< 2 Sarakuna 3 >

1 Yoram, ɗan Ahab ya zama sarki Isra’ila, a Samariya, a shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yehoshafat, sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki shekara goma sha biyu.
And Jehoram [the] son of Ahab he became king over Israel in Samaria in year eight-teen of Jehoshaphat [the] king of Judah and he reigned two [plus] ten year[s].
2 Yoram ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, amma ba kamar yadda mahaifinsa da mahaifiyarsa suka yi ba. Ya kawar da dutsen tsarkin Ba’al wanda mahaifinsa ya yi.
And he did the evil in [the] eyes of Yahweh only not like father his and like mother his and he removed [the] sacred pillar of Baal which he had made father his.
3 Duk da haka ya manne wa zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, bai rabu da su ba.
Only to [the] sins of Jeroboam [the] son of Nebat which he caused to sin Israel he clung not he turned aside from it.
4 Mesha, sarkin Mowab yana kiwon tumaki, ya kuma zama tilas yă biya haraji ga sarkin Isra’ila. Saboda haka yakan ba da’yan tumaki dubu ɗari, da kuma gashin raguna dubu ɗari.
And Mesha [the] king of Moab he was a sheep-breeder and he returned to [the] king of Israel one hundred thousand lambs and one hundred thousand rams wool.
5 Amma bayan mutuwar Ahab, sai sarkin Mowab ya yi wa sarkin Isra’ila tawaye.
And it was when died Ahab and he rebelled [the] king of Moab against [the] king of Israel.
6 To, a lokacin, Sarki Yoram ya tashi daga Samariya, ya tattara sojoji daga dukan Isra’ila.
And he went out the king Jehoram on the day that from Samaria and he mustered all Israel.
7 Ya kuma aika da wannan saƙo ga Yehoshafat sarkin Yahuda cewa, “Sarkin Mowab ya yi mini tawaye. Za ka tafi tare da ni mu yaƙi Mowab?” Sai sarkin Yahuda ya ce, “I, ina shirye mu tafi. Ai, sojojina sojojinka ne, dawakaina kuma dawakanka ne.”
And he went and he sent to Jehoshaphat [the] king of Judah saying [the] king of Moab he has rebelled against me ¿ will you go with me against Moab for battle and he said I will go up as me as you as people my as people your as horses my as horses your.
8 Ya ƙara da cewa, “Wace hanya za mu bi?” Sai Yoram ya amsa ya ce, “Ta hanyar jejin Edom.”
And he said where? this [is] the way [which] we will go up and he said [the] way of [the] wilderness of Edom.
9 Saboda haka sarkin Isra’ila ya fita tare da sarkin Yahuda, da kuma sarkin Edom. Da suka yi kwana bakwai suna ta zagawa, sai sojoji da dabbobi suka rasa ruwan sha.
And he went [the] king of Israel and [the] king of Judah and [the] king of Edom and they went around a journey of seven days and not it belonged water to the army and to the animal[s] which [was] at feet their.
10 Sai sarkin Isra’ila ya ce, “Mene! Ubangiji ya kira mu sarakunan nan uku don kawai yă ba da mu ga Mowab ne?”
And he said [the] king of Israel alas! for he has summoned Yahweh [the] three the kings these to give them in [the] hand of Moab.
11 Amma Yehoshafat ya yi tambaya ya ce, “Babu wani annabin Ubangiji a nan da za mu nemi nufin Ubangiji ta wurinsa?” Wani hafsan sarkin Isra’ila ya amsa ya ce, “Ai, akwai Elisha ɗan Shafat, wanda dā ya yi wa Iliya hidima.”
And he said Jehoshaphat ¿ [is] there not here a prophet of Yahweh and let us consult Yahweh from him and he answered one from [the] servants of [the] king of Israel and he said [is] here Elisha [the] son of Shaphat who he poured water on [the] hands of Elijah.
12 Yehoshafat ya ce, “Maganar Ubangiji tana tare da shi.” Saboda haka sarkin Isra’ila da Yehoshafat da kuma sarkin Edom suka tafi wurin Elisha.
And he said Jehoshaphat there him [is] [the] word of Yahweh and they went down to him [the] king of Israel and Jehoshaphat and [the] king of Edom.
13 Elisha ya ce wa sarkin Isra’ila, “Ina ruwana da kai? Tafi wurin annabawan mahaifinka da annabawa mahaifiyarka.” Sai sarkin Isra’ila ya ce, “A’a, ai Ubangiji ne ya kira mu, mu sarakunan nan uku don yă bashe mu ga Mowab.”
And he said Elisha to [the] king of Israel what? [is] to me and to you go to [the] prophets of father your and to [the] prophets of mother your and he said to him [the] king of Israel may not [it be so] for he has summoned Yahweh [the] three the kings these to give them in [the] hand of Moab.
14 Sai Elisha ya ce, “Muddin Ubangiji Maɗaukaki yana a raye, wanda nake bauta, da ba don ina ganin girman Yehoshafat Sarkin Yahuda ba, da ko kallonka ba zan yi ba.
And he said Elisha [by] [the] life of Yahweh of hosts whom I stand before him for if not [the] face of Jehoshaphat [the] king of Judah I [am] lifting up if I will look to you and if I will see you.
15 Amma yanzu, a kawo mini makaɗin garaya.” Yayinda makaɗin garayan yake kiɗa, ikon Ubangiji ya sauko a kan Elisha
And now fetch for me a musician and it was when played the musician and it was on him [the] hand of Yahweh.
16 ya kuma ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, zan cika kwarin nan da tafkunan ruwa.
And he said thus he says Yahweh make the wadi this ditches - ditches.
17 Gama ga abin da Ubangiji ya ce, ko da yake babu iska, ko ruwan sama, duk da haka kwarin nan zai cika da ruwa, har ku da dabbobinku da kuma sauran dabbobi ku sha.
For thus - he says Yahweh not you will see wind and not you will see rain and the wadi that it will be filled water and you will drink you and livestock your and animal[s] your.
18 Wannan abu mai sauƙi ne a wurin Ubangiji; zai kuma ba da Mowab a gare ku.
And it will be trifling this in [the] eyes of Yahweh and he will give Moab in hand your.
19 Za ku ci kowane birni mai katanga, da kowane babban gari. Za ku sare kowane itace mai kyau, ku kuma tattoshe maɓuɓɓugan ruwa. Za ku kuma yi amfani da duwatsu ku lalatar da kowace gona mai kyau.”
And you will strike down every city of fortification and every city of choice and every tree good you will make fall and all [the] springs of water you will stop up and every portion of land good you will spoil with stones.
20 Kashegari, daidai lokacin hadaya, sai ga ruwa yana gangarowa daga gefen Edom! Ƙasar kuwa ta cika da ruwa.
And it was in the morning when went up the offering and there! waters [were] coming from [the] direction of Edom and it was filled the land the waters.
21 To, dukan Mowabawa suka ji cewa sarakuna suna tafe don su yaƙe su; saboda haka aka kira kowane namiji, babba da yaro, wanda ya isa ɗaukan makami, aka jera su a bakin iyaka.
And all Moab they had heard that they had come up the kings to fight against them and they were summoned from every [one who] girds on a belt and up-wards and they took their stand at the border.
22 Da suka tashi da sassafe, rana tana haska ruwa. Sai ruwan ya yi ja kamar jini a idanun Mowabawan da suke a ƙetare.
And they rose early in the morning and the sun it shone on the water and they saw Moab from before the water red like blood.
23 Sai suka ce, “Jini ne! Ba shakka sarakunan nan sun yaƙe juna, suka karkashe juna. Ya Mowabawa, mu tafi mu kwashi ganima!”
And they said [is] blood this certainly they have fought one another the kings and they have struck down each neighbor his and therefore to the plunder O Moab.
24 Amma da Mowabawa suka isa sansanin Isra’ila, sai Isra’ilawa suka taso suka auka musu har sai da suka gudu. Isra’ilawa kuwa suka kai musu hari, suka karkashe Mowabawa.
And they came to [the] camp of Israel and they arose Israel and they struck down Moab and they fled from before them (and they struck down *Q(K)*) it and they struck down Moab.
25 Suka ragargaza garuruwa, kowane mutum kuwa ya jefa dutse a kowane gona mai kyau har sai da aka rufe gonakin gaba ɗaya. Suka tattoshe duk maɓulɓulan ruwa, suka kuma sare duk itace mai kyau. Kir Hareset ne kaɗai aka bari tare da duwatsunsa yadda suke, amma mutanen da suke da majajjawa suka yi wa birnin zobe, suka kai masa hari shi ma.
And the cities they tore down and every portion of land good they threw each stone his and they filled it and every spring of water they stopped up and every tree good they made fall until he left behind stones its in Kir Hareseth and they surrounded [it] the slingers and they struck it.
26 Da sarkin Mowab ya ga yaƙi ya rinjaye shi, sai ya ɗauki mutane masu takobi ɗari bakwai, ya ratsa zuwa wajen sarkin Edom, amma ba su yi nasara ba.
And he saw [the] king of Moab that it was [too] strong for him the battle and he took him seven hundred man [who] drew a sword to break through to [the] king of Edom and not they were able.
27 Sa’an nan ya ɗauki ɗansa na fari, wanda zai gāje shi, ya yi hadaya da shi a bisa katangan birnin. Isra’ilawa suka firgita ƙwarai; sai suka janye suka koma ƙasarsu.
And he took son his the firstborn who he will reign in place of him and he offered up him a burnt offering on the wall and it was wrath great towards Israel and they departed from on him and they returned to the land.

< 2 Sarakuna 3 >