< Ezra 10 >

1 Yayinda Ezra yake addu’a, yake kuma furta laifi, yana kuka, yana a durƙushe da kansa ƙasa a gaban gidan Allah, sai babban taron jama’ar Isra’ilawa, maza, mata da yara, suka taru a wurinsa. Su ma suka yi kuka mai zafi.
And just as was praying Ezra and just as was confessing he weeping and prostrating himself before [the] house of God they gathered to him from Israel a company great very men and women and children for they wept the people great weeping.
2 Sai Shekaniya ɗan Yehiyel, daga zuriyar Elam ya ce wa Ezra, “Mun yi wa Allah rashin aminci ta wurin yin auratayya da maƙwabtanmu, amma duk da haka bai yashe mutanen Isra’ila ba.
And he answered Shecaniah [the] son of Jehiel one of [the] descendants of (Elam *Q(K)*) and he said to Ezra we we have acted unfaithfully against God our and we have married women foreign from [the] peoples of the land and now there [is] hope for Israel on this.
3 Yanzu bari mu yi alkawari da Allahnmu, mu kori matan da yaransu bisa ga abin da ranka yă daɗe da sauran shugabannin da kuke girmama umarnin Allah kuka shawarce mu, bari mu yi haka bisa ga doka.
And therefore let us make a covenant to God our to send out all wives and those born from them by [the] counsel of [the] Lord and the [people] trembling at [the] commandment of God our and according to the law let it be done.
4 Sai ka tashi, gama wannan hakkinka ne, za mu ba ka goyon baya. Saboda haka ka yi ƙarfin hali ka aikata shi.”
Arise for [is] on you the matter and we [will be] with you be strong and act.
5 Sai Ezra ya tashi ya sa firistoci da suke shugabanni, da Lawiyawa, da dukan mutanen Isra’ila su rantse, cewa za su yi abin da aka ce. Sai suka yi rantsuwar.
And he arose Ezra and he made to swear an oath [the] leaders of the priests the Levites and all Israel to do according to the manner this and they swore [the] oath.
6 Sa’an nan Ezra ya tashi daga gidan Allah ya tafi gidan Yehohanan ɗan Eliyashib, a can ma bai ci wani abu ba, bai sha ruwa ba domin ya ci gaba da yin baƙin cikin rashin aminci na waɗanda suka dawo daga bauta.
And he arose Ezra from to before [the] house of God and he went into [the] room of Jehohanan [the] son of Eliashib and he went there food not he ate and water not he drank for [he was] mourning on [the] unfaithfulness of the exile[s].
7 Aka yi shela a duk fāɗin Yahuda da Urushalima cewa dukan waɗanda suka dawo daga bauta su tattaru a Urushalima.
And they caused to pass a proclamation in Judah and Jerusalem to all [the] children of the exile to assemble Jerusalem.
8 Duk wanda bai zo a cikin kwana uku ba, za a washe shi, a kuma ware shi daga jama’ar da suka dawo daga bauta. Haka shugabanni da dattawa suka zartar.
And every [one] who not he will come to [the] three the days according to [the] counsel of the leaders and the elders it will be forfeited all property his and he he will be separated from [the] assembly of the exile[s].
9 A cikin kwana uku duk mutanen Yahuda da na Benyamin suka taru a Urushalima. A ranar ashirin ga watan tara, dukan mutanen suka zauna a dandali a gaban gidan Allah cike da ɓacin rai saboda abin da ya faru da kuma ruwan da aka yi.
And they assembled all [the] people of Judah and Benjamin - Jerusalem to [the] three the days it [was the] month ninth on [day] twenty in the month and they sat all the people in [the] open place of [the] house of God trembling on the matter and from the rains.
10 Sai Ezra firist ya miƙe tsaye ya yi musu magana ya ce, “Kun yi rashin aminci; kun aure mata baƙi, ta haka kuka ƙara kan zunubin Isra’ila.
And he arose Ezra the priest and he said to them you you have acted unfaithfully and you have married women foreign to add to [the] guilt of Israel.
11 Yanzu sai ku furta zunubanku ga Ubangiji, Allahn kakanninku, ku kuma yi nufinsa. Ku raba kanku da mutanen da suke kewaye da ku, ku kuma rabu da baƙin mata.”
And therefore give praise to Yahweh [the] God of ancestors your and do will his and separate yourselves from [the] peoples of the land and from the women foreign.
12 Mutanen kuwa suka tā da murya da ƙarfi suka ce, “Gaskiya ka faɗa, dole mu yi yadda ka ce,
And they answered all the assembly and they said a voice great so (according to word your *Q(K)*) on us to do.
13 Amma akwai mutane da yawa, kuma lokacin damina ne; saboda haka ba za mu iya tsayawa a waje ba. Ban da haka ma, aikin nan ba na kwana ɗaya ko biyu ba ne, domin ba ƙaramin laifi muka yi ba.
But the people [is] numerous and the time [is] rains and there not [is] ability to stand on the outside and the business not [belongs] to a day one and not to two for we have increased to transgress in the matter this.
14 Bari shugabanninmu su yi wani abu a madadin mutane duka, sa’an nan sai duk wanda ya san ya auri baƙuwar mace a garuruwanmu, sai yă zo nan a lokacin da aka shirya tare da dattawa da alƙalan kowane gari, har sai Allah ya huce fushinsa mai zafi da yake kanmu.”
Let them stand please leaders our for all the assembly and every [one] - who [is] in cities our who he has married women foreign let him come to times appointed and with them [the] elders of a city and a city and judges its until turn back [the] burning of [the] anger of God our from us until to the matter this.
15 Yonatan ɗan Asahel, da Yazehiya ɗan Tikba su ne kaɗai ba su yarda da wannan shirin ba, sai Meshullam da Shabbetai Balawe kuma suka goyi bayansu.
Only Jonathan [the] son of Asahel and Jahzeiah [the] son of Tikvah they stood on this and Meshullam and Shabbethai the Levite[s] they supported them.
16 Sai waɗanda suka dawo daga bauta suka yi yadda aka zartar. Ezra firist ya zaɓi mutane waɗanda su ne shugabannin iyalai, ɗaya daga kowane sashe, aka rubuta sunan kowannensu. A ranar ɗaya ga watan goma kuwa suka zauna don su yi binciken waɗannan abubuwa.
And they did thus [the] children of the exile and they separated themselves Ezra the priest men [the] leaders of the fathers for [the] house of ancestors their and all of them by names and they sat down on day one of the month tenth to investigate the matter.
17 A rana ta farko ga watan farko, suka gama da bincike duk waɗanda suka auri baƙin mata.
And they finished with everything [the] men who they had married women foreign until day one of the month first.
18 A cikin zuriyar firistoci, ga waɗanda suka auri mata baƙi. Daga zuriyar Yeshuwa ɗan Yozadak da’yan’uwansa, akwai Ma’asehiya, da Eliyezer, da Yarib, da Gedaliya.
And it was found some of [the] sons of the priests who they had married women foreign some of [the] sons of Jeshua [the] son of Jozadak and brothers his Maaseiah and Eliezer and Jarib and Gedaliah.
19 (Su ne suka miƙa hannuwansu suka nuna sun yarda su kori matansu baƙi, kowannensu kuma ya ba da rago daga cikin garkensa don a miƙa hadaya don zunubi.)
And they gave hand their to send out wives their and [being] guilty a ram of [the] flock on guilt their.
20 Daga zuriyar Immer, akwai Hanani da Zebadiya.
And of [the] sons of Immer Hanani and Zebadiah.
21 Daga zuriyar Harim, akwai Ma’asehiya, Iliya, Shemahiya, Yehiyel da Uzziya.
And of [the] sons of Harim Maaseiah and Elijah and Shemaiah and Jehiel and Uzziah.
22 Daga zuriyar Fashhur, akwai Eliyohenai, Ma’asehiya, Ishmayel, Netanel, Yozabad da Eleyasa.
And of [the] sons of Pashhur Elioenai Maaseiah Ishmael Nethanel Jozabad and Eleasah.
23 Cikin Lawiyawa, akwai Yozabad, Shimeyi, Kelaya (wato, Kelita), Fetahahiya, Yahuda, Eliyezer.
And of the Levites Jozabad and Shimei and Kelaiah that [is] Kelita Pethahiah Judah and Eliezer.
24 Daga mawaƙa, akwai Eliyashib. Daga masu tsaron ƙofofin haikali, akwai Shallum, Telem da Uri.
And of the singers Eliashib and of the gatekeepers Shallum and Telem and Uri.
25 Ga sunayen sauran mutanen Isra’ilan da suke da wannan laifi. Daga zuriyar Farosh, akwai Ramiya, da Izziya, Malkiya, Miyamin, Eleyazar, Malkiya da Benahiya.
And of Israel of [the] sons of Parosh Ramiah and Izziah and Malkijah and Mijamin and Eleazar and Malkijah and Benaiah.
26 Daga zuriyar Elam, akwai Mattaniya, Zakariya, Yehiyel, Abdi, Yeremot, da Iliya.
And of [the] sons of Elam Mattaniah Zechariah and Jehiel and Abdi and Jeremoth and Elijah.
27 Daga iyalin Zattu, akwai Eliyohenai, Eliyashib, Mattaniya Yeremot da Zabad da Aziza.
And of [the] sons of Zattu Elioenai Eliashib Mattaniah and Jeremoth and Zabad and Aziza.
28 Daga zuriyar Bebai, akwai Yehohanan, Hananiya, Zabbai, da Atlai.
And of [the] sons of Bebai Jehohanan Hananiah Zabbai Athlai.
29 Daga zuriyar Bani, akwai Meshullam, Malluk, Adahiya, Yashub, Sheyal, da Ramot.
And of [the] sons of Bani Meshullam Malluch and Adaiah Jashub and Sheal (and Ramoth. *Q(K)*)
30 Daga zuriyar Fahat-Mowab, akwai Adna, Kelal, Benahiya, Ma’asehiya, Mattaniya, Bezalel, Binnuyi, da Manasse.
And of [the] sons of Pahath-Moab Adna and Kelal Benaiah Maaseiah Mattaniah Bezalel and Binnui and Manasseh.
31 Daga zuriyar Harim, akwai Eliyezer, Isshiya, Malkiya, Shemahiya, Simeyon,
And [the] sons of Harim Eliezer Isshiah Malkijah Shemaiah Simeon.
32 Benyamin, Malluk da Shemariya.
Benjamin Malluch Shemariah.
33 Daga zuriyar Hashum, akwai Mattenai, da Mattatta, Zabad, Elifelet, Irmai, Manasse, da Shimeyi.
Of [the] sons of Hashum Mattenai Mattattah Zabad Eliphelet Jeremai Manasseh Shimei.
34 Daga zuriyar Bani, akwai Ma’adai, Amram, Yuwel,
Of [the] sons of Bani Maadai Amram and Uel.
35 Benahiya, Bedeya, Keluhi,
Benaiah Bedeiah (Keluhi. *Q(K)*)
36 Baniya, Meremot, Eliyashib,
Vaniah Meremoth Eliashib.
37 Mattaniya, Mattenai da Ya’asu.
Mattaniah Mattenai (and Jaasai. *Q(K)*)
38 Daga zuriyar Binnuyi, akwai Shimeyi,
And Bani and Binnui Shimei.
39 Shelemiya, Natan, Adahiya,
And Shelemiah and Nathan and Adaiah.
40 Maknadebai, Shashai, Sharai,
Machnadebai Shashai Sharai.
41 Azarel, Shelemiya, da Shemariya,
Azarel and Shelemiah Shemariah.
42 Shallum da Amariya da Yusuf.
Shallum Amariah Joseph.
43 Daga zuriyar Nebo, akwai Yehiyel, Mattitiya, Zabad, Zebina, Yaddai, Yowel da Benahiya.
Of [the] sons of Nebo Jeiel Mattithiah Zabad Zebina (Jaddai *Q(K)*) and Joel Benaiah.
44 Dukan waɗannan sun auri baƙin mata, waɗansunsu suna da’ya’ya.
All these (they had taken *Q(K)*) women foreign and there [were] some of them wives and they [masc] had made children.

< Ezra 10 >