< Ishaya 35 >

1 Hamada da ƙeƙasasshiyar ƙasa za su yi murna; jeji zai yi farin ciki ya kuma hudo. Kamar fure,
Padang gurun dan tanah kering akan bergembira, bunga-bunga bermekaran di padang belantara.
2 zai buɗu ya hudo; zai yi farin ciki mai girma ya kuma yi sowa don farin ciki. Za a maido wa Lebanon da darajarta, darajar Karmel da Sharon; za su ga ɗaukakar Ubangiji, darajar Allahnmu.
Padang gurun berkembang dengan lebatnya, dan berdendang dengan lagu-lagu ria. Keindahannya seperti gunung Libanon, serinya seperti lembah Karmel dan Saron. Maka setiap orang akan melihat kuasa TUHAN, dan keagungan Allah kita.
3 Ku ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi, ku ƙarfafa gwiwoyin da suka gaji;
Kuatkanlah tangan yang lemah, teguhkanlah lutut yang goyah.
4 ku faɗa wa waɗanda suka karai a zukata, “Ku yi ƙarfin hali, kada ku ji tsoro; Allahnku zai zo, zai zo domin ya ɗau fansa; da ramuwar Allah zai zo don yă cece ku.”
Katakanlah kepada yang kecil hati, "Kuatkan hatimu, jangan takut, Allahmu datang untuk menghukum musuh, Ia datang menyelamatkan kamu."
5 Sa’an nan idanun makafi za su buɗe kunnuwan kurame kuma su ji.
Pada waktu itu orang buta akan dapat melihat, dan orang tuli akan dapat mendengar.
6 Sa’an nan guragu za su yi tsalle kamar barewa, bebaye kuma su yi sowa don farin ciki. Ruwa zai kwararo daga jeji rafuffuka kuma a cikin hamada.
Orang lumpuh melompat-lompat seperti rusa, orang bisu bersorak-sorak gembira. Sebab mata air memancar di padang gurun, sungai mengalir di padang belantara.
7 Yashi mai ƙuna zai zama tafki, ƙeƙasasshiyar ƙasa kuma za tă cika da maɓulɓulan rafuffuka. A mazaunin diloli, inda suka taɓa zama, ciyawa da iwa da kyauro za su yi girma.
Pasir yang panas akan menjadi kolam, tanah yang gersang menjadi sumber-sumber air. Tempat yang semula didiami anjing hutan, akan ditumbuhi gelagah dan pandan.
8 Kuma babbar hanya za tă kasance a can; za a ce ta ita Hanyar Mai Tsarki. Marasa tsarki ba za su yi tafiya a kanta ba; za tă zama domin waɗanda suka yi tafiya a wannan Hanya ce; mugaye da wawaye ba za su yi ta yawo a kanta ba.
Di sana akan ada jalan raya, "Jalan menuju keselamatan" namanya. Orang berdosa tak akan lewat di sana, orang bodoh tak akan menyesatkan orang yang melaluinya.
9 Zaki ba zai kasance a can ba, balle wani naman jeji mai faɗa ya haura kanta; ba za a same su a can ba. Amma fansassu ne kaɗai za su yi tafiya a can,
Di tempat itu tak akan ada singa, atau binatang buas lainnya. Orang-orang yang diselamatkan TUHAN akan berjalan di sana.
10 kuma fansassu na Ubangiji za su komo. Za su shiga Sihiyona da rerawa; matuƙar farin ciki zai mamaye su. Murna da farin ciki za su sha kansu, baƙin ciki kuma da nishi za su gudu.
Orang-orang yang dibebaskan TUHAN akan pulang; mereka masuk kota Yerusalem dengan sorak-sorai, wajah mereka berseri karena suka-cita abadi. Mereka akan bergembira dan bersuka ria; duka dan keluh kesah lenyaplah sudah.

< Ishaya 35 >