à tes sentiers.
Na yi tunani a kan farillanka na kuma lura da hanyoyinka.
16 Je prends plaisir à tes statuts, et je n'oublierai point tes paroles.
Na yi murna a cikin ƙa’idodinka; ba zan ƙyale maganarka ba.
17 GUIMEL. Fais ce bien à ton serviteur que. je vive, et je garderai ta parole.
Ka yi alheri ga bawanka, zan kuwa rayu; zan yi biyayya da maganarka.
18 Dessille mes yeux, afin que je regarde aux merveilles de ta Loi.
Ka buɗe idanuna don in iya gani abubuwan banmamaki a cikin dokarka.
19 Je suis voyageur en la terre; ne cache point de moi tes commandements.
Ni baƙo ne a duniya; kada ka ɓoye mini umarnanka.
20 Mon âme est toute embrasée de l'affection qu'elle a de tout temps pour tes ordonnances.
Zuciyata ta ƙosa saboda marmari don dokokinka koyaushe.
21 Tu as rudement tancé les orgueilleux maudits, qui se détournent de tes commandements.
Ka tsawata wa masu fariya, waɗanda suke la’anta waɗanda kuma suka kauce daga umarnanka.
22 Ote de dessus moi l'opprobre et le mépris; car j'ai gardé tes témoignages.
Ka cire mini ba’a da reni, gama ina kiyaye farillanka.
23 Même les principaux se sont assis [et] ont parlé contre moi, pendant que ton serviteur s'entretenait de tes statuts.
Ko da yake masu mulki sun zauna tare suna ɓata mini suna, bawanka zai yi tunani a kan ƙa’idodinka.
24 Aussi tes témoignages [sont] mes plaisirs, [et] les gens de mon conseil.
Farillanka ne abin farin cikina; su ne mashawartana.
25 DALETH. Mon âme est attachée à la poudre; fais-moi revivre selon ta parole.
An kwantar da ni ƙasa cikin ƙura; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
26 Je t'ai déclaré au long mes voies, et tu m'as répondu; enseigne-moi tes statuts.
Na ba da labari hanyoyina ka kuma amsa mini; ka koya mini ƙa’idodinka.
27 Fais-moi entendre la voie de tes commandements, et je discourrai de tes merveilles.
Bari in gane koyarwar farillanka; sa’an nan zan yi tunani a kan abubuwan banmamakinka.
28 Mon âme s'est fondue d'ennui, relève moi selon tes paroles.
Raina ya gaji da baƙin ciki; ka ƙarfafa ni bisa ga maganarka.
29 Eloigne de moi la voie du mensonge, et me donne gratuitement ta Loi.
Ka kiyaye ni daga hanyoyin ruɗu; ka yi mini alheri ta wurin dokokinka.
30 J'ai choisi la voie de la vérité, et je me suis proposé tes ordonnances.
Na zaɓi hanyar gaskiya; na sa zuciyata a kan dokokinka.
31 J'ai été attaché à tes témoignages, ô Eternel! ne me fais point rougir de honte.
Na riƙe farillanka kankan, ya Ubangiji; kada ka sa in sha kunya.
32 Je courrai par la voie de tes commandements, quand tu auras mis mon cœur au large.
Ina gudu a kan hanyar umarnanka, gama ka’yantar da zuciyata.
33 HE. Eternel, enseigne-moi la voie de tes statuts, et je la garderai jusques au bout.
Ka koya mini Ya Ubangiji, don in bi ƙa’idodinka; sa’an nan zan kiyaye su har ƙarshe.
34 Donne-moi de l'intelligence; je garderai ta Loi, et je l'observerai de tout [mon] cœur.
Ka ba ni ganewa, zan kuwa kiyaye dokarka in kuma yi biyayya da ita da dukan zuciyata.
35 Fais-moi marcher dans le sentier de tes commandements; car j'y prends plaisir.
Ka bi da ni a hanyar umarnanka, gama a can zan sami farin ciki.
36 Incline mon cœur à tes témoignages, et non point au gain déshonnête.
Ka juye zuciyata wajen farillanka ba wajen riba ta sonkai ba.
37 Détourne mes yeux qu'ils ne regardent à la vanité; fais-moi revivre par le moyen de tes voies.
Ka juye idanuna daga abubuwa marasa amfani; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
38 Ratifie ta parole à ton serviteur, qui est adonné à ta crainte.
Ka cika alkawarinka ga bawanka, saboda a ji tsoronka.
39 Ote mon opprobre, lequel j'ai craint; car tes ordonnances sont bonnes.
Ka kawar da shan kunyar da nake tsoro, gama dokokinka nagari ne.
40 Voici, je suis affectionné à tes commandements; fais-moi revivre par ta justice.
Ina marmarin farillanka ƙwarai! Ka kiyaye raina cikin adalcinka.
41 VAU. Et que tes faveurs viennent sur moi, ô Eternel! [et] ta délivrance aussi, selon ta parole;
Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zo gare ni, ya Ubangiji, cetonka bisa ga alkawarinka;
42 Afin que j'aie de quoi répondre à celui qui me charge d'opprobre: car j'ai mis ma confiance en ta parole.
sa’an nan zan amsa wa masu cin mutuncina, gama na dogara ga maganarka.
43 Et n'arrache point de ma bouche la parole de vérité; car je me suis attendu à tes ordonnances.
Kada ka ƙwace maganarka daga bakina, gama na sa zuciyata a dokokinka.
44 Je garderai continuellement ta Loi, à toujours et à perpétuité.
Kullayaumi zan yi biyayya da dokokinka, har abada abadin.
45 Je marcherai au large, parce que j'ai recherché tes commandements.
Zan yi ta yawo a sake gama na nemi farillanka.
46 Je parlerai de tes témoignages devant les Rois, et je ne rougirai point de honte.
Zan yi maganar farillanka a gaban sarakuna ba kuwa za a kunyata ni ba,
47 Et je prendrai mon plaisir en tes commandements, que j'ai aimés;
gama ina farin ciki da umarnanka saboda ina ƙaunarsu.
48 Même j'étendrai mes mains vers tes commandements, que j'ai aimés; et je m'entretiendrai de tes statuts.
Na ɗaga hannuwana ga umarnanka, waɗanda nake ƙauna, ina kuma tunani a kan ƙa’idodinka.
49 ZAIN. Souviens-toi de la parole donnée à ton serviteur, à laquelle tu as fait que je me suis attendu.
Tuna da maganarka ga bawanka, gama ka ba ni bege.
50 C'[est] ici ma consolation dans mon affliction, que ta parole m'a remis en vie.
Ta’aziyyata cikin wahalata ita ce alkawarinka yana kiyaye raina.
51 Les orgueilleux se sont fort moqués de moi, [mais] je ne me suis point dé tourné de ta Loi.
Masu fariya suna yi mini ba’a ba tare da an hana su ba, amma ban rabu da dokar ba.
52 Eternel, je me suis souvenu des jugements d'ancienneté, et je me suis consolé [en eux].
Na tuna da dokokinka na tun dā, ya Ubangiji, na kuwa sami ta’aziyya a cikinsu.
53 L'horreur m'a saisi, à cause des méchants qui ont abandonné ta Loi.
Fushi ya kama ni saboda mugaye, waɗanda suka keta dokokinka.
54 Tes statuts ont été le sujet de mes cantiques dans la maison où j ai demeuré comme voyageur.
Ƙa’idodinka su ne kan waƙata a duk inda na sauka.
55 Eternel, je me suis souvenu de ton Nom pendant la nuit, et j'ai gardé ta Loi.
Da dare na tuna da sunanka, ya Ubangiji, zan kuwa kiyaye dokarka.
56 Cela m'est arrivé, parce que je gardais tes commandements.
Wannan shi ne na saba yi, ina yin biyayya da farillanka.
57 HETH. Ô Eternel! j'ai conclu que ma portion était de garder tes paroles.
Kai ne rabona, ya Ubangiji; na yi alkawarin in kiyaye maganarka.
58 Je t'ai supplié de tout mon cœur, aie pitié de moi selon ta parole.
Na nemi fuskarka da dukan zuciyata; ka yi mini alheri bisa ga alkawarinka.
59 J'ai fait le compte de mes voies, et j'ai rebroussé chemin vers tes témoignages.
Na lura da hanyoyina na kuma mayar da matakaina ga farillanka.
60 Je me suis hâté, je n'ai point différé à garder tes commandements.
Zan gaggauta ba zan ɓata lokaci ba in yi biyayya da umarnanka.
61 Les troupes des méchants m'ont pillé, [mais] je n'ai point oublié ta Loi.
Ko da yake mugaye sun ɗaura ni da igiyoyi, ba zan manta da dokokinka ba.
62 Je me lève à minuit pour te célébrer à cause des ordonnances de ta justice.
Da tsakar dare nakan tashi in gode maka saboda dokokinka masu adalci.
63 Je m'accompagne de tous ceux qui te craignent, et qui gardent tes commandements.
Ni aboki ne ga duk mai tsoronka, ga duk wanda yake bin farillanka.
64 Eternel, la terre est pleine de tes faveurs; enseigne-moi tes statuts.
Duniya ta cika da ƙaunarka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
65 TETH. Eternel, tu as fait du bien à ton serviteur selon ta parole.
Ka yi wa bawanka alheri bisa ga maganarka, ya Ubangiji.
66 Enseigne-moi d'avoir bon sens et connaissance, car j'ai ajouté foi à tes commandements.
Ka koya mini sani da kuma hukunci mai kyau, gama na gaskata a umarnanka.
67 Avant que je fusse affligé, j'allais à travers champs; mais maintenant j'observe ta parole.
Kafin in sha wahala na kauce, amma yanzu ina biyayya da maganarka.
68 Tu [es] bon et bienfaisant, enseigne-moi tes statuts.
Kai nagari ne, kuma abin da kake yi yana da kyau; ka koya mini ƙa’idodinka.
69 Les orgueilleux ont forgé des faussetés contre moi; [mais] je garderai de tout mon cœur tes commandements.
Ko da yake masu fariya sun shafe ni da ƙarairayi, na kiyaye farillanka da dukan zuciyata.
70 Leur cœur est comme figé de graisse; mais moi, je prends plaisir en ta Loi.
Zukatansu sun yi tauri da kuma marasa tausayi amma ina farin ciki a dokarka.
71 Il m'est bon que j'aie été affligé, afin que j'apprenne tes statuts.
Ya yi kyau da na sha wahala don in koyi ƙa’idodinka.
72 La Loi [que tu as prononcée] de ta bouche, m'[est] plus précieuse que mille [pièces] d'or ou d'argent.
Doka daga bakinka ya fi mini daraja fiye da azurfa da zinariya guda dubu.
73 JOD. Tes mains m'ont fait, et façonné; rends-moi entendu, afin que j'apprenne tes commandements.
Hannuwanka ne suka yi suka kuma siffanta ni; ka ba ni ganewa don in koyi umarnanka.
74 Ceux qui te craignent me verront, et se réjouiront; parce que je me suis attendu à ta parole.
Bari waɗanda suke tsoronka su yi farin ciki sa’ad da suke gan ni, gama na sa zuciyata a maganarka.
75 Je connais, ô Eternel! que tes ordonnances ne sont que justice; et que tu m'as affligé suivant ta fidélité.
Ya Ubangiji na sani, cewa dokokinka masu adalci ne, kuma cikin aminci ka hore ni.
76 Je te prie, que ta miséricorde me console, selon ta parole [adressée] à ton serviteur.
Bari ƙaunarka marar ƙarewa tă yi mini ta’aziyya, bisa ga alkawarinka ga bawanka.
77 Que tes compassions se répandent sur moi, et je vivrai; car ta Loi est tout mon plaisir.
Bari tausayinka yă zo mini don in rayu, gama dokarka ce farin cikina.
78 Que les orgueilleux rougissent de honte, de ce qu ils m'ont renversé sans sujet; [mais] moi, je discourrai de tes commandements.
Bari masu girman kai su sha kunya saboda abubuwa marasa kyau da suke yi mini ba dalili; amma zan yi tunani a kan farillanka.
79 Que ceux qui te craignent, et ceux qui connaissent tes témoignages, reviennent vers moi.
Bari waɗanda suke tsoronka su juya gare ni, waɗanda suka gane da farillanka.
80 Que mon cœur soit intègre dans tes statuts, afin que je ne rougisse point de honte.
Bari zuciyata ta kasance marar abin zargi wajen ƙa’idodinka, don kada in sha kunya.
81 CAPH. Mon âme s'est consumée en attendant ta délivrance; je me suis attendu à ta parole.
Raina ya tafke da marmari don cetonka, amma na sa zuciyata a maganarka.
82 Mes yeux se sont épuisés [en attendant] ta parole, lorsque j'ai dit: quand me consoleras-tu?
Idanuna sun gaji, suna jiran alkawarinka; Na ce, “Yaushe za ka ta’azantar da ni?”
83 Car je suis devenu comme un outre mis à la fumée, [et je] n'ai point oublié tes statuts.
Ko da yake ni kamar salkar ruwan inabi ne a cikin hayaƙi, ban manta da ƙa’idodinka ba.
84 Combien [ont à durer] les jours de ton serviteur? Quand jugeras-tu ceux qui me poursuivent?
Har yaushe bawanka zai yi ta jira? Yaushe za ka hukunta masu tsananta mini?
85 Les orgueilleux m'ont creusé des fosses, ce qui n'est pas selon ta Loi.
Masu girman kai sun haƙa mini rami, sun ƙetare dokarka.
86 Tous tes commandements [ne sont que] fidélité; on me persécute sans cause; aide-moi.
Dukan umarnanka abin dogara ne; ka taimake ni, gama mutane suna tsananta mini ba dalili.
87 On m'a presque réduit à rien, [et] mis par terre: mais je n'ai point abandonné tes commandements.
Sun kusa gama da ni a duniya, amma ban bar bin farillanka ba.
88 Fais-moi revivre selon ta miséricorde, et je garderai le témoignage de ta bouche.
Ka kiyaye raina bisa ga ƙaunarka, zan kuwa yi biyayya da farillan bakinka.
89 LAMED. Ô Eternel! ta parole subsiste à toujours dans les cieux.
Maganarka, ya Ubangiji madawwamiya ce; tana nan daram a cikin sammai.
90 Ta fidélité dure d'âge en âge; tu as établi la terre, et elle demeure ferme.
Amincinka yana cin gaba cikin dukan zamanai; ka kafa duniya ta kuma dawwama.
91 [Ces choses] subsistent aujourd'hui selon tes ordonnances; car toutes choses te servent.
Dokokinka sun dawwama har yă zuwa yau, gama dukan abubuwa suna maka hidima.
92 N'eût été que ta Loi a été tout mon plaisir, j'eusse déjà péri dans mon affliction.
Da ba don dokarka ce farin cikina ba, da na hallaka a cikin azabana.
93 Je n'oublierai jamais tes commandements; car tu m'as fait revivre par eux.
Ba zan taɓa manta da farillanka ba, gama ta wurinsu ne ka kiyaye raina.
94 Je suis à toi, sauve-moi; car j'ai recherché tes commandements.
Ka cece ni, gama ni naka ne; na yi ƙoƙarin neman farillanka.
95 Les méchants m'ont attendu, pour me faire périr; [mais] je me suis rendu attentif à tes témoignages.
Mugaye suna jira su hallaka ni, amma zan yi ta tunani a kan farillanka.
96 J'ai vu un bout dans toutes les choses les plus parfaites; [mais] ton commandement [est] d'une très-grande étendue.
Ga duk cikakke na ga kāsawa; amma umarnanka ba su da iyaka.
97 MEM. Ô combien j'aime ta Loi! c'est ce dont je m'entretiens tout le jour.
Kash, ga yadda nake ƙaunar dokarka! Ina tunani a kanta dukan yini.
98 Tu m'as rendu plus sage par tes commandements, que ne sont mes ennemis; parce que tes commandements sont toujours avec moi.
Umarnanka suna sa in zama mai hikima fiye da abokan gābana, gama kullum suna tare da ni.
99 J'ai surpassé en prudence tous ceux qui m'avaient enseigné, parce que tes témoignages son mon entretien.
Ina da ganewa sosai fiye da dukan malamaina, gama ina tunani a kan farillanka.
100 Je suis devenu plus intelligent que les anciens, parce que j'ai observé tes commandements.
Ina da ganewa fiye da dattawa, gama ina biyayya da farillanka.
101 J'ai gardé mes pieds de toute mauvaise voie, afin que j'observasse ta parole.
Na kiyaye ƙafafuna daga kowace muguwar hanya domin in yi biyayya da maganarka.
102 Je ne me suis point détourné de tes ordonnances, parce que tu me [les] as enseignées.
Ban rabu da dokokinka ba, gama kai da kanka ne ka koya mini.
103 Ô que ta parole a été douce à mon palais! plus douce que le miel à ma bouche.
Ɗanɗanon maganarka akwai zaki, sun ma fi zuma zaki a bakina!
104 Je suis devenu intelligent par tes commandements, c'est pourquoi j'ai haï toute voie de mensonge.
Na sami ganewa daga farillanka; saboda haka ina ƙin kowace hanyar da ba daidai ba.
105 NUN. Ta parole est une lampe à mon pied, et une lumière à mon sentier.
Maganarka fitila ce ga ƙafafuna haske kuma a kan hanyata.
106 J'ai juré, et je le tiendrai, d'observer les ordonnances de ta justice.
Na yi rantsuwa na kuma tabbatar da shi, cewa zan bi dokokinka masu adalci.
107 Eternel, je suis extrêmement affligé, fais-moi revivre selon ta parole.
Na sha wahala sosai; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga maganarka.
108 Eternel, je te prie, aie pour agréables les oblations volontaires de ma bouche, et enseigne-moi tes ordonnances.
Ka karɓi yabon bakina da nake yi da yardar rai, ya Ubangiji, ka kuwa koya mini dokokinka.
109 Ma vie a été continuellement en danger, toutefois je n'ai point oublié ta Loi.
Ko da yake kullum ina riƙe da raina a hannuwana, ba zan manta da dokarka ba.
110 Les méchants m'ont tendu des piéges, toutefois je ne me suis point égaré de tes commandements.
Mugaye sun kafa mini tarko, amma ban kauce daga farillanka ba.
111 J'ai pris pour héritage perpétuel tes témoignages; car ils sont la joie de mon cœur.
Farillanka su ne gādona har abada; su ne farin cikin zuciyata.
112 J'ai incliné mon cœur à accomplir toujours tes statuts jusques au bout.
Zuciyata ta shirya a kan kiyaye ƙa’idodinka har ƙarshe.
113 SAMECH. J'ai eu en haine les pensées diverses, mais j'ai aimé ta Loi.
Na ƙi mutane masu baki biyu, amma ina ƙauna dokarka.
114 Tu es mon asile et mon bouclier, je me suis attendu à ta parole.
Kai ne mafakata da garkuwata; na sa zuciyata a maganarka.
115 Méchants, retirez-vous de moi, et je garderai les commandements de mon Dieu.
Ku rabu da ni, ku masu aikata mugunta, don in kiyaye umarnan Allahna!
116 Soutiens-moi suivant ta parole, et je vivrai; et ne me fais point rougir de honte en me refusant ce que j'espérais.
Ka raya ni bisa ga alkawarinka, zan kuwa rayu; kada ka bari a gwale sa zuciyata.
117 Soutiens-moi, et je serai en sûreté, et j'aurai continuellement les yeux sur tes statuts.
Ka riƙe ni za a kuma cece ni; kullayaumi zan ɗauka ƙa’idodinka da muhimmanci.
118 Tu as foulé aux pieds tous ceux qui se détournent de tes statuts; car le mensonge est le moyen dont ils se servent pour tromper.
Ka ki dukan waɗanda suka kauce daga ƙa’idodinka, gama yaudararsu banza ne.
119 Tu as réduit à néant tous les méchants de la terre, comme n'étant qu'écume; c'est pourquoi j'ai aimé tes témoignages.
Dukan mugayen duniya ka zubar kamar datti; saboda haka nake ƙaunar farillanka.
120 Ma chair a frémi de la frayeur que j'ai de toi, et j'ai craint tes jugements.
Naman jikina na rawan jiki don tsoronka; na cika da tsoron dokokinka.
121 HAJIN. J'ai exercé jugement et justice, ne m'abandonne point à ceux qui me font tort.
Na aikata abin da yake mai adalci da kuma daidai; kada ka ni a hannun masu danne ni.
122 Sois le pleige de ton serviteur pour son bien; [et ne permets pas] que je sois opprimé par les orgueilleux,
Ka tabbatar da lafiyar bawanka; kada ka bar masu girman kai su danne ni.
123 Mes yeux se sont épuisés en attendant ta délivrance, et la parole de ta justice.
Idanuna sun gaji, da jiran cetonka, da jiran alkawarinka mai adalci.
124 Agis envers ton serviteur suivant ta miséricorde et m'enseigne tes statuts.
Ka yi da bawanka bisa ga ƙaunarka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
125 Je suis ton serviteur, rends-moi intelligent, et je connaîtrai tes témoignages.
Ni bawanka ne, ka ba ni fahimi don in gane farillanka.
126 Il est temps que l'Eternel opère; ils ont aboli ta Loi.
Lokaci ya yi da za ka yi wani abu, ya Ubangiji; ana karya dokarka.
127 C'est pourquoi j'ai aimé tes commandements, plus que l'or, même plus que le fin or.
Saboda ina ƙaunar umarnanka fiye da zinariya, kai, fiye da zinariya zalla,
128 C'est pourquoi j'ai estimé droits tous les commandements que tu donnes de toutes choses, [et] j'ai eu en haine toute voie de mensonge.
saboda kuma ina lura da dukan farillanka da kyau, na ƙi kowace hanyar da ba daidai ba.
129 PE. Tes témoignages sont des choses merveilleuses; c'est pourquoi mon âme les a gardés.
Farillanka masu banmamaki ne; saboda haka nake yin biyayya da su.
130 L'entrée de tes paroles illumine, [et] donne de l'intelligence aux simples.
Fassarar maganganunka sukan ba da haske; sukan ba da ganewa ga marar ilimi.
131 J'ai ouvert ma bouche, et j'ai soupiré; car j'ai souhaité tes commandements.
Ina hakkin da bakina a buɗe, ina marmarin umarnanka.
132 Regarde-moi, et aie pitié de moi, selon que tu as ordinairement compassion de ceux qui aiment ton Nom.
Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, yadda kullum ka yi wa waɗanda suke ƙaunar sunanka.
133 Affermis mes pas sur ta parole, et que l'iniquité n'ait point d'empire sur moi.
Ka bi da sawuna bisa ga maganarka; kada ka bar zunubi yă mallake ni.
134 Délivre-moi de l'oppression des hommes, afin que je garde tes commandements.
Ka fanshe ni daga mutane masu danniya, don in yi biyayya da farillanka.
135 Fais luire ta face sur ton serviteur, et m'enseigne tes statuts.
Ka sa fuskarka ta haskaka a kan bawanka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
136 Mes yeux se sont fondus en ruisseaux d'eau, parce qu'on n'observe point ta Loi.
Hawaye suna malalowa daga idanuna kamar rafi, gama ba a biyayya da dokarka.
137 TSADE. Tu es juste, ô Eternel! et droit en tes jugements.
Mai adalci ne kai, ya Ubangiji, dokokinka kuma daidai ne.
138 Tu as ordonné tes témoignages comme une chose juste, et souverainement ferme.
Farillan da ka shimfiɗa masu adalci ne; su kuma abin dogara ne ƙwarai.
139 Mon zèle m'a miné; parce que mes adversaires ont oublié tes paroles.
Kishina ya cinye ni ɗungum, gama abokan gābana sun yi biris da maganganunka.
140 Ta parole est souverainement raffinée, c'est pourquoi ton serviteur l'aime.
An gwada alkawuranka sarai, bawanka kuwa yana ƙaunarsu.
141 Je suis petit et méprisé, [toutefois] je n'oublie point tes commandements.
Ko da yake ni ba kome ba ne an kuwa rena ni, ba na manta da farillanka.
142 Ta justice est une justice à toujours, et ta Loi est la vérité.
Adalcinka dawwammame ne dokar kuma gaskiya ce.
143 La détresse et l'angoisse m'avaient rencontré; [mais] tes commandements sont mes plaisirs.
Wahala da damuwa suna a kaina, amma umarnanka su ne farin cikina.
144 Tes témoignages ne sont que justice à toujours; donne m'en l’intelligence, afin que je vive.
Farillanka daidai ne har abada; ka ba ni ganewa don in rayu.
145 KOPH. J'ai crié de tout mon cœur, réponds-moi, ô Eternel! [et] je garderai tes statuts.
Na yi kira da dukan zuciyata; ka amsa mini, ya Ubangiji, zan kuwa yi biyayya da ƙa’idodinka.
146 J'ai crié vers toi; sauve-moi, afin que j'observe tes témoignages.
Na yi kira gare ka; ka cece ni zan kuwa kiyaye farillanka.
147 J'ai prévenu le point du jour, et j'ai crié; je me suis attendu à ta parole.
Na tashi kafin fitowar rana na kuma yi kukan neman taimako; na sa zuciyata a maganarka.
148 Mes yeux ont prévenu les veilles de la nuit pour méditer la parole.
Ban rufe idanuna ba dukan dare, don in yi tunani a kan alkawuranka.
149 Ecoute ma voix selon ta miséricorde: ô Eternel! fais-moi revivre selon ton ordonnance.
Ka ji muryata bisa ga ƙaunarka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga dokokinka.
150 Ceux qui sont adonnés à des machinations se sont approchés de moi, [et] ils se sont éloignés de ta Loi.
Waɗanda suke ƙirƙiro mugayen dabaru suna nan kusa, amma suna nesa da dokarka.
151 Eternel, tu es aussi près de moi; et tous tes commandements ne sont que vérité.
Duk da haka kana kusa, ya Ubangiji, kuma dukan umarnanka gaskiya ne.
152 J'ai connu dès longtemps touchant tes témoignages, que tu les as fondés pour toujours.
Tun tuni na koyi daga farillanka cewa ka kafa su su kasance har abada.
153 RESCH. Regarde mon affliction, et m'en retire; car je n'ai point oublié ta Loi.
Ka dubi wahalata ka cece ni, gama ban manta da dokarka ba.
154 Soutiens ma cause, et me rachète; fais-moi revivre suivant ta parole.
Ka kāre manufata ka kuma fanshe ni, ka cece rai na kamar yadda ka alkawarta!
155 La délivrance est loin des méchants; parce qu'ils n'ont point recherché tes statuts.
Ceto yana nesa da mugaye, gama ba sa neman ƙa’idodinka.
156 Tes compassions sont en grand nombre, ô Eternel! fais-moi revivre selon tes ordonnances.
Tausayinka da girma yake, ya Ubangiji; ka kiyaye raina bisa ga dokokinka.
157 Ceux qui me persécutent et qui me pressent, [sont] en grand nombre: [toutefois] je ne me suis point détourné de tes témoignages.
Maƙiya masu yawa ne suke tsananta mini, amma ban rabu da farillanka ba.
158 J'ai jeté les yeux sur les perfides et j'ai été rempli de tristesse de ce qu'ils n'observaient point ta parole.
Na dubi marasa aminci da ƙyama, gama ba sa yin biyayya da maganarka.
159 Regarde combien j'ai aimé tes commandements; Eternel! fais-moi revivre selon ta miséricorde.
Dubi yadda nake ƙaunar farillanka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga ƙaunarka.
160 Le principal point de ta parole est la vérité, et toute l'ordonnance de ta justice est à toujours.
Dukan maganganunka gaskiya ne; dukan dokokinka masu adalci madawwami ne.
161 SCIN. Les principaux du peuple m'ont persécuté sans sujet; mais mon cœur a été effrayé à cause de ta parole.
Masu mulki suna tsananta mini ba dalili, amma zuciyata na rawan jiki game da maganarka.
162 Je me réjouis de ta parole, comme ferait celui qui aurait trouvé un grand butin.
Ina farin ciki da alkawarinka kamar yadda wani kan sami ganima mai girma.
163 J'ai eu en haine et en abomination le mensonge; j'ai aimé ta Loi.
Na ƙi ina kuma ƙyamar ƙarya amma ina ƙaunar dokarka.
164 Sept fois le jour je te loue à cause des ordonnances de ta justice.
Sau bakwai a rana ina yabonka saboda dokokinka masu adalci.
165 Il y a une grande paix pour ceux qui aiment ta Loi, et rien ne peut les renverser.
Waɗanda suke ƙaunar dokarka suna da babban salama, kuma babu abin da zai sa su yi tuntuɓe.
166 Eternel, j'ai espéré en ta délivrance, et j'ai fait tes commandements.
Ina jiran cetonka, ya Ubangiji, ina kuma bin umarnanka.
167 Mon âme a observé tes témoignages, et je les ai souverainement aimés.
Ina biyayya da farillanka, gama ina ƙaunarsu ƙwarai.
168 J'ai observé tes commandements et tes témoignages; car toutes mes voies sont devant toi.
Ina biyayya da farillanka da kuma koyarwarka, gama dukan hanyoyina sanannu ne gare ka.
169 THAU. Eternel, que mon cri approche de ta présence; rends-moi intelligent selon ta parole.
Bari kukata ta zo gare ka, ya Ubangiji; ka ba ni ganewa bisa ga maganarka.
170 Que ma supplication vienne devant toi; délivre-moi selon ta parole.
Bari roƙona yă zo gabanka; ka cece ni bisa ga alkawarinka.
171 Mes lèvres publieront ta louange, quand tu m'auras enseigné tes statuts.
Bari leɓunana su cika da yabonka, gama ka koya mini ƙa’idodinka.
172 Ma langue ne s'entretiendra que de ta parole; parce que tous tes commandements ne sont que justice.
Bari harshena yă rera game da maganarka, gama dukan umarnanka masu adalci ne.
173 Que ta main me soit en aide, parce que j'ai choisi tes commandements.
Bari hannunka yă kasance a shirye don yă taimake ni, gama na zaɓi farillanka.
174 Eternel, j'ai souhaité ta délivrance, et ta Loi est tout mon plaisir.
Ina marmarin cetonka, ya Ubangiji, dokarka kuwa ita ce farin cikina.
175 Que mon âme vive, afin qu'elle te loue; et fais que tes ordonnances me soient en aide.
Bari in rayu don in yabe ka, bari kuma dokokinka su raya ni.
176 J'ai été égaré comme la brebis perdue; cherche ton serviteur; car je n'ai point mis en oubli tes commandements.
Na kauce kamar ɓatacciyar tunkiya. Ka nemi bawanka, gama ban manta da umarnanka ba.

< Psaumes 119 >