< 2 Tarihi 14 >

1 Abiya kuwa ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda. Asa ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki, a zamaninsa kuma ƙasar ta zauna lafiya na shekara goma.
И почил Авия с отцами своими, и похоронили его в городе Давидовом. И воцарился Аса, сын его, вместо него. Во дни его покоилась земля десять лет.
2 Asa ya yi abin da yake da kyau da kuma daidai a gaban Ubangiji Allahnsa.
И делал Аса доброе и угодное в очах Господа Бога своего:
3 Ya kawar da baƙin bagade da masujadai bisa tudu, ya farfashe keɓaɓɓun duwatsu, ya kuma sassare ginshiƙan Ashera.
и отверг он жертвенники богов чужих и высоты, и разбил статуи, и вырубил посвященные дерева;
4 Ya umarci Yahuda su nemi Ubangiji Allah na kakanninsu, su kuma yi biyayya da dokoki da kuma umarnansa.
и повелел Иудеям взыскать Господа Бога отцов своих, и исполнять закон Его и заповеди;
5 Ya kawar da masujadan kan tudu da bagadan turare a kowane gari a Yahuda, masarautar kuwa ta zauna lafiya a ƙarƙashinsa.
и отменил он во всех городах Иудиных высоты и статуи солнца. И спокойно было при нем царство.
6 Ya gina biranen katanga na Yahuda, da yake ƙasar tana zaman lafiya. Babu wanda yake yaƙi da shi a waɗannan shekaru, gama Ubangiji ya ba shi hutu.
И построил он укрепленные города в Иудее, ибо спокойна была земля, и не было у него войны в те годы, так как Господь дал покой ему.
7 Ya ce wa Yahuda, “Bari mu gina waɗannan garuruwa mu sa katanga kewaye da su, da hasumiyoyi, ƙofofi da ƙyamare. Ƙasar har yanzu tamu ce domin mun nemi Ubangiji Allahnmu, mun neme shi ya kuwa ba mu hutu a kowane gefe.” Saboda haka suka gina suka kuma yi nasara.
И сказал он Иудеям: построим города сии и обнесем их стенами с башнями, с воротами и запорами. Земля еще наша, потому что мы взыскали Господа Бога нашего: мы взыскали Его, - и Он дал нам покой со всех сторон. И стали строить, и имели успех.
8 Asa ya kasance da mayaƙa dubu ɗari uku daga Yahuda, kintsatse da manyan garkuwoyi da māsu, da kuma mayaƙa dubu ɗari biyu da dubu tamanin daga Benyamin, riƙe da ƙananan garkuwoyi da kuma baka. Dukan waɗannan jarumawa ne ƙwarai.
И было у Асы военной силы: вооруженных щитом и копьем из колена Иудина триста тысяч, и из колена Вениаминова вооруженных щитом и стрелявших из лука двести восемьдесят тысяч, людей храбрых.
9 Zera mutumin Kush ya taka ya fita don yă yaƙe su da babban runduna da kuma kekunan yaƙi ɗari uku, ya kuma zo har Maresha.
И вышел на них Зарай Ефиоплянин с войском в тысячу тысяч и с тремястами колесниц и дошел до Мареши.
10 Asa ya fita don yă ƙara da shi, suka ja dāgā yaƙi a Kwarin Zefata kusa da Maresha.
И выступил Аса против него, и построились к сражению на долине Цефата у Мареши.
11 Sai Asa ya kira ga Ubangiji Allahnsa ya ce, “Ubangiji, babu wani kamar ka da zai taimaki marar ƙarfi a kan mai ƙarfi. Ka taimake mu, ya Ubangiji Allahnmu, gama mun dogara a gare ka, kuma a cikin sunanka muka fito don mu yaƙi wannan babbar runduna. Ya Ubangiji, kai ne Allahnmu; kada ka bar mutum yă yi nasara a kanka.”
И воззвал Аса к Господу Богу своему, и сказал: Господи! не в Твоей ли силе помочь сильному или бессильному? помоги же нам, Господи Боже наш: ибо мы на Тебя уповаем и во Имя Твое вышли мы против множества сего. Господи! Ты Бог наш: да не превозможет Тебя человек.
12 Ubangiji fa ya bugi mutanen Kush a gaban Asa da Yahuda. Mutanen Kush suka gudu,
И поразил Господь Ефиоплян пред лицем Асы и пред лицем Иуды, и побежали Ефиопляне.
13 Asa kuwa da mayaƙansa suka bi su har Gerar. Mutanen Kush suka mutu a ranan nan har ba a iya ƙidaya, aka buge su a gaban Ubangiji da rundunansa. Mutanen Yahuda suka kwashi ganima sosai.
И преследовал их Аса и народ, бывший с ним, до Герара, и пали Ефиопляне, так что у них никого не осталось в живых, потому что они поражены были пред Господом и пред воинством Его. И набрали добычи великое множество.
14 Suka hallaka dukan ƙauyukan kewaye da Gerar, gama tsoron Ubangiji ya kama su. Suka kwashi ganima na dukan ƙauyukan nan, da yake akwai ganima sosai a can.
И разрушили все города вокруг Герара, потому что напал на них ужас от Господа; и разграбили все города и вынесли из них весьма много добычи.
15 Suka kuma yaƙi sansanin makiyaya suka kwashe tumaki da awaki da raƙuma. Suka koma Urushalima.
Также и пастушеские шалаши разорили и угнали множество стад мелкого скота и верблюдов и возвратились в Иерусалим.

< 2 Tarihi 14 >