< Ezekiyel 17 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of the LORD came to me, saying,
2 “Ɗan mutum, ka shirya kacici-kacici ka faɗa wa gidan Isra’ila misali.
Son of man, put forth a riddle, and speak a parable to the house of Israel;
3 Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa babbar gaggafa mai manyan fikafikai, dogayen gasusuwa da gasusuwa da yawa masu launi iri-iri ta zo Lebanon. Ta cire kan al’ul,
And say, Thus saith the Lord GOD; A great eagle with great wings, long-winged, full of feathers, which had divers colors, came to Lebanon, and took the highest branch of the cedar:
4 ta karya kan tohonsa da yake can bisansa ta kai ƙasar ciniki, inda ta shuka shi a birnin’yan kasuwa.
He cropped off the top of its young twigs, and carried it into a land of traffick; he set it in a city of merchants.
5 “‘Ta ɗebi waɗansu irin ƙasarku ta sa a ƙasa mai taƙi. Ta shuka shi kamar itacen wardi kusa da ruwa mai yawa,
He took also of the seed of the land, and planted it in a fruitful field; he placed [it] by great waters, [and] set it [as] a willow tree.
6 ya kuwa yi toho ya zama kuringa gajeruwa mai yaɗuwa. Rassanta suka tanƙwasa wajen gaggafar, amma saiwoyinta suka zauna a ƙarƙashinta. Ta haka ta zama kuringa, ta yi rassa ta kuma fid da ganyaye.
And it grew, and became a spreading vine of low stature, whose branches turned towards him, and its roots were under him: so it became a vine, and brought forth branches, and shot forth sprigs.
7 “‘Akwai kuma wata babbar gaggafa mai manyan fikafikai da gashi mai yawa. Kuringan nan ta tanƙwasa saiwoyinta zuwa wajen wannan gaggafa daga inda aka shuka ta, ta kuma miƙe rassanta wajenta don gaggafar ta yi mata banruwa.
There was also another great eagle with great wings and many feathers: and behold, this vine did bend her roots towards him, and shot forth her branches towards him, that he might water it by the furrows of her plantation.
8 An shuka ta a ƙasa mai kyau kusa da ruwa mai yawa don tă yi rassa masu yawa, ta ba da’ya’ya ta kuma zama kuringa mai daraja.’
It was planted in a good soil by great waters, that it might bring forth branches, and that it might bear fruit, that it might be a goodly vine.
9 “Ka gaya musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wannan za tă ci gaba? Ba za a tumɓuke ta a kuma kakkaɓe’ya’yanta don ta bushe ba? Dukan sababbin tohonta za su bushe. Ba sai da hannu mai ƙarfi, ko kuwa da yawan mutane za a tumɓuke ta daga saiwoyinta ba.
Say thou, Thus saith the Lord GOD; Shall it prosper? shall he not pull up its roots, and cut off its fruit, that it may wither? it shall wither in all the leaves of her spring, even without great power or many people to pluck it up by its roots.
10 Ko da an sāke shuka ta, za tă yi amfani ne? Ba za tă bushe gaba ɗaya sa’ad da iskar gabas ta hura ba, tă bushe a ƙasar da ta yi girma?’”
Yes, behold, [being] planted, shall it prosper? shall it not utterly wither, when the east wind toucheth it? it shall wither in the furrows where it grew.
11 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Moreover the word of the LORD came to me, saying,
12 “Ka faɗa wa gidan’yan tawayen nan, ‘Ba ka san abin da waɗannan abubuwa suke nufi ba?’ Ka faɗa musu cewa, ‘Sarkin Babilon ya tafi Urushalima ya tafi da sarkinta da kuma manyan garinta, ya dawo da su Babilon.
Say now to the rebellious house, Know ye not what these [things mean]? tell [them], Behold, the king of Babylon hath come to Jerusalem, and hath taken its king, and its princes, and led them with him to Babylon;
13 Sa’an nan ya ɗauki wani daga iyalin sarauta ya yi yarjejjeniya da shi, ya sa shi ya yi rantsuwa. Ya kuma tafi da shugabannin ƙasar,
And hath taken of the king's seed, and made a covenant with him, and hath taken an oath from him: he hath also taken the mighty of the land:
14 don a raunana masarautar, kada tă ƙara tashi, amma ta tsaya dai kan cika yarjejjeniyarsa.
That the kingdom might be base, that it might not lift itself up, [but] that by keeping his covenant it might stand.
15 Amma sarkin nan ya yi tawaye a kan sarkin Babilon ta wurin aika jakadunsa zuwa Masar don a ba shi dawakai da sojoji masu yawa. Zai ci nasara? Shi da ya yi wannan abu zai tsira? Zai iya taka yarjejjeniya har ya tsere?
But he rebelled against him in sending his embassadors into Egypt, that they might give him horses and many people. Shall he prosper? shall he escape that doeth such [things]? or shall he break the covenant, and be delivered?
16 “‘Muddin in raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zai mutu a Babilon, a ƙasar sarkin nan da ya naɗa shi, domin bai cika rantsuwa da alkawarin da ya yi ba.
[As] I live, saith the Lord GOD, surely in the place [where] the king [dwelleth] that made him king, whose oath he despised, and whose covenant he broke, [even] with him in the midst of Babylon he shall die.
17 Fir’auna da yawan sojojinsa da kuma yawan jama’arsa ba zai zama da taimako gare shi a yaƙi ba, sa’ad da sarkin Babilon zai gina mahaurai ya kuma yi ƙawanya don yă hallaka rayuka masu yawa.
Neither shall Pharaoh with [his] mighty army and great company make for him in the war, by casting up mounts, and building forts, to cut off many persons:
18 Bai cika rantsuwa ba ta wurin take alkawari. Domin sarkin Isra’ila ya ƙulla alkawari ya kuma aikata dukan waɗannan abubuwa, ba zai tsira ba.
Seeing he despised the oath by breaking the covenant, when lo, he had given his hand, and hath done all these [things], he shall not escape.
19 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce muddin ina raye, zan nemi hakkin rantsuwata da ya ƙi cikawa da kuma alkawarin da ya take.
Therefore thus saith the Lord GOD; [As] I live, surely my oath that he hath despised, and my covenant that he hath broken, even that will I recompense upon his own head.
20 Zan kafa masa tarkona, zai kuma fāɗi a tarkona. Zan kawo shi a Babilon in kuma hukunta shi a can domin ya yi mini rashin aminci.
And I will spread my net upon him, and he shall be taken in my snare, and I will bring him to Babylon, and will plead with him there for his trespass that he hath trespassed against me.
21 Dukan sojojinsa zaɓaɓɓu za a kashe su da takobi, za a kuma watsar da waɗanda suka ragu ko’ina. Ta haka za ku san cewa Ni Ubangiji na faɗa.
And all his fugitives with all his bands shall fall by the sword, and they that remain shall be scattered towards all winds: and ye shall know that I the LORD have spoken [it].
22 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ni kaina zan cire toho a kan itacen al’ul da yake can bisa in shuka; zan kuma karya ƙanƙanin reshe daga can bisan tohon in shuka a dutse mai tsayi.
Thus saith the Lord God, I will also take of the highest branch of the high cedar, and will set [it]; I will crop off from the top of its young twigs a tender one, and will plant [it] upon a high mountain and eminent:
23 A ƙwanƙolin dutsen Isra’ila zan shuka shi; zai yi rassa yă ba da’ya’ya yă kuma zama al’ul mai daraja. Tsuntsaye iri-iri za su yi sheƙa a cikinsa; za su sami mafaka a inuwar rassansa.
In the mountain of the hight of Israel will I plant it: and it shall bring forth boughs, and bear fruit, and be a goodly cedar: and under it shall dwell all fowl of every wing; in the shade of its branches shall they dwell.
24 Dukan itatuwan jeji za su san cewa Ni Ubangiji ne mai sa manyan itatuwa su zama ƙanana in kuma sa ƙananan itatuwa su zama manya. Nakan sa ɗanyen itace ya bushe, busasshen itace kuma ya zama ɗanye. “‘Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.’”
And all the trees of the field shall know that I the LORD have brought down the high tree, have exalted the low tree, have dried up the green tree, and have made the dry tree to flourish: I the LORD have spoken and have done [it].

< Ezekiyel 17 >