< Fitowa 20 >

1 Sai Allah ya faɗi waɗannan kalmomi ya ce,
Alors, le Seigneur prononça tous les discours qui suivent, et il dit:
2 “Ni ne Ubangiji Allahnka, wanda ya fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta.
Je suis le Seigneur ton Dieu, qui t'ai tiré de la terre d'Égypte, de la maison de servitude.
3 “Ba za ka yi wa kanka waɗansu alloli ba sai ni.
Tu n'auras point d'autres dieux que moi.
4 Ba za ka yi wa kanka waɗansu alloli a siffar wani abu a sama a bisa, ko a ƙarƙashin ƙasa, ko a ƙarƙashin ruwa ba.
Tu ne te feras pas d'idoles ni d'images d'aucune chose existant au ciel, sur la terre, sous la terre et dans les eaux.
5 Ba za ka durƙusa gare su, ko ka yi musu sujada ba. Gama ni, Ubangiji Allahnka mai kishi ne, nakan hukunta’ya’ya har tsara ta uku da ta huɗu na waɗanda suke ƙina,
Tu ne les adoreras point, tu ne les serviras pas; car je suis le Seigneur ton Dieu, Dieu jaloux, vengeant sur les enfants les péchés des pères, jusqu'à la troisième et à la quatrième génération de ceux qui me haïssent,
6 amma ina nuna ƙauna ga tsara dubbai na waɗanda suke ƙaunata, suke kuma kiyaye umarnaina.
Et faisant miséricorde, pendant des milliers de générations, à ceux qui m'aiment et qui observent mes commandements.
7 Ba za ka yi amfani da sunan Ubangiji Allahnka a banza ba, gama Ubangiji zai hukunta duk wanda ya mai da sunansa banza.
Tu ne prendras pas en vain le nom du Seigneur ton Dieu; car le Seigneur, ton Dieu, ne regardera point comme pur celui qui aura pris son nom en vain.
8 Ka tuna da ranar Asabbaci domin ka kiyaye ta da tsarki.
Souviens-toi de sanctifier le jour du sabbat.
9 Kwana shida za ka yi dukan aikinka,
Pendant six jours travaille et fais tous tes ouvrages.
10 amma rana ta bakwai Asabbaci ne ga Ubangiji, Allahnka. A ranar ba za ka yi wani aiki ba, ko kai, ko ɗanka, ko’yarka, ko bawa, ko baiwa, ko dabbarka, ko baƙon da yake zama tare da kai.
Mais le septième jour est le sabbat (repos) du Seigneur ton Dieu; tu ne feras aucune œuvre en ce jour-là: ni toi, ni ton fils, ni ta fille, ni ton serviteur, ni ta servante, ni ton bœuf, ni ton âne, ni aucune de tes bêtes, ni le prosélyte demeurant avec toi.
11 Gama kwana shida Ubangiji ya halicci sama da ƙasa, da teku, da duk abin da yake cikinsu, amma ya huta a rana ta bakwai. Saboda haka Ubangiji ya albarkaci ranar Asabbaci, ya kuma mai da ita mai tsarki.
Car, en six jours, le Seigneur a créé le ciel, et la terre, et la mer, et tout ce qu'ils contiennent, et il s'est reposé le septième jour; c'est pourquoi Dieu a béni le septième jour, et l’a sanctifié.
12 Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, domin ka yi tsawon rai a ƙasar da Ubangiji Allahnka yake ba ka.
Honore ton père et ta mère, afin que tu sois heureux et que tu vives longtemps sur la terre fortunée que te donnera le Seigneur ton Dieu.
13 Ba za ka yi kisankai ba.
Tu ne seras point adultère.
14 Ba za ka yi zina ba.
Tu ne voleras point.
15 Ba za ka yi sata ba.
Tu ne tueras point.
16 Ba za ka ba da shaidar ƙarya a kan maƙwabcinka ba.
Tu ne porteras point de faux témoignage contre ton prochain.
17 Ba za ka yi ƙyashin gidan maƙwabcinka ba. Ba za ka yi ƙyashin matar maƙwabcinka ba, ko bawansa, ko baiwarsa, ko sansa, ko jakinsa, ko duk abin da yake na maƙwabcinka ba.”
Tu ne convoiteras point la femme de ton prochain; tu ne convoiteras point la maison de ton prochain, ni son champ, ni son serviteur, ni sa servante, ni son bœuf, ni son âne, ni une seule de ses bêtes, ni rien de ce qui est à ton prochain.
18 Da mutane suka ga tsawa da walƙiya, suka ji karar ƙaho, suka kuma ga dutsen yana hayaƙi, sai suka yi rawar jiki don tsoro. Suka tsaya da nisa
Tout le peuple entendait la voix et le son des trompettes, il voyait les lueurs et la montagne fumante; et, frappé de terreur, tout le peuple se tenait au loin.
19 suka ce wa Musa, “Ka yi magana da mu da kanka, za mu kasa kunne. Amma kada Allah ya yi mana magana, don kada mu mutu.”
Et ils dirent à Moise, parle-nous, toi; que le Seigneur cesse de nous parler, de peur que nous ne mourions.
20 Musa ya ce wa mutane, “Kada ku ji tsoro, gama Allah ya zo don yă gwada ku, don ku riƙa girmama shi, don kuma kada ku yi zunubi.”
Et Moïse leur répondit: Rassurez-vous; c'est pour vous éprouver que Dieu est venu, afin que la crainte de Dieu soit en vous, et que vous ne péchiez pas.
21 Sa’ad da mutane suka tsattsaya da nesa, sai Musa ya matsa kusa da girgije mai duhu, inda Allah yake.
Tandis que le peuple d'Israël se tenait au loin, Moïse entra dans la nuée sombre où était Dieu.
22 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka faɗa wa Isra’ilawa wannan. ‘Kun gani da kanku cewa na yi magana da ku daga sama.
Et le Seigneur dit à Moïse: Voici ce que tu diras à la maison de Jacob, ce que tu déclareras aux fils d'Israël: Vous avez vu vous-mêmes que du ciel je vous ai parlé;
23 Kada ku yi waɗansu alloli in ban da ni, kada ku yi wa kanku allolin azurfa ko na zinariya.
Vous ne vous ferez pas de dieux d'argent, vous ne ferez point pour vous de dieux d'or.
24 “‘Ku yi mini bagaden ƙasa, ku kuma miƙa mini hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama, za ku hadayar da tumakinku da awakinku da shanu. Duk inda na sa a girmama sunana, zan zo wurinku, in sa muku albarka.
Vous ferez un autel de terre, et vous y sacrifierez vos holocaustes et vos hosties pacifiques, brebis ou génisses, en tout lieu où j'imposerai mon nom; et je viendrai vers toi, et je te bénirai.
25 In kuka yi mini bagade dutse, kada ku gina shi da sassaƙaƙƙun duwatsu, gama inda guduma ta taɓa duwatsun, sun haramtu ke nan.
Et, si tu me bâtis un autel en pierres, tu les emploieras sans les tailler, car tu les profanerais en portant le ciseau sur elles.
26 Kada ku gina wa bagadena matakala, domin kada yayinda wani yana hawa, mutane su ga tsiraicinsa.’
Tu ne monteras pas par des degrés à mon autel, de peur qu'après de l'autel tu ne sois découvert indécemment.

< Fitowa 20 >