< Fitowa 9 >

1 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka je wurin Fir’auna ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Allah na Ibraniyawa ya ce, “Ka bar mutanena su tafi, domin su yi mini sujada.”
Then the LORD said to Moses, Go in to Pharaoh, and tell him, Thus saith the LORD God of the Hebrews, Let my people go, that they may serve me.
2 In ka ƙi ka bar su su tafi, kana ta riƙonsu,
For if thou shalt refuse to let [them] go, and wilt hold them still,
3 hannun Ubangiji zai kawo muguwar annoba a kan dabbobinka a gona, a kan dawakanka, da jakuna da raƙuma, da kuma a kan shanunka da tumaki da awaki.
Behold, the hand of the LORD is upon thy cattle which are in the field, upon the horses, upon the asses, upon the camels, upon the oxen, and upon the sheep: [there shall be] a very grievous murrain.
4 Amma Ubangiji zai raba tsakanin dabbobin Isra’ila da na Masar, saboda kada wata dabbar Isra’ilawa ta mutu.’”
And the LORD shall sever between the cattle of Israel, and the cattle of Egypt: and there shall nothing die of all [that] belongs to the children of Israel.
5 Sai Ubangiji ya sa lokaci ya ce, “Gobe Ubangiji zai yi wannan a ƙasar.”
And the LORD appointed a set time, saying, To-morrow the LORD will do this thing in the land.
6 Kashegari Ubangiji ya yi haka. Dukan dabbobin Masarawa suka mutu, amma babu dabba guda ta Isra’ilawan da ta mutu.
And the LORD did that thing on the morrow, and all the cattle of Egypt died: but of the cattle of the children of Israel died not one.
7 Fir’auna ya aiki mutane su bincika, sai suka tarar babu dabba guda ta Isra’ilawan da ta mutu. Duk da haka zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa bar mutanen su tafi ba.
And Pharaoh sent, and behold, there was not one of the cattle of the Israelites dead. And the heart of Pharaoh was hardened, and he did not let the people go.
8 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna, “Ɗibi tokar matoya cike da tafin hannuwanku, Musa kuwa zai watsa tokar sama a gaban Fir’auna.
And the LORD said to Moses and to Aaron, Take to you handfuls of ashes of the furnace, and let Moses sprinkle it towards heaven in the sight of Pharaoh.
9 Za tă zama ƙura bisa dukan ƙasar Masar, sai marurai masu zafi su fiffito bisa mutane da dabbobi a dukan ƙasar.”
And it shall become small dust in all the land of Egypt, and shall be a boil breaking forth [with] blains upon man, and upon beast, throughout all the land of Egypt.
10 Sai suka ɗibi tokar matoya, suka tsaya a gaban Fir’auna, Musa ya watsa ta a iska, sai marurai masu zafi suka fiffito bisa mutane da dabbobi.
And they took ashes of the furnace, and stood before Pharaoh; and Moses sprinkled it towards heaven; and it became a boil breaking forth [with] blains upon man, and upon beast.
11 Bokaye suka kāsa tsayawa a gaban Musa saboda maruran da suke bisansu da a kan dukan Masarawa.
And the magicians could not stand before Moses, because of the boil: for the boil was upon the magicians, and upon all the Egyptians.
12 Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa saurare Musa da Haruna ba kamar yadda Ubangiji ya riga ya ce wa Musa.
And the LORD hardened the heart of Pharaoh, and he hearkened not to them; as the LORD had spoke to Moses.
13 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Tashi da sassafe, ka sadu da Fir’auna, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Ibraniyawa ya ce, Ka bar mutanena su tafi don su yi mini sujada,
And the LORD said to Moses, Rise early in the morning, and stand before Pharaoh, and say to him, Thus saith the LORD God of the Hebrews, Let my people go, that they may serve me.
14 ko kuwa a wannan lokaci zan aika da cikakkiyar annoba mai ƙarfi a kanka da a kan fadawanka da mutanenka, domin ka san cewa ba kama da ni a dukan duniya.
For I will at this time send all my plagues upon thy heart, and upon thy servants, and upon thy people: that thou mayest know that [there is] none like me in all the earth.
15 Gama da ni kaina na miƙa hannuna na buge ka da jama’arka da annoba, ai, da an hallaka ku a duniya ƙaƙaf.
For now I will stretch out my hand, that I may smite thee and thy people with pestilence; and thou shalt be cut off from the earth.
16 Amma na bar ka ka rayu domin in nuna maka ikona, domin kuma sunana yă zama abin darajantawa a dukan duniya.
And in very deed for this [cause] have I raised thee up, to show [in] thee my power; and that my name may be declared throughout all the earth.
17 Har yanzu kana gāba da mutanena, ba ka kuma bar su su tafi ba.
As yet dost thou exalt thyself against my people, that thou wilt not let them go?
18 Saboda haka, gobe war haka, zan sa a yi ƙanƙara mai tsananin gaske, irin wadda Masar ba tă taɓa gani ba tun kahuwarta, har yă zuwa yanzu.
Behold, to-morrow about this time I will cause it to rain a very grievous hail, such as hath not been in Egypt since its foundation even until now.
19 Yanzu, ka ba da umarni a dawo da shanunku da kuma kome da kuke da shi wanda yake a gona zuwa gida, gama ƙanƙarar za tă kashe kowane mutum ko dabba wadda take a gona wadda ba a kawo cikin gida ba, sa’ad da ta fāɗo.’”
Send therefore now, [and] gather thy cattle, and all that thou hast in the field: [for upon] every man and beast which shall be found in the field, and shall not be brought home, the hail shall come down upon them, and they shall die.
20 Waɗansu daga cikin dattawan Fir’auna suka cika da tsoro saboda abin da Ubangiji ya faɗa, nan da nan suka shigo da dabbobinsu da bayinsu da sauri daga gona zuwa cikin gida.
He that feared the word of the LORD, among the servants of Pharaoh, made his servants and his cattle flee into the houses:
21 Amma waɗanda ba su kula da maganar Ubangiji ba, suka bar bayinsu da dabbobi a gona.
And he that regarded not the word of the LORD, left his servants and his cattle in the field.
22 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka sama don a yi ƙanƙara a bisa dukan Masar, a bisa mutane da dabbobi, da bisa dukan abubuwan da suke girma a gonakin Masar.”
And the LORD said to Moses, Stretch forth thy hand towards heaven, that there may be hail in all the land of Egypt, upon man, and upon beast, and upon every herb of the field, throughout the land of Egypt.
23 Da Musa ya miƙa sandansa sama, sai Ubangiji ya aiko da tsawa da ƙanƙara, da walƙiya har ƙasa. Ta haka Ubangiji ya yi ruwan ƙanƙara a bisa ƙasar Masar;
And Moses stretched forth his rod towards heaven, and the LORD sent thunder and hail, and the fire ran along upon the ground: and the LORD rained hail upon the land of Egypt.
24 ƙanƙara ta fāɗo, walƙiya kuma tana ta wulƙawa. Wannan ce ƙanƙara mafi munin da aka taɓa yi, a dukan ƙasar Masar, tun tarihin kahuwarta na zaman al’umma.
So there was hail, and fire mingled with the hail, very grievous, such as there had been none like it in all the land of Egypt, since it became a nation.
25 Ko’ina a Masar ƙanƙara ta bugi duk abin da yake a gonaki, mutane da dabbobi, ta bugi duk ganyaye da suke a gonaki, ta kuma ragargaza kowane itace.
And the hail smote, throughout all the land of Egypt, all that [was] in the field, both man and beast, and the hail smote every herb of the field and broke every tree of the field.
26 Wuri guda kaɗai da ba a yi ruwan ƙanƙara ba, shi ne yankin Goshen, inda Isra’ilawa suke.
Only in the land of Goshen, where the children of Israel [were], there was no hail.
27 Sai Fir’auna ya aika a kira Musa da Haruna. Ya ce musu, “A wannan karo na yi zunubi. Ubangiji, shi ne da gaskiya, ni da mutane mu ke da kuskure.
And Pharaoh sent, and called for Moses and Aaron, and said to them, I have sinned this time: the LORD [is] righteous, and I and my people [are] wicked.
28 Ku roƙi Ubangiji, yă tsai da tsawar da ƙanƙarar. Ni kuwa na yi alkawari zan bar ku ku tafi, ba za ku ƙara tsayawa a nan ba.”
Entreat the LORD (for [it is] enough) that there be no [more] mighty thunderings and hail; and I will let you go, and ye shall stay no longer.
29 Musa ya amsa, “To, da kyau, da zarar na fita daga birnin, zan yi addu’a ga Ubangiji, tsawar za tă tsaya, ƙanƙarar kuma za tă daina, don ku sani cewa duniya ta Ubangiji ce.
And Moses said to him, As soon as I am gone out of the city, I will spread abroad my hands to the LORD; [and] the thunder shall cease, neither shall there be any more hail; that thou mayest know how that the earth [is] the LORD'S.
30 Amma na san cewa kai da fadawanka, har wa yau ba ku ji tsoron Ubangiji Allah ba tukuna.”
But as for thee and thy servants, I know that ye will not yet fear the LORD God.
31 (Rama da sha’ir suka lalace, gama sha’ir ya riga ya nuna, rama kuwa tana fid da kai.
And the flax and the barley were smitten: for the barley [was] in the ear, and the flax [was] bolled.
32 Alkama da gero kam, ba a hallaka su ba, gama lokacin nunansu bai yi ba tukuna.)
But the wheat and the rye were not smitten; for they [were] not grown up.
33 Sai Musa ya tashi daga gaban Fir’auna, ya fita daga birni. Da ya miƙa hannuwansa ta wajen Ubangiji, sai tsawa da ƙanƙara suka tsaya, kwararowar ruwa kuma ta ɗauke.
And Moses went out of the city from Pharaoh, and spread abroad his hands to the LORD: and the thunders and hail ceased, and the rain was not poured upon the earth.
34 Da Fir’auna ya ga cewa ruwa da ƙanƙara da tsawa sun daina, sai ya sāke yin zunubi. Shi da fadawansa, suka taurare zukatansu.
And when Pharaoh saw that the rain and the hail and the thunders had ceased, he sinned yet more, and hardened his heart, he and his servants.
35 Ta haka zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa bar Isra’ilawa suka tafi ba, kamar yadda Ubangiji ya riga ya faɗa ta wurin Musa.
And the heart of Pharaoh was hardened, neither would he let the children of Israel go; as the LORD had spoken by Moses.

< Fitowa 9 >