< Psaumes 41 >

1 Psaume de David, [donné] au maître chantre. Ô que bienheureux est celui qui se conduit sagement envers l'affligé! l'Eternel le délivrera au jour de la calamité.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Mai albarka ne wanda yake jin tausayin marasa ƙarfi; Ubangiji yakan kuɓutar da shi a lokutan wahala.
2 L'Eternel le gardera et le préservera en vie; il sera même rendu heureux en la terre; ne le livre donc point au gré de ses ennemis.
Ubangiji zai kāre shi yă kuma kiyaye ransa; zai albarkace shi a cikin ƙasar ba kuwa zai miƙa shi ga hannun maƙiyansa ba.
3 L'Eternel le soutiendra [quand il sera] dans un lit de langueur; tu transformeras tout son lit, [quand il sera] malade.
Ubangiji zai ba shi ƙarfi a gadon rashin lafiyarsa ya mayar masa da lafiya daga ciwon da ya kwantar da shi.
4 J'ai dit: Eternel! aie pitié de moi, guéris mon âme; quoique j'aie péché contre toi.
Na ce, “Ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai; ka warkar da ni, gama na yi maka zunubi.”
5 Mes ennemis [me souhaitant] du mal, disent: Quand mourra-t-il? et quand périra son nom?
Abokan gābana suna muguwar magana a kaina cewa, “Yaushe zai mutu sunansa yă ɓace ne?”
6 Et si quelqu'un d'eux vient me visiter, il parle en mensonge; son cœur s'amasse de quoi me fâcher. Est-il sorti? il en parle dehors.
Duk sa’ad da wani ya zo ganina, yakan yi maganar ƙarya, yayinda zuciyarsa tana tattare da cin zarafi; sa’an nan yă fita yă yi ta bazawa ko’ina.
7 Tous ceux qui m'ont en haine murmurent sourdement ensemble contre moi, [et] machinent du mal contre moi.
Dukan abokan gābana suna raɗa tare a kaina; suna fata mugun abu ya same ni, suna cewa,
8 Quelque action, [disent-ils, telle que] les méchants [commettent], le tient enserré, et cet homme qui est couché, ne se relèvera plus.
“Mugun ciwo ya kama shi; ba zai taɓa tashi daga inda yake kwanciya ba.”
9 Même celui qui avait la paix avec moi, sur lequel je m'assurais, [et] qui mangeait mon pain, a levé le talon contre moi.
Har abokina na kurkusa, wanda na amince da shi, wanda muke cin abinci tare, ya juya yana gāba da ni.
10 Mais toi, ô Eternel! aie pitié de moi, et me relève; et je le leur rendrai.
Amma kai, ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai, ka tā da ni, don in sāka musu.
11 En ceci je connais que tu prends plaisir en moi, que mon ennemi ne triomphe point de moi.
Na sani kana jin daɗina, gama abokin gābana ba zai ci nasara a kaina ba.
12 Pour moi, tu m'as maintenu dans mon entier, et tu m'as établi devant toi pour toujours.
Cikin mutuncina ka riƙe ni ka sa ni a gabanka har abada.
13 Béni soit l'Eternel, le Dieu d'Israël, de siècle en siècle. Amen! Amen!
Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, har abada abadin.

< Psaumes 41 >