< 2 Sarakuna 4 >

1 Matar wani daga ƙungiyar annabawa ta yi wa Elisha kuka ta ce, “Mijina, bawanka, ya mutu, ka kuma san yadda ya girmama Ubangiji. Amma ga shi yanzu mai binsa bashi ya zo yă kwashe’ya’yana maza biyu su zama bayinsa.”
Torej tam je neka ženska, izmed žena preroških sinov, zaklicala k Elizeju, rekoč: »Tvoj služabnik, moj soprog, je mrtev, in ti veš, da se je tvoj služabnik bal Gospoda in prišel je upnik, da bi si moja dva sinova k sebi vzel za sužnja.«
2 Elisha ya amsa mata ya ce, “Me kike so in yi miki? Ki faɗa mini, me kike da shi a gidanki?” Sai ta ce, “Baiwarka ba ta da kome a can, sai ɗan tulun man zaitun.”
Elizej ji je rekel: »Kaj naj storim zate? Povej mi, kaj imaš v hiši?« Rekla je: »Tvoja pomočnica nima v hiši ničesar razen lonca olja.«
3 Elisha ya ce, “Ki je wurin dukan maƙwabtanki, ki nemi tulunan da babu kome a ciki. Kada ki nemo kaɗan kawai.
Potem je rekel: »Pojdi, izposodi si posode od vseh svojih sosed, prazne posode. Ne izposodi si jih malo.
4 Sa’an nan ki shiga ciki, ki kulle ƙofar da ke da’ya’yanki kuke ciki. Ku ɗuɗɗura man a dukan tulunan, sa’ad da kowanne ya cika, sai ki ajiye a gefe.”
Ko vstopiš noter, boš za seboj in za svojima sinovoma zaprla vrata in izlivala v vse tiste posode in tisto, ki je polna, boš postavila na stran.«
5 Ta tashi ta shiga tare da’ya’yanta maza, suka kulle ƙofa.’Ya’yanta suka kawo mata tuluna, ita kuma tana ɗurawa.
Tako je odšla od njega in za seboj in za svojima sinovoma, ki sta k njej prinesla posode, zaprla vrata in ona je izlivala.
6 Da dukan tulunan suka cika, sai ta ce wa ɗanta, “Kawo mini wani tulu.” Amma ya amsa ya ce, “Ai, ba saura.” Sa’an nan man ya daina zuba.
Pripetilo se je, ko so bile posode polne, da je svojemu sinu rekla: »Še mi prinesi posodo.« Rekel ji je: »Nobene posode ni več.« In olje se je ustavilo.
7 Sai ta tafi ta faɗa wa mutumin Allah. Shi kuwa ya ce mata, “Tafi, ki sayar da man, ki biya bashinki. Ki biya bukatanki da na’ya’yanki da sauran da ya rage.”
Potem je prišla in povedala Božjemu možu. Rekel je: »Pojdi, prodaj olje in poplačaj svoj dolg in od preostanka živite ti in tvoja otroka.«
8 Wata rana Elisha ya tafi Shunem. Akwai wata mai arziki a can wadda ta gayyace shi cin abinci. Sai ya zama duk lokacin da yake wucewa, yakan tsaya a can don cin abinci.
Zgodilo se je na nek dan, da je Elizej odšel v Šuném, kjer je bila plemenita ženska; in ta ga je primorala, da jé kruh. In to je bilo tako, da tako pogosto, kot je šel mimo, se je obrnil tja, da bi jedel kruh.
9 Ta ce wa mijinta, “Na san cewa wannan mutum da kullum yake zuwa nan mai tsarki ne na Allah.
Svojemu soprogu je rekla: »Glej torej, zaznavam, da je to sveti Božji mož, ki nenehno hodi mimo nas.
10 Bari mu yi ɗan ɗaki a rufin gida mu kuma sa masa gado da tebur da kujera da kuma fitila. Saboda a duk lokacin da ya zo wurinmu, sai yă sauka a can.”
Narediva majhno sobo, prosim te, na zidu in tam zanj postavimo posteljo, mizo, stolček in svečnik. In zgodilo se bo, ko prihaja k nam, da se bo obrnil tja noter.«
11 Wata rana da Elisha ya zo, sai ya haura ɗakinsa ya kwanta.
Zgodilo se je na nek dan, da je prišel tja, se obrnil v sobo in se tam ulegel.
12 Ya ce wa bawansa Gehazi, “Kira mutuniyar Shunam nan.” Sai ya kira ta, ta zo ta tsaya a gabansa.
Svojemu služabniku Gehazíju je rekel: »Pokliči to Šunémko.« Ko jo je ta poklical, je obstala pred njim.
13 Elisha ya ce masa, “Ka ce mata, ‘Kin yi duk wannan ɗawainiya saboda mu. Yanzu, me kike so a yi miki? Kina so mu yi magana a madadinki wa sarki ko babban hafsan mayaƙa?’” Sai ta ce, “A’a, ina da dukan abin da nake bukata a cikin jama’ata.”
Rekel mu je: »Sedaj ji povej: ›Glej, hitela si za naju z vso to skrbjo. Kaj naj bo storjeno zate? Ali naj zate govorim kralju ali poveljniku vojske?‹« Odgovorila je: »Prebivam med svojim lastnim ljudstvom.«
14 Sai Elisha ya tambayi Gehazi ya ce, “Me za mu yi mata?” Sai ya amsa ya ce, “Ba ta da ɗa, ga shi kuma mijinta ya tsufa.”
Rekel je: »Kaj naj bo potem storjeno zanjo?« Gehazí je odgovoril: »Resnično, ona nima otroka in njen soprog je star.«
15 Sai Elisha ya ce, “Ka kira ta.” Sai ya kira ta, ta zo ta tsaya a bakin ƙofa.
Rekel je: »Pokliči jo.« Ko jo je poklical, je obstala med vrati.
16 Elisha ya ce mata, “War haka baɗi, za ki riƙe ɗa na kanki.” Sai ta ce masa, “A’a, ranka yă daɗe, mutumin Allah, kada ka ruɗi baiwarka!”
Rekel je: »Okoli tega obdobja, glede na čas življenja, boš objemala sina.« Rekla je: »Ne, moj gospod, Božji mož, ne laži svoji pomočnici.«
17 Amma matan ta yi ciki, a shekara ta biye kuwa a daidai lokacin, sai ta haifi ɗa kamar yadda Elisha ya faɗa mata.
Ženska je spočela in rodila sina v tistem obdobju, ki ji ga je Elizej povedal, glede na čas življenja.
18 Yaron ya yi girma, wata rana sai ya tafi wurin mahaifinsa, wanda yake tare da masu girbi.
Ko je otrok postal večji, se je nekega dne zgodilo, da je odšel ven k svojemu očetu, k žanjcem.
19 Ba zato sai ya ce wa mahaifinsa, “Wayyo! Kaina yana mini ciwo! Kaina yana mini ciwo!” Sai mahaifinsa ya ce wa bawansa, “Kai shi wurin mahaifiyarsa.”
Svojemu očetu je rekel: »Moja glava, moja glava.« In ta je rekel mladeniču: »Odnesi ga k njegovi materi.«
20 Bayan bawan ya ɗaga shi ya kai wurin mahaifiyarsa, sai yaron ya zauna a cinyarta har tsakar rana, sa’an nan ya mutu.
Ko ga je ta vzel in ga privedel k njegovi materi, je do opoldneva sedel na njenih kolenih, potem pa je umrl.
21 Sai ta haura ta shimfiɗa shi a gadon mutumin Allah, ta rufe ƙofar, ta fita.
Vzdignila se je, ga položila na posteljo Božjega moža, zaprla vrata za njim in odšla ven.
22 Ta kira mijinta ta ce, “Ina roƙonka ka aika mini da ɗaya daga cikin bayi da kuma jaka, don in yi sauri in je wurin mutumin Allah in dawo.”
Poklicala je k svojemu soprogu in rekla: »Pošlji mi, prosim te, enega izmed mladeničev in enega izmed oslov, da lahko stečem k Božjemu možu in ponovno pridem nazaj.«
23 Sai ya ce, “Me zai kai ki wurinsa, ai, yau ba Sabon Wata ba ne ko ranar Asabbaci?” Sai ta ce, “Ba kome.”
Rekel je: »Čemu hočeš iti k njemu danes? Ni niti mlaj niti šabat.« Rekla je: » To bo dobro.«
24 Sai ta sa wa jakar sirdi ta ce wa bawanta, “Yi ta kora mini jakar, kada ka sassauta, sai na faɗa maka.”
Potem je osedlala osla in svojemu mladeniču rekla: »Požêni in pojdi naprej. Svojega jahanja ne upočasnjuj zaradi mene, razen če ti ne zapovem.«
25 Ta haka ta kama hanya ta tafi wurin mutumin Allah a Dutsen Karmel. Da ya hange ta daga nesa, sai mutumin Allah ya ce wa bawansa Gehazi, “Duba! Ga mutuniyar Shunam nan can!
Tako je odšla in prišla k Božjemu možu na goro Karmel. Pripetilo se je, ko jo je Božji mož od daleč zagledal, da je svojemu služabniku Gehazíju rekel: »Glej, tam je ta Šunémka.
26 Ka yi gudu ka tarye ta ka tambaye ta, ‘Lafiyarki? Mijinki yana nan lafiya? Yaronki yana nan lafiya?’” Ta amsa ta ce, “Kome lafiya yake.”
Steci sedaj, prosim te, da jo srečaš in ji reci: › Ali je dobro s teboj? Ali je dobro s tvojim soprogom? Ali je dobro z otrokom?‹« Odgovorila je: »Dobro je.«
27 Da ta isa wurin mutumin Allah a dutsen, sai ta kama ƙafafunsa. Sai Gehazi ya zo don yă ture ta, amma mutumin Allah ya ce, “Ka bar ta! Tana cikin baƙin ciki ƙwarai, amma Ubangiji ya ɓoye mini, bai kuma faɗa mini me ya sa ba.”
Ko pa je prišla k Božjemu možu na hrib, se je oklenila njegovih stopal. Toda Gehazí se je približal, da jo pahne proč. Božji mož pa je rekel: »Pusti jo; kajti njena duša je zagrenjena znotraj nje in Gospod je to skril pred menoj in mi ni povedal.«
28 Sai ta tambaya shi ta ce, “Na roƙe ka ɗa ne, ranka yă daɗe? Ba na ce maka, ‘Kada ka sa in fara bege ba’?”
Potem je rekla: »Ali sem si jaz želela sina od svojega gospoda?« Ali nisem rekla: »Ne zavajaj me?«
29 Elisha ya ce wa Gehazi, “Ka yi ɗamara, ka ɗauki sandana ka ruga a guje. Idan ka sadu da wani, kada ka gaishe shi, idan kuma wani ya gaishe ka, kada ka amsa. Ka shimfiɗa sandana a fuskar yaron.”
Potem je rekel Gehazíju: »Opaši svoja ledja in v svojo roko vzemi mojo palico in pojdi svojo pot. Če srečaš kateregakoli človeka, ga ne pozdravi in če kdorkoli pozdravi tebe, mu ravno tako ne odgovori, in mojo palico položi na otrokov obraz.«
30 Amma mahaifiyar yaron ta ce, “Muddin Ubangiji yana raye, kai kuma kana a raye, ba zan bar ka ba.” Saboda haka ya tashi ya bi ta.
Otrokova mati je rekla: » Kakor Gospod živi in kakor tvoja duša živi, te ne bom zapustila.« Vstal je in ji sledil.
31 Gehazi ya yi gaba, ya shimfiɗa sandan a fuskar yaron, amma babu motsi, babu alamar rai. Saboda haka Gehazi ya koma ya taryi Elisha, ya faɗa masa, “Yaron bai tashi ba.”
Gehazí je šel pred njima in palico položil na otrokov obraz, toda ni bilo niti glasu niti uslišanja. Zatorej je ponovno odšel, da ga sreča in mu povedal, rekoč: »Otrok se ni prebudil.«
32 Da Elisha ya isa gidan, sai ga gawar yaron kwance a kan gadonsa.
Ko je Elizej prišel v hišo, glej, je bil otrok mrtev in položen na njegovo posteljo.
33 Sai ya shiga, ya rufe ƙofa, daga shi sai yaron, ya kuma yi addu’a ga Ubangiji.
Vstopil je torej in zaprl vrata za njima ter molil h Gospodu.
34 Sa’an nan ya hau gadon yă kwanta a bisa yaron, ya miƙe a kansa, baki da baki, ido da ido, hannu da hannu. Yayinda ya miƙe kansa a kan yaron, sai jikin yaron ya ɗau ɗumi.
Povzpel se je in legel na otroka ter svoja usta položil na njegova usta in svoje oči na njegove oči in svoje roke na njegove roke. Raztegnil se je nad otrokom in otrokovo meso se je ogrelo.
35 Elisha ya tashi, ya yi ta kai komo a cikin ɗakin. Sa’an nan ya sāke koma kan gadon yă miƙe a kan yaron, sai yaron ya yi atishawa sau bakwai, ya kuma buɗe idanunsa.
Potem se je vrnil in po hiši hodil sem ter tja, se povzpel in sebe raztegnil nad njim. Otrok je sedemkrat kihnil in otrok je odprl svoje oči.
36 Elisha ya kira Gehazi ya ce, “Kirawo mutuniyar Shunam.” Ya kuwa kira ta. Sa’ad da ta zo, sai Elisha ya ce mata, “Ɗauki ɗanki.”
Poklical je Gehazíja in rekel: »Pokliči to Šunémko.« Tako jo je poklical. Ko je vstopila k njemu, je rekel: »Vzemi svojega sina.«
37 Sai ta shiga, ta fāɗi a ƙafafunsa ta rusuna har ƙasa. Sa’an nan ta ɗauki ɗanta ta fita.
Potem je vstopila, padla k njegovim stopalom, se priklonila do tal, vzela svojega sina in odšla ven.
38 Sai Elisha ya koma Gilgal, a can kuwa ana yunwa a yankin. Yayinda ƙungiyar annabawa suke tattaunawa da shi, sai ya ce wa Gehazi bawansa, “Ka sa babban tukunya a wuta, ka yi wa mutanen nan fate.”
Elizej je ponovno prišel v Gilgál. Tam pa je bilo v deželi pomanjkanje. Sinovi prerokov so sedeli pred njim. Svojemu služabniku je rekel: »Pristavi velik lonec in za sinove prerokov zavri juho.«
39 Ɗaya daga cikin mutanen ya shiga gona don neman ganyaye, ya kuwa sami kabewar jeji. Ya tsinko’ya’yanta cike da shafin rigarsa. Da ya dawo, sai ya yayyanka su ya zuba a cikin tukunyar faten, ko da yake ba wanda ya san ko mene ne.
Nekdo je odšel na polje, da nabere zelišča in našel divjo trto in od nje nabral polno naročje divjih buč in prišel in jih zrezal v lonec juhe, kajti niso jih poznali.
40 Sai aka zuba wa mutanen faten, amma da suka fara ci, sai suka yi ihu suna cewa, “Ya mutumin Allah, akwai dafi a cikin tukunyan nan!” Suka kuwa kāsa ci.
Tako so nalili, da bi možje jedli. Pripetilo pa se je, ko so jedli juho, da so zavpili in rekli: »Oh ti Božji mož, smrt je v loncu.« In tega niso mogli jesti.
41 Elisha ya ce, “Samo mini ɗan gari.” Aka kawo masa ya kuma sa a cikin tukunyan ya ce, “Raba wa mutanen su ci.” Ya kasance kuwa babu wani abin damuwa a tukunyar.
Toda rekel je: »Torej prinesite moko.« Vrgel jo je v lonec in rekel: »Nalij za ljudstvo, da bodo lahko jedli.« In v loncu ni bilo nič škodljivega.
42 Sai ga wani mutum ya zo daga Ba’al-Shalisha, ya kawo wa Elisha dunƙulen burodi guda ashirin na sha’ir da aka gasa daga nunan fari na hatsi, tare da kawunan sababbin hatsi. Sai Elisha ya ce, “Ka ba mutanen su ci.”
Prišel je mož iz Báal Šalíša in Božjemu možu prinesel kruh od prvih sadov, dvajset ječmenovih hlebov in polno žitno klasje v luščinah. Rekel je: »Dajte ljudstvu, da bodo lahko jedli.«
43 Sai bawansa ya ce, “Yaya zan raba wa mutane ɗari wannan?” Amma Elisha ya amsa ya ce, “Ka raba wa mutane su ci, gama haka Ubangiji ya ce, ‘Za su ci har su bar saura.’”
Njegov strežnik pa je rekel: »Kaj, mar naj bi to postavil pred sto mož?« Ponovno je rekel: »Daj ljudstvu, da bodo lahko jedli, kajti tako govori Gospod: › Od tega bodo jedli in še bo ostalo.‹«
44 Sa’an nan ya ajiye a gabansu, suka kuwa ci har suka bar saura, bisa ga maganar Ubangiji.
Tako je to postavil prednje in so jedli in od tega pustili, glede na Gospodovo besedo.

< 2 Sarakuna 4 >