< 2 Sarakuna 2 >

1 Da lokaci ya yi da Ubangiji zai ɗauki Iliya zuwa sama cikin guguwa, Iliya da Elisha kuwa suna kan hanyarsu daga Gilgal.
Forsothe it was don, whanne the Lord wolde reise Elie bi a whirlewynd in to heuene, Elie and Elisee yeden fro Galgalis.
2 Sai Iliya ya ce wa Elisha, “Ka dakata a nan; Ubangiji ya aike ni Betel.” Amma Elisha ya amsa ya ce, “Muddin Ubangiji yana a raye, kai kuma kana a raye, ba zan rabu da kai ba.” Saboda haka suka gangara zuwa Betel.
And Elie seide to Elisee, Sitte thou here, for the Lord sente me til into Bethel. To whom Elisee seide, The Lord lyueth and thi soule lyueth, for Y schal not forsake thee. And whanne thei hadden come doun to Bethel,
3 Sai ƙungiyar annabawa a Betel suka fito zuwa wajen Elisha suka ce masa, “Ka san cewa Ubangiji zai ɗauki maigidanka daga wurinka yau?” Sai ya ce, “I, na sani, amma kada ku yi magana game da wannan.”
the sones of prophetis, that weren in Bethel, yeden out to Elisee, and seiden to hym, Whether thou knowist, that the Lord schal take awey thi lord to dai fro thee? Which answeride, And I knowe; be ye stille.
4 Sai Iliya ya ce masa, “Ka dakata a nan Elisha; Ubangiji ya aike ni Yeriko.” Sai ya ce masa, “Muddin Ubangiji yana a raye, kai ma kana a raye, ba zan rabu da kai ba.” Saboda haka sai suka tafi Yeriko.
Forsothe Elie seide to Elisee, Sitte thou here, for the Lord sente me into Jerico. And he seide, The Lord lyueth and thi soule lyueth, for Y schal not forsake thee. And whanne thei hadden come to Jerico,
5 Ƙungiyar annabawa a Yeriko suka haura zuwa wajen Elisha suka ce, “Ko ka san Ubangiji zai ɗauki maigidanka daga gare ka yau?” Sai ya ce, “I, na sani, amma ku bar zancen nan tukuna.”
the sones of prophetis, that weren in Jerico, neiyiden to Elisee, and seiden to hym, Whether thou knowist, that the Lord schal take awei thi lord to dai fro thee? And he seide, Y knowe; be ye stille.
6 Sai Iliya ya ce masa, “Ka dakata a nan, Ubangiji ya aike ni Urdun.” Sai Elisha ya ce masa, “Muddin Ubangiji yana a raye, kai kuma kana raye, ba zan rabu da kai ba.” Saboda haka suka ci gaba da tafiya tare.
Forsothe Elie seide to Elisee, Sitte thou here, for the Lord sente me `til to Jordan. Which seide, The Lord lyueth and thi soule lyueth, for Y schal not forsake thee. Therfor bothe yeden togidere;
7 Mutum hamsin na ƙungiyar annabawa suka je suka tsaya da nisa, suna fuskantar inda Iliya da Elisha suka tsaya a Urdun.
and fifti men of the sones of prophetis sueden, which also stoden fer euen ayens; sothely thei bothe stoden ouer Jordan.
8 Sai Iliya ya tuɓe rigarsa, ya nannaɗe ya bugi ruwan Urdun da shi. Sai ruwan ya dāre gida biyu, suka haye a busasshiyar ƙasa.
And Elie took his mentil, and wlappide it, and smoot the watris; whiche weren departid `into euer ethir part, and bothe yeden bi the drie.
9 Da suka haye, sai Iliya ya ce wa Elisha, “Faɗi mini, abin da kake so in yi maka kafin a ɗauke ni daga gare ka!” Elisha ya amsa ya ce, “Bari in gāji ninki biyu na ruhunka.”
And whanne thei hadden passid, Elie seide to Elisee, Axe thou that, that thou wolt that Y do to thee, bifor that Y be takun awey fro thee. And Elisee seide, Y biseche, that thi double spirit be `maad in me.
10 Iliya ya ce, “Ka nemi abu mai wuya, amma in ka ga lokacin da aka ɗauke ni daga gare ka, zai zama naka, in ba haka ba, ba za ka samu ba ke nan.”
Which Elie answeride, Thou axist an hard thing; netheles if thou schalt se me, whanne Y schal be takun awei fro thee, that that thou axidist schal be; sotheli, if thou schalt not se, it schal not be.
11 Yayinda suke tafiya suna magana, sai kwatsam, keken yaƙin wuta da dawakan wuta suka ratse tsakaninsu, sai Iliya ya tafi sama a cikin guguwa.
And whanne thei yeden, and spaken goynge, lo! a chare of fier and horsys of fier departiden euer either; and Elie stiede bi a whirlewynd in to heuene.
12 Da Elisha ya ga haka sai ya yi ihu yana cewa, “Babana! Babana! Kekunan yaƙin da mahayan dawakan Isra’ila!” Elisha kuwa bai sāke ganinsa ba. Sai ya kama tufafinsa ya yayyage.
Forsothe Elise siy, and criede, My fadir! my fadir! the chare of Israel, and the charietere therof. And he siy no more Elie. And he took hise clothis, and to-rente tho in to twei partis.
13 Sai ya ɗauki rigar da ta fāɗo daga Iliya ya koma ya tsaya a gaɓar Kogin Urdun.
And he reiside the mentil of Elie, that felde doun to hym; and he turnede ayen, and stood ouer the ryuer of Jordan.
14 Sa’an nan Elisha ya ɗauki rigar da ta fāɗo daga Iliya ya bugi ruwan da shi. Ya ce, “Yanzu ina Ubangiji Allah na Iliya?” Da ya bugi ruwan sai ruwan ya dāre gida biyu, sai ya haye.
And with the mentil of Elie, that felde doun to hym, he smoot the watris, whiche weren not departid. And he seide, Where is God of Elie also now? And he smoot the watris, and tho weren departid hidur and thidur; and Elisee passide.
15 Ƙungiyar annabawa daga Yeriko, waɗanda suke kallo, suka ce, “Ruhun Iliya yana a kan Elisha.” Sai suka je su tarye shi, suka rusuna har ƙasa a gabansa.
Sotheli the sones of prophetis, that weren in Jerico euene ayens, siyen, and seiden, The spirit of Elie restide on Elisee. And thei camen in to the meetyng of hym, and worschipiden hym lowli to erthe.
16 Suka ce, “Duba, mu bayinka muna da masu ji da ƙarfi hamsin. Bari su je su nemi maigidanka. Wataƙila, Ruhun Ubangiji ya ɗauke shi ya ajiye bisa wani dutse, ko wani kwari.” Elisha ya ce, “A’a, kada ku aike su.”
And thei seiden to hym, Lo! with thi seruauntis ben fifti stronge men, that moun go, and seke thi lord, lest perauenture the Spirit of the Lord hath take hym, and hath cast forth hym in oon of the hillis, ethir in oon of the valeys.
17 Amma suka matsa masa har ya ji ba ya iya hana su. Saboda haka ya ce, “Ku aike su.” Sai suka aiki mutane hamsin, suka yi ta nema har kwana uku amma ba su same Iliya ba.
Which seide, `Nyle ye sende. And thei constreyneden hym, til he assentide to hem, and seide, Sende ye. And thei senten fifti men; and whanne thei hadden souyt bi thre daies, thei founden not.
18 Da suka dawo wurin Elisha, wanda yake a Yeriko, sai ya ce musu, “Ban ce muku kada ku tafi ba?”
And thei turneden ayen to hym; and he dwelide in Jerico. And he seide to hem, Whether Y seide not to you, Nyle ye sende?
19 Mutane garin suka ce wa Elisha, “Ranka yă daɗe, duba, garin yana da kyan gani, amma ruwan ba shi da kyau, ƙasar kuma ba ta ba da amfani.”
Therfor the men of the citee seiden to Elisee, Lo! the dwellyng of this cite is ful good, as thou thi silf, lord, seest; but the watris ben ful yuele, and the lond is bareyn.
20 Sai ya ce, “Ku kawo mini sabuwar ƙwarya, ku kuma sa gishiri a ciki.” Sai suka kawo masa.
And he seide, Brynge ye to me a newe vessel, and sende ye salt in to it. And whanne thei hadden brouyt it,
21 Sai ya tafi maɓulɓular ruwan yana watsa gishirin a ciki, yana cewa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Na warkar da ruwan nan. Ba zai ƙara jawo mutuwa, ko yă hana ƙasar ba da amfani ba.’”
he yede out to the welle of watris, and sente salt in to it, and seide, The Lord seith these thingis, Y haue helid these watris, and nethir deeth, nether bareynesse, schal be more in tho.
22 Ruwan ya tsabtacce har yă zuwa yau, bisa ga faɗin Elisha.
Therfor the watris weren heelid til in to this dai, bi the word of Elisee, which he spak.
23 Daga nan sai Elisha ya tafi Betel. Yayinda yake tafiya a hanya, sai waɗansu matasa suka fito daga cikin gari, suka yi masa dariya suna cewa, “Ka haura, ya kai mai kai marar gashi! Ka haura, kai mai kai marar gashi!”
Forsothe Elisee stiede fro thennus in to Bethel; and whanne he stiede bi the weie, litle children yeden out of the citee, and scorneden hym, and seiden, Stie, thou ballard! stie, thou ballard!
24 Sai ya juya ya dube su, ya la’anta su da sunan Ubangiji. Sai beyar guda biyu suka fito daga jeji suka hallaka matasa arba’in da biyu daga cikinsu.
And whanne he hadde biholde, he siy hem, and curside hem in the name of the Lord. And twey beeris yeden out of the forest, and to-rente fourti children of hem.
25 Sai ya ci gaba zuwa Dutsen Karmel, daga can kuma ya koma Samariya.
Sotheli Elisee wente fro thennus in to the hil of Carmele, and fro thennus he turnede `ayen to Samarie.

< 2 Sarakuna 2 >