< 2 Samuel 3 >

1 Or il y eut une longue guerre entre la maison de Saül et la maison de David; mais David allait se fortifiant, et la maison de Saül allait s'affaiblissant.
Aka daɗe ana yaƙi tsakanin gidan Shawulu da gidan Dawuda. Dawuda kuwa ya yi ta ƙara ƙarfi, yayinda gidan Shawulu ya yi ta raguwa a ƙarfi.
2 Et il naquit des fils à David, à Hébron; son premier-né fut Amnon, d'Achinoam de Jizréel;
An haifa wa Dawuda’ya’ya maza a Hebron. Ɗansa na fari shi ne Amnon, ɗan Ahinowam mutuniyar Yezireyel;
3 Le second fut Kiléab, d'Abigaïl, de Carmel, qui avait été femme de Nabal; le troisième, Absalom, fils de Maaca, fille de Thalmaï, roi de Gueshur;
na biyu shi ne Kileyab, ɗan Abigiyel gwauruwar Nabal mutumin Karmel; na uku shi ne Absalom, ɗan Ma’aka’yar Talmai sarkin Geshur;
4 Le quatrième, Adonija, fils de Hagguith; le cinquième, Shéphatia, fils d'Abital;
na huɗu shi ne Adoniya, ɗan Haggit; na biyar shi ne Shefatiya, ɗan Abital;
5 Et le sixième, Jithréam, d'Égla, femme de David. Ceux-là naquirent à David, à Hébron.
na shida kuma shi ne Itireyam, ɗan Egla matar Dawuda. An haifi waɗannan wa Dawuda a Hebron.
6 Or, pendant qu'il y eut guerre entre la maison de Saül et la maison de David, Abner soutenait la maison de Saül.
Sa’ad da ake yaƙi tsakanin gidan Shawulu da gidan Dawuda, sai Abner ya yi ta ƙarfafa matsayinsa a gidan Shawulu.
7 Et Saül avait eu une concubine qui s'appelait Ritspa, fille d'Ajja; et Ishbosheth dit à Abner: Pourquoi es-tu venu vers la concubine de mon père?
To, Shawulu yana da ƙwarƙwarar da ake kira Rizfa,’yar Aiya. Sai Ish-Boshet ya ce wa Abner, “Don me kake kwana da ƙwarƙwarar mahaifina?”
8 Et Abner fut fort irrité des paroles d'Ishbosheth, et lui dit: Suis-je une tête de chien, moi qui, contre Juda, use aujourd'hui de bonté envers la maison de Saül, ton père, et envers ses frères et ses amis, et qui ne t'ai point livré entre les mains de David, que tu me recherches aujourd'hui pour le péché d'une femme?
Abner ya husata saboda abin da Ish-Boshet ya ce, sai ya ce, “Kana tsammani ni mai cin amana ne? Kana zato ni mai goyon bayan Yahuda ne? Tun farko na nuna aminci ga gidan babanka Shawulu, da’yan’uwansa, da abokansa! Ban kuwa ba da kai a hannun Dawuda ba. Ga shi yanzu a kan mace za ka ga laifina?
9 Que Dieu punisse sévèrement Abner, si je ne fais à David tout ce que l'Éternel lui a juré,
Allah yă yi wa Abner hukunci mai tsanani, in ban goyi bayan Dawuda ya sami abin da Ubangiji ya yi masa alkawari da rantsuwa ba.
10 En transportant la royauté de la maison de Saül dans la sienne, et en établissant le trône de David sur Israël et sur Juda, depuis Dan jusqu'à Béer-Shéba.
Zan kuma mayar wa Dawuda sarautar gidan Shawulu, in kafa kursiyin Dawuda a kan Isra’ila, da kan Yahuda tun daga Dan har zuwa Beyersheba.”
11 Et Ishbosheth n'osa répondre un mot à Abner, parce qu'il le craignait.
Ish-Boshet bai ƙara yin karambanin ce wa Abner kome ba, gama yana tsoronsa.
12 Abner envoya donc des messagers à David, pour dire de sa part: A qui appartient le pays? en ajoutant: Traite alliance avec moi; et voici, ma main sera avec toi, pour réunir à toi tout Israël.
Sai Abner ya aiki manzanni a madadinsa wurin Dawuda su ce masa, “Ƙasar ta wane ne? Ka yi yarjejjeniya da ni, zan kuwa taimake ka, in juye dukan Isra’ila zuwa ɓangarenka.”
13 Et David répondit: C'est bien; je traiterai alliance avec toi; je te demande seulement une chose; c'est que tu ne voies point ma face, que tu ne m'aies d'abord ramené Mical, fille de Saül, quand tu viendras me voir.
Dawuda ya ce, “Da kyau, zan yi yarjejjeniya da kai, amma fa ina bukata abu guda daga gare ka, kada ka zo gabana in ba tare da matata Mikal,’yar Shawulu ba.”
14 Alors David envoya des messagers à Ishbosheth, fils de Saül, pour lui dire: Rends-moi ma femme Mical, que j'ai épousée pour cent prépuces de Philistins.
Sai Dawuda ya aiki manzanni zuwa wurin Ish-Boshet ɗan Shawulu cewa, “Ka ba ni matata Mikal wadda na biya sadakinta da loɓa ɗari na Filistiyawa.”
15 Et Ishbosheth l'envoya prendre à son mari Paltiel, fils de Laïsh.
Sai Ish-Boshet ya ba da umarni, aka kuwa ɗauke ta daga gidan mijinta Faltiyel ɗan Layish.
16 Et son mari s'en alla avec elle, pleurant en la suivant jusqu'à Bachurim. Puis Abner lui dit: Va, retourne-t'en! Et il s'en retourna.
Amma mijin ya raka ta, yana tafe yana kuka, ya bi ta har Bahurim. Sai Abner ya ce masa, “Koma gida!” Sai ya koma.
17 Or Abner parla aux anciens d'Israël et dit: Vous désiriez autrefois d'avoir David pour votre roi.
Abner ya tattauna da dattawan Isra’ila ya ce, “An daɗe kuna nema ku naɗa Dawuda sarkinku.
18 Maintenant donc, faites-le; car l'Éternel a parlé à David et a dit: C'est par David, mon serviteur, que je délivrerai mon peuple d'Israël de la main des Philistins et de la main de tous ses ennemis.
To, yanzu sai ku yi haka! Gama Ubangiji ya yi wa Dawuda alkawari ya ce, ‘Ta wurin bawana Dawuda zan ceci mutanena Isra’ila daga hannun Filistiyawa, da kuma hannun dukan abokan gābansu.’”
19 Et Abner parla de même à ceux de Benjamin; puis il alla dire à David, à Hébron, ce qui avait été approuvé par Israël et par toute la maison de Benjamin.
Abner kuma ya yi magana da mutane Benyamin da kansa. Sa’an nan ya tafi Hebron yă gaya wa Dawuda ko mene ne Isra’ila da kuma dukan gidan Benyamin suke so su yi.
20 Abner vint donc vers David à Hébron, et vingt hommes avec lui; et David fit un festin à Abner et aux hommes qui étaient avec lui.
Sa’ad da Abner wanda yake tare da mutane ashirin suka zo wurin Dawuda a Hebron, Dawuda ya shirya masa liyafa tare da mutanensa.
21 Puis Abner dit à David: Je me lèverai, et je m'en irai rassembler tout Israël auprès du roi, mon seigneur, pour qu'ils traitent alliance avec toi, et tu régneras comme ton âme le souhaite. Et David renvoya Abner qui s'en alla en paix.
Sai Abner ya ce wa Dawuda, “Bari in tafi nan da nan in tattara dukan Isra’ila wa ranka yă daɗe, sarki, saboda su yi alkawari da kai, ka kuma ka yi mulki bisa dukansu yadda ranka yake so.” Saboda haka Dawuda ya sallami Abner, ya kuwa tafi lafiya.
22 Et voici, les gens de David revenaient avec Joab de faire une incursion, et amenaient avec eux un grand butin. Or Abner n'était plus avec David à Hébron; car il l'avait renvoyé, et il s'en était allé en paix.
Ba a jima ba sai mutanen Dawuda da Yowab suka dawo daga hari. Suka kawo ganima da yawa tare da su. Abner kuwa ya riga ya bar Dawuda a Hebron, domin Dawuda ya sallame shi, shi kuma ya tafi lafiya.
23 Joab, et toute l'armée qui était avec lui, revint donc; et on fit rapport à Joab en ces mots: Abner, fils de Ner, est venu vers le roi, qui l'a laissé partir, et il s'en est allé en paix.
Sa’ad da Yowab da dukan sojoji suka dawo, aka gaya masa cewa Abner ɗan Ner ya zo wurin sarki, sarki kuwa ya sallame shi, ya kuma tafi lafiya.
24 Et Joab vint vers le roi, et dit: Qu'as-tu fait? Voici, Abner est venu vers toi; pourquoi l'as-tu renvoyé, et s'en est-il allé ainsi?
Sai Yowab ya je wurin sarki ya ce, “Me ke nan ka yi? Abner ya zo wurinka. Don me ka ƙyale shi yă tafi? Ga shi kuwa ya tafi!
25 Tu connais Abner, fils de Ner; c'est pour te tromper qu'il est venu, pour reconnaître tes démarches, et pour savoir tout ce que tu fais.
Ka san Abner ɗan Ner ya zo ne yă ruɗe ka, yă ga fitarka da shigarka, yă kuma binciki kome da kake yi.”
26 Puis Joab, ayant quitté David, envoya après Abner des gens qui le ramenèrent de la fosse de Sira, sans que David le sût.
Yowab ya tashi daga gaban Dawuda ya tafi ya aika manzanni su bi Abner. Suka same shi a rijiyar Sira suka komo da shi, Dawuda kuwa bai sani ba.
27 Abner étant donc revenu à Hébron, Joab le tira à part, en dedans de la porte, comme pour lui parler en secret, et là il le frappa au ventre; et Abner mourut ainsi, à cause du sang d'Asaël, frère de Joab.
To, da Abner ya komo Hebron, Yowab ya ratse da shi zuwa hanyar shigar gari kamar zai gana da shi a kaɗaice. Amma a can ya soki Abner a ciki, ya kashe shi don yă rama mutuwar ɗan’uwansa Asahel.
28 Et David l'apprit ensuite, et dit: Je suis innocent, moi et mon royaume, devant l'Éternel, à jamais, du sang d'Abner, fils de Ner.
Daga baya, Dawuda ya ji labarin sai ya ce, “Ni da masarautata har abada ba mu da laifi a gaban Ubangiji game da jinin Abner ɗan Ner.
29 Que ce sang retombe sur la tête de Joab, et sur toute la maison de son père! Et que la maison de Joab ne soit jamais sans quelque homme ayant un flux, ou la lèpre, ou qui s'appuie sur un bâton, ou qui tombe par l'épée, ou qui manque de pain!
Alhakin jininsa yă kasance a kan Yowab da kuma a kan dukan iyalin mahaifinsa! Kada gidan Yowab yă rasa mai ɗiga, ko kuturu, ko mai jingina ga sanda, ko wanda aka kashe da takobi, ko kuma wanda ba shi da abinci.”
30 Ainsi Joab et Abishaï, son frère, tuèrent Abner, parce qu'il avait tué Asaël, leur frère, près de Gabaon, dans le combat.
(Yowab da ɗan’uwansa Abishai suka kashe Abner don yă kashe ɗan’uwansu Asahel a yaƙin Gibeyon.)
31 Mais David dit à Joab et à tout le peuple qui était avec lui: Déchirez vos vêtements et ceignez-vous de sacs, et menez deuil sur Abner. Et le roi David marcha derrière le cercueil.
Sa’an nan Dawuda ya ce wa Yowab da dukan mutanen da suke tare da shi, “Ku yayyage rigunarku, ku sa tsummoki, ku yi tafiya kuna kuka a gaban Abner.” Sarki Dawuda kansa ya bi masu ɗauke da gawar daga baya.
32 Et quand ils eurent enseveli Abner à Hébron, le roi éleva la voix et pleura près du tombeau d'Abner; et tout le peuple pleura aussi.
Suka binne Abner a Hebron, sarki kuwa ya ɗaga murya ya yi kuka a kabarin Abner.
33 Et le roi fit une complainte sur Abner, et dit: Abner devait-il mourir comme meurt un méchant?
Sarki ya kuma yi wannan waƙar makoki domin Abner ya ce, “Daidai ne Abner yă mutu, kamar yadda marasa bin doka suke mutuwa?
34 Tes mains ne furent point liées, ni tes pieds mis dans les fers. Tu es tombé comme on tombe devant les méchants! Et tout le peuple recommença à pleurer sur lui.
Hannuwanka ba a daure suke ba, ƙafafunka ba a tabaibaye suke ba. Ka mutu kamar waɗanda suke mutuwa a hannun mugaye.” Sai dukan mutane suka sāke fashe da kuka saboda shi.
35 Puis tout le peuple vint pour faire prendre quelque nourriture à David, pendant qu'il était encore jour; mais David fit serment et dit: Que Dieu me punisse sévèrement, si avant que le soleil soit couché, je goûte du pain ou quelque autre chose.
Sa’an nan duk suka zo suka roƙi Dawuda yă ci wani abu tun rana ba tă fāɗi ba; amma Dawuda ya rantse ya ce, “Bari Allah yă hukunta ni, in na ɗanɗana abinci ko wani abu kafin rana ta fāɗi!”
36 Et tout le peuple l'entendit, et l'approuva; et tout le peuple trouva bon tout ce que fit le roi.
Dukan mutane suka lura suka kuma ji daɗi ƙwarai, tabbatacce kome da sarki ya yi, ya gamshe su.
37 Ainsi, en ce jour-là, tout le peuple et tout Israël connut que ce n'était point par ordre du roi qu'on avait fait mourir Abner, fils de Ner.
Saboda haka a ranar dukan mutane da dukan Isra’ila suka gane sarki ba shi da hannu a kisan Abner ɗan Ner.
38 Et le roi dit à ses serviteurs: Ne savez-vous pas qu'un capitaine, et un grand capitaine, est tombé aujourd'hui en Israël?
Sa’an nan sarki ya ce wa mutanensa, “Ba ku gane cewa ɗan sarki kuma babban mutum ya mutu a ƙasar Isra’ila a yau ba?
39 Et je suis encore faible aujourd'hui, bien que j'aie été oint roi; mais ces gens, les fils de Tséruja, sont trop puissants pour moi. Que l'Éternel rende à celui qui a fait le mal, selon sa malice!
A yau, ko da yake ni naɗaɗɗen sarki ne, duk da haka na raunana, kuma waɗannan’ya’yan Zeruhiya sun fi ƙarfina. Ubangiji yă sāka wa mai aikata mugunta da muguntar da ya aikata!”

< 2 Samuel 3 >