< Psaumes 24 >

1 Psaume de David. La terre appartient à l'Eternel, avec tout ce qui est en elle, la terre habitable, et ceux qui y habitent.
Zabura ta Dawuda. Duniya ta Ubangiji ce da kome da yake cikinta, duniya, da dukan waɗanda suke zama a cikinta;
2 Car il l'a fondée sur les mers, et l'a posée sur les fleuves.
gama ya gina ta a kan tekuna ya kafa ta a kan ruwaye.
3 Qui est-ce qui montera en la montagne de l'Eternel? et qui est-ce qui demeurera dans le lieu de sa sainteté?
Wa zai iya hawan tudun Ubangiji? Wa zai iya tsaya a wurinsa mai tsarki?
4 Ce sera l'homme qui a les mains pures et le cœur net, qui n'aspire point de son âme à la fausseté, et qui ne jure point en tromperie.
Sai wanda yake da hannu mai tsabta da kuma tsabtar zuciya, wanda ba ya ba da ransa ga bautar gunki ko ya rantse bisa abin da yake ƙarya.
5 Il recevra bénédiction de l'Eternel, et justice de Dieu son Sauveur.
Zai sami albarka daga Ubangiji da fiffitawa daga Allah Mai cetonsa.
6 Tels sont ceux qui l'invoquent, ceux qui cherchent ta face en Jacob: (Sélah)
Irin tsaran waɗanda suke nemansa ke nan, waɗanda suke neman fuskarka, ya Allah na Yaƙub. (Sela)
7 Portes, élevez vos linteaux, et vous portes éternelles, haussez-vous, et le Roi de gloire entrera.
Ku ɗaga kawunanku, ya ku ƙofofi; ku ɗagu, ku daɗaɗɗun ƙofofi, don Sarkin ɗaukaka yă shiga.
8 Qui est ce Roi de gloire? C'est l'Eternel fort et puissant, l'Eternel puissant en bataille.
Wane ne wannan Sarkin ɗaukaka? Ubangiji ne mai ƙarfi mai iko, Ubangiji mai girma a yaƙi.
9 Portes, élevez vos linteaux, élevez-les aussi, vous portes éternelles, et le Roi de gloire entrera.
Ku ɗaga kawunanku, ya ku ƙofofi; ku ɗagu, ku daɗaɗɗun ƙofofi, don Sarkin ɗaukaka yă shiga.
10 Qui est ce Roi de gloire? L'Eternel des armées; c'est lui qui est le Roi de gloire: (Sélah)
Wane ne shi, wannan Sarkin ɗaukaka? Ubangiji Maɗaukaki, shi ne Sarkin ɗaukaka. (Sela)

< Psaumes 24 >