< Ishaya 3 >

1 Yanzu ka duba fa, Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, yana shirin yă ɗauke kowane tanadi da taimako daga Urushalima da Yahuda dukan tanade-tanaden abinci da kuma dukan tanade-tanaden ruwa,
For behold, the LORD, the LORD of hosts, doth take away from Jerusalem and from Judah the rod and the staff, the whole support of bread, and the whole support of water,
2 jarumi, da soja, alƙali da annabi masu duba da dattijo,
The mighty man, and the man of war, the judge, and the prophet, and the prudent, and the ancient,
3 shugaban sojojin hamsin da mutum mai makami, mai ba da shawara, gwanin sarrafa abubuwa da mai gwanintan dabo.
The captain of fifty, and the honorable man, and the counselor, and the skillful artificer, and the eloquent orator.
4 “Zan sa’yan yara su zama shugabanninsu;’yan yara kurum za su yi mulkinsu.”
And I will give children [to be] their princes, and babes shall rule over them.
5 Mutane za su zalunci juna mutum da mutum, maƙwabci da maƙwabci. Yara za su rena tsofaffi, ƙasƙantacce zai rena mai daraja.
And the people shall be oppressed, every one by another, and every one by his neighbor: the child shall behave himself proudly against the elder, and the base against the honorable.
6 Mutum zai kama ɗaya daga cikin’yan’uwansa a gidan mahaifinsa ya ce, “Kana da abin sawa, ka zama shugabanmu; wannan kango kuma yă zama a ƙarƙashinka!”
When a man shall take hold of his brother of the house of his father, [saying], Thou hast clothing, be thou our ruler, and [let] this ruin [be] under thy hand:
7 Amma a ranan nan zai tā da murya ya ce, “Ba ni ba dai. Ba ni da abinci ko abin sawa a gidana; kada ka mai da ni shugaban mutane.”
In that day shall he swear, saying, I will not be a healer; for in my house [is] neither bread nor clothing: make me not a ruler of the people.
8 Urushalima tana tangaɗi, Yahuda yana fāɗuwa; maganganunsu da ayyukansu suna gāba da Ubangiji, suna rena ɗaukakar kasancewarsa.
For Jerusalem is ruined, and Judah is fallen: because their tongue and their doings [are] against the LORD, to provoke the eyes of his glory.
9 Fuskokinsu shaidu ne a kansu; suna nuna zunubinsu a fili kamar yadda Sodom ya yi; ba sa ma ɓoye shi. Kaitonsu! Sun jawo wa kansu masifa.
The show of their countenance doth witness against them; and they declare their sin as Sodom, they hide [it] not. Woe to their soul! for they have rewarded evil to themselves.
10 Ku faɗa wa masu adalci cewa kome zai zama musu da kyau, gama za su ji daɗin aikin da hannuwansu suka yi.
Say ye to the righteous, that [it shall be] well [with him]: for they shall eat the fruit of their doings.
11 Kaiton masu mugunta! Masifa tana a kansu! Za a rama abin da hannuwansu suka yi.
Woe to the wicked! [it shall be] ill [with him]: for the reward of his hands shall be given him.
12 Matasa suna zalunta mutanena, mata suna mulki a bisansu. Ya mutanena, jagorarinku suna ɓad da ku; suna karkatar da ku daga hanya.
[As for] my people, children [are] their oppressors, and women rule over them. O my people, they who lead thee cause [thee] to err, and destroy the way of thy paths.
13 Ubangiji ya ɗauki mazauninsa a cikin ɗakin shari’a; ya tashi don yă shari’anta mutane.
The LORD standeth up to plead, and standeth to judge the people.
14 Ubangiji yana shari’a da dattawa da kuma shugabannin mutanensa, “Ku ne kuka lalace gonar inabina; ganimar talakawa suna a gidajenku.
The LORD will enter into judgment with the elders of his people, and with their princes: for ye have eaten up the vineyard; the spoil of the poor [is] in your houses.
15 Ina dalilin da kuke marmatsa mutanena kuna gurgurje fuskokin talakawa?” Ni Ubangiji Maɗaukaki na faɗa.
What mean ye [that] ye beat my people to pieces, and grind the faces of the poor? saith the LORD God of hosts.
16 Ubangiji ya ce, “Matan Sihiyona suna da girman kai, suna tafiya da wuya a miƙe, da idanu masu yaudara, suna takawa ɗaya-ɗaya a hankali, da mundaye a ƙafafunsu, suna cas-cas.
Moreover the LORD saith, Because the daughters of Zion are haughty, and walk with extended necks and wanton eyes, walking and mincing [as] they go, and making a tinkling with their feet:
17 Saboda haka Ubangiji zai kawo gyambuna a kawunan matan Sihiyona; Ubangiji zai sa a aske kawunansu, a bar su ƙwal.”
Therefore the LORD will smite with a scab the crown of the head of the daughters of Zion, and the LORD will uncover their secret parts.
18 A wannan rana Ubangiji zai ƙwace abin da suke taƙama da shi, mundayensu, ɗankwalin kansu da abin wuyansu,
In that day the LORD will take away the show of [their] tinkling ornaments [about their feet], and [their] cauls, and [their] round tires like the moon.
19 ’yan kunnensu, kwandagansu da lulluɓinsu,
The chains, and the bracelets, and the mufflers,
20 kitsonsu, sarƙar da suke sa wa damatsansu da ɗamararsu, kwalabai turare da layu,
The bonnets, and the ornaments of the legs, and the head-bands, and the tablets, and the ear-rings,
21 da ƙawanen da suka sa a yatsotsinsu da hancinsu,
The rings, and nose-jewels,
22 tufafi masu kyau, da manyan rigunansu, da mayafansu, da jakar kuɗinsu
The changeable suits of apparel, and the mantles, and the wimples, and the crisping-pins,
23 da madubi, da kuma tufafin lilin da adikai, da gyale.
The glasses, and the fine linen, and the hoods, and the vails.
24 A maimakon ƙanshi, wari ne za a ji; a maimakon abin ɗamara, igiya ce za a samu; a maimakon kyakkyawan gashi, sanƙo za su kasance da shi a kai; a maimakon tufafi masu kyau, za su sa tsummoki; a maimakon kyau, za su zama munana.
And it shall come to pass, [that] instead of sweet smell there shall be an offensive odor; and instead of a girdle a rent; and instead of well set hair baldness; and instead of a stomacher a girding of sackcloth; [and] burning instead of beauty.
25 Mazanku za su mutu ta wurin takobi, jarumawanku za su mutu a yaƙi.
Thy men shall fall by the sword, and thy mighty in the war.
26 Ƙofofin Sihiyona za su yi makoki su kuma yi kuka; za tă zama wofi, za tă zauna a ƙasa.
And her gates shall lament and mourn; and she [being] desolate, shall sit upon the ground.

< Ishaya 3 >