< Maleachi 4 >

1 "Der Tag wird kommen, gleich einem Ofen flammt er auf. Die Frevler und die Missetäter all sind Stoppeln, und sie verzehrt der Tag, der kommt", so spricht der Herr der Heerscharen. "Von ihnen bleibt nicht Zweig noch Wurzel übrig.
“Tabbatacce rana tana zuwa; za tă yi ƙuna kamar wutar maƙera. Dukan masu girman kai da kowane mai aikata mugunta zai zama ciyawa, wannan rana mai zuwa za tă ƙone su. Babu saiwa ko reshen da za a bar musu,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
2 Euch aber, die ihr meinen Namen fürchtet, strahlt die Sonne der Gerechtigkeit, und Heilung liegt in ihren Strahlen. Ihr kommt hervor und hüpft wie Kälber aus dem Stalle,
Amma ku da kuke girmama sunana, ranar adalci za tă fito tare da warkarwa a fikafikanta. Za ku kuwa fita kuna tsalle kamar’yan maruƙan da aka sake daga garke.
3 die Frevler zu zertreten. Sie werden unter euren Füßen Staub an jenem Tag, da ich erscheine." So spricht der Herr der Heerscharen.
Sa’an nan za ku tattake mugaye; za su zama toka a ƙarƙashin tafin ƙafafunku a ranar da zan aikata waɗannan abubuwa, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
4 "Gedenket also des Gesetzes Mosis, meines Dieners! Am Horeb gab ich für ganz Israel Gebote ihm und Satzungen.
“Ku tuna da dokar bawana Musa, ƙa’idodi da dokokin da na ba shi a Horeb domin dukan Isra’ila.
5 Ich sende euch Elias, den Propheten, zu. Bevor der Tag des Herrn erscheint, der große, schreckliche,
“Ga shi, zan aika muku da annabi Iliya kafin babbar ranan nan mai banrazana ta Ubangiji tă zo.
6 bemüht er sich, das Herz der Väter für die Kinder, das Herz der Kinder für die Väter wiederzugewinnen. Sonst muß ich, wenn ich komme, das Land zum Untergang verdammen."
Zai juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, zukatan’ya’ya kuma ga iyayensu; in ba haka ba zan bugi ƙasar da hallaka gaba ɗaya.”

< Maleachi 4 >