< Sophonie 1 >

1 [C'est ici] la parole de l'Eternel qui fut [adressée] à Sophonie fils de Cusi, fils de Guédalia, fils d'Amaria, fils d'Ezéchias, du temps de Josias fils d'Amon Roi de Juda.
Domin mai bi da kaɗe-kaɗe. A kan kayan kiɗi masu tsirkiyata. Maganar Ubangiji da ta zo wa Zefaniya ɗan Kushi, ɗan Gedaliya, ɗan Amariya, ɗan Hezekiya, a zamanin Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda.
2 Je ferai entièrement périr toutes choses de dessus cette terre, dit l'Eternel.
“Zan hallaka kome a fuskar duniya,” in ji Ubangiji.
3 Je ferai périr l'homme et le bétail; je consumerai les oiseaux des cieux, et les poissons de la mer; et les ruines [arriveront] aux méchants, et je retrancherai les hommes de dessus cette terre, dit l'Eternel.
“Zan hallaka mutane da dabbobi; zan kuma hallaka tsuntsayen sama da kifayen teku, da gumakan da suke sa mugaye su yi tuntuɓe.” “Sa’ad da zan kawar da mutum daga fuskar duniya,” in ji Ubangiji.
4 J'étendrai ma main sur Juda, et sur tous les habitants de Jérusalem; je retrancherai de ce lieu-ci le reste des Bahalins, et les noms des prêtres des faux dieux, et les sacrificateurs;
“Zan miƙa hannuna gāba da Yahuda da kuma dukan mazaunan Urushalima. Zan datse raguwar Ba’al daga wannan wuri, da sunayen firistocin gumaka da na marasa sanin Allah,
5 Et ceux qui se prosternent sur les toits devant l'armée des cieux, et ceux qui se prosternent devant l'Eternel, jurent par lui, et qui jurent aussi par Malcam:
waɗanda suka rusuna a kan rufin ɗaki don su yi sujada ga rundunar taurari. Waɗanda suka rusuna suka kuma yi rantsuwa da sunan Ubangiji suke kuma rantsuwa da sunan Molek.
6 Et ceux qui se détournent de l'Eternel, et ceux qui n'ont point cherché l'Eternel, qui ne l'ont point recherché.
Waɗanda suka juya daga bin Ubangiji, ba sa kuma neman Ubangiji ko su nemi nufinsa.”
7 Tais-toi, à cause de la présence du Seigneur l'Eternel, car la journée de l'Eternel est proche; l'Eternel a préparé le sacrifice, il a invité ses conviés.
Ku yi shiru a gaban Ubangiji Mai Iko Duka, gama ranar Ubangiji ta yi kusa. Ubangiji ya shirya hadaya; ya kuma tsarkake waɗanda ya gayyato.
8 Et il arrivera au jour du sacrifice de l'Eternel que je punirai les Seigneurs, et les enfants du Roi, et tous ceux qui s'habillent de vêtements étrangers.
“A ranar hadayar Ubangiji zan hukunta sarakuna da kuma’ya’yan sarakuna da duk waɗanda suke sanye da rigunan ƙasashen waje.
9 Et je punirai en ce jour-là tous ceux qui sautent par-dessus le seuil, [et] ceux qui remplissent de violence et de fraude la maison de leurs maîtres.
A wannan rana zan hukunta dukan waɗanda suke kauce taka madogarar ƙofa, waɗanda suke cika haikalin allolinsu da rikici da ruɗu.
10 Et en ce jour-là dit l'Eternel, il y aura de grands cris vers la porte des poissons, et des hurlements vers la seconde [ville], et une grande désolation vers les coteaux.
“A wannan rana,” in ji Ubangiji, “Za a ji kuka daga Ƙofar Kifi, kururuwa daga Sabon Mazauni, da kuma amo mai ƙarfi daga tuddai.
11 Vous qui habitez dans Mactès, hurlez; car tous ceux qui trafiquaient ont été défaits, et tous ceux qui apportaient de l'argent, ont été retranchés.
Ku yi kururuwa, ku da kuke zaune a yankin kasuwa; za a hallaka dukan’yan kasuwanku, dukan waɗanda suke kasuwanci da azurfa za su lalace.
12 Et il arrivera en ce temps-là, que je fouillerai Jérusalem avec des lampes, que je punirai les hommes qui sont figés sur leurs lies, et qui disent en leurs cœurs; L'Eternel ne [nous] fera ni bien ni mal.
A wannan lokaci zan bincike Urushalima da fitilu in kuma hukunta waɗanda ba su kula ba, waɗanda suke kamar ruwan inabin da aka bar a ƙasan tukunya, waɗanda suke tsammani, ‘Ubangiji ba zai yi kome ba nagari ko mummuna.’
13 Et leurs biens seront au pillage, et leurs maisons en désolation, et ils auront bâti des maisons, mais ils n'y habiteront point; et ils auront planté des vignes, mais ils n'en boiront pas le vin.
Za a washe dukiyarsu, a rurrushe gidajensu. Za su gina gidaje amma ba za su zauna a ciki ba; za su shuka inabi amma ba za su sha ruwansa ba.”
14 La grande journée de l'Eternel est proche, elle est proche, et elle se hâte fort; la journée de l'Eternel n'est que bruit; celui qui est en amertume, crie de toute sa force; Là sont les hommes forts.
Babbar ranar Ubangiji ta yi kusa, ta yi kusa kuma tana zuwa da sauri. Ku saurara! Kukan ranar Ubangiji za tă yi zafi, za a ji kururuwan jarumi a can.
15 Cette journée-là est une journée de fureur, une journée de détresse et d'angoisse, une journée de bruit éclatant et effrayant, une journée de ténèbres et d'obscurité, une journée de nuées et de brouillards;
Ranan nan za tă zama ranar fushi, rana ce ta baƙin ciki da azaba, rana ce ta tashin hankali da lalacewa, ranar duhu baƙi ƙirin, ranar gizagizai da baƙin duhu,
16 Une journée de cornet et d'alarme contre les villes munies, et contre les hautes tours.
rana ce ta busa ƙaho da kururuwar yaƙi gāba da birane masu mafaka, da kuma kusurwar hasumiyoyi.
17 Je mettrai les hommes dans la détresse, et ils marcheront comme des aveugles, parce qu'ils ont péché contre l'Eternel; et leur sang sera répandu comme de la poussière, et leur chair comme de la fiente.
“Zan kawo baƙin ciki a kan mutane za su kuma yi tafiya kamar makafi, domin sun yi wa Ubangiji zunubi. Za a zubar da jininsu kamar ƙura kayan cikinsu kuma kamar najasa.
18 Ni leur argent ni leur or ne les pourront point délivrer en la journée de la fureur de l'Eternel; et tout ce pays sera dévoré par le feu de sa jalousie; car il se hâtera de consumer tous les habitants de ce pays.
Azurfarsu ko zinariyarsu ba za su iya cetonsu ba a ranar fushin Ubangiji.” A cikin zafin kishinsa za a hallaka dukan duniya gama zai kawo ƙarshen dukan mazaunan duniya nan da nan.

< Sophonie 1 >