< Zacharie 13 >

1 En ce temps-là il y aura une source ouverte en faveur de la maison de David, et des habitants de Jérusalem, pour le péché, et pour la souillure.
“A ranan nan za a buɗe maɓulɓulan ruwa zuwa gidan Dawuda da mazaunan Urushalima, don a tsarkake su daga zunubi da rashin tsabta.
2 Il arrivera aussi en ce temps-là, dit l'Eternel des armées, que je retrancherai du pays les noms des faux dieux; et on n'en fera plus mention; j'ôterai aussi du pays les [faux] prophètes, et l'esprit d'impureté.
“A ranan nan, zan kawar da sunayen gumaka daga ƙasar, ba kuwa za a ƙara tunawa da su ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan kawar da annabawa da kuma ruhu marar tsabta daga ƙasar.
3 Et il arrivera que quand quelqu'un prophétisera dorénavant, son père et sa mère qui l'auront engendré, lui diront: Tu ne vivras plus; car tu as prononcé des mensonges au Nom de l'Eternel; et son père et sa mère qui l'auront engendré, le transperceront quand il prophétisera.
In kuma wani ya yi annabci, sai mahaifinsa da mahaifiyarsa su ce masa, ‘Ba za ka rayu ba, gama kana faɗar ƙarya da sunan Ubangiji.’ Sa’ad da yake yin annabci, iyayensa za su soke shi da takobi.
4 Et il arrivera en ce temps-là que ces prophètes seront confus chacun de sa vision, quand il aura prophétisé; et ils ne seront plus vêtus de manteau de poil, pour mentir.
“A ranan nan kowane annabi zai ji kunyar annabcin wahayinsa. Ba zai sa rigar annabci mai gashi ba don yă yi ruɗu.
5 Et il dira: Je ne suis point prophète, [mais] je suis un laboureur; car on m'a appris à gouverner du bétail dès ma jeunesse.
Zai ce, ‘Ni ba annabi ba ne. Ni manomi ne; ƙasa ce nake samun abin zaman gari tun ina matashi.’
6 Et on lui dira: Que veulent donc dire ces blessures en tes mains? Et il répondra: Ce sont celles qui m'ont été faites dans la maison de mes amis.
In wani ya tambaye shi, ‘Waɗanne miyaku ne haka a jikinka?’ Zai amsa yă ce, ‘Miyakun da aka yi mini a gidan abokaina ne.’
7 Epée, réveille-toi sur mon Pasteur, et sur l'homme qui est mon compagnon, dit l'Eternel des armées; frappe le Pasteur, et les brebis seront dispersées, et je tournerai ma main sur les petits.
“Tashi, ya takobi, gāba da makiyayina, mutumin da yake kusa da ni sosai!” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Kashe makiyayin, sai tumakin su watse, in kuma tayar wa ƙananan.
8 Et il arrivera dans toute la terre, dit l'Eternel, que deux parties seront retranchées en elle, et défaudront, mais la troisième y demeurera de reste.
A cikin ƙasar duka,” in ji Ubangiji, “kashi biyu bisa uku za a buge su su hallaka; duk da haka za a bar kashi ɗaya bisa uku a cikinta.
9 Et j'amènerai la troisième partie au feu, je les affinerai comme on affine l'argent, et je les éprouverai comme on éprouve l'or, chacun d'eux invoquera mon Nom, et je l'exaucerai; je dirai: C'est [ici] mon peuple; et il dira: L'Eternel est mon Dieu.
Wannan kashi ɗaya bisa ukun zan kawo in sa a cikin wuta; zan tace su kamar azurfa in gwada su kamar zinariya. Za su kira bisa sunana zan kuwa amsa musu; zan ce, ‘Su mutanena ne,’ za su kuma ce, ‘Ubangiji ne Allahnmu.’”

< Zacharie 13 >