< Fitowa 1 >

1 Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Isra’ila maza, waɗanda suka tafi Masar tare da Yaƙub; kowanne da iyalinsa.
Now these [are] the names of the children of Israel, who came into Egypt; every man and his household came with Jacob.
2 Ruben, Simeyon, Lawi da Yahuda;
Reuben, Simeon, Levi, and Judah,
3 Issakar, Zebulun da Benyamin;
Issachar, Zebulun, and Benjamin,
4 Dan da Naftali; Gad da Asher.
Dan, and Naphtali, Gad, and Asher.
5 Zuriyar Yaƙub duka sun kai mutum saba’in. Yusuf ya riga ya kasance a Masar.
And all the souls that descended from Jacob, were seventy souls: for Joseph was in Egypt [already].
6 Yanzu Yusuf da dukan’yan’uwansa da kuma dukan tsaran nan da suka tafi Masar, sun mutu,
And Joseph died, and all his brethren, and all that generation.
7 amma Isra’ilawa sun riɓaɓɓanya, suka kuma yi ta haihuwa sosai, suka yi yawan sosai, har ƙasar ta cika da su.
And the children of Israel were fruitful, and increased abundantly, and multiplied, and became exceeding mighty; and the land was filled with them.
8 Sai wani sabon sarki wanda bai san Yusuf ba, ya hau sarautar Masar.
Now there arose a new king over Egypt, who knew not Joseph.
9 Ya ce wa mutanensa, “Duba Isra’ilawa sun yi yawa, sun fi ƙarfinmu.
And he said to his people, Behold, the people of the children of Israel [are] more and mightier than we.
10 Ku zo, mu yi dabara a kansu, in ba haka ba za su ƙaru fiye da haka, in kuwa yaƙi ya tashi tsakaninmu da abokan gāba, za su iya haɗa kai da abokan gāba, su yaƙe mu, su bar ƙasar.”
Come, let us deal wisely with them: lest they multiply, and it shall come to pass, that when there falleth out any war, they will join with our enemies, and fight against us, and depart from the land.
11 Saboda haka sai suka naɗa shugabannin gandu a kansu don su wahalshe su, su kuma bauta musu, suka sa su suka gina biranen Fitom da Rameses su zama biranen ajiya, domin Fir’auna.
Therefore they set over them task-masters, to afflict them with their burdens. And they built for Pharaoh treasure-cities, Pithom, and Raamses.
12 Amma duk da wannan ƙarin wulaƙancin da ake yi musu, su kuwa sai daɗa riɓaɓɓanya suke ta yi. Sai tsoron Isra’ilawa ya ƙaru a zuciyar Masarawa,
But the more they afflicted them, the more they multiplied and grew. And they were grieved because of the children of Israel.
13 ganin haka sai Masarawa suka ƙara musu wahala.
And the Egyptians made the children of Israel to serve with rigor.
14 Suka baƙanta wa Isra’ilawa rai da bauta mai wuya, ta wurin sa su yin tubali da yumɓu, da kuma kowace irin bauta a gonaki. A cikin dukan ayyukansu, Masarawa ba su ji tausayinsu ba ko kaɗan.
And they made their lives bitter with hard bondage, in mortar, and in brick, and in all manner of service in the field: all their service in which they made them serve, [was] with rigor.
15 Sai Sarkin Masar ya gaya wa ungozomomin matan Ibraniyawa, wato, su Shofra da Fuwa ya ce,
And the king of Egypt spoke to the Hebrew midwives (of which the name of one [was] Shiphrah, and the name of the other Puah: )
16 “Sa’ad da kuke taimakon matan Ibraniyawa lokacin haihuwa, in jaririn namiji ne ku kashe shi, amma in ta mace ce, ku bar ta da rai.”
And he said, When ye do the office of a midwife to the Hebrew women, and see [them] upon the stools; if it [shall be] a son, then ye shall kill him; but if it [shall be] a daughter, then she shall live.
17 Amma ungozomomin nan masu tsoron Allah ne, ba su kuwa aikata abin da sarkin Masar ya gaya musu ba; suka bar jarirai maza su rayu.
But the midwives feared God, and did not as the king of Egypt commanded them, but saved the male-children alive.
18 Sai sarkin Masar ya kira ungozomomin, ya tambaye su ya ce, “Don me kuka yi haka? Don me kuka bar jarirai maza su rayu?”
And the king of Egypt called for the midwives, and said to them, Why have ye done this thing, and have saved the male-children alive?
19 Ungozoman suka amsa wa Fir’auna suka ce, “Ai, matan Ibraniyawa ba kamar matan Masarawa ba ne, gwarzaye ne, sukan haihu kafin ungozomomin su kai wurinsu.”
And the midwives said to Pharaoh, Because the Hebrew women [are] not as the Egyptian women: for they [are] lively, and are delivered ere the midwives come in to them.
20 Saboda haka Allah ya nuna alheri wa ungozomomin, Isra’ilawa kuwa suka yi yawa fiye da dā.
Therefore God dealt well with the midwives: and the people multiplied, and became very mighty.
21 Saboda ungozomomin suna tsoron Allah, sai Allah ya ba su iyalan kansu.
And it came to pass, because the midwives feared God, that he made them houses.
22 Sai Fir’auna ya ba da umarni wa mutanensa ya ce, “Duk yaron da yake namijin da haka haifa, dole ku jefa shi cikin kogi, amma ku bar yara mata su rayu.”
And Pharaoh charged all his people, saying, Every son that is born ye shall cast into the river, and every daughter ye shall save alive.

< Fitowa 1 >