< Irmiya 18 >

1 Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji.
The word which came to Jeremiah from the LORD, saying,
2 “Ka gangara zuwa gidan mai ginin tukwane, a can zan ba ka saƙona.”
Arise, and go down to the potter’s house, and there I will cause thee to hear my words.
3 Sai na gangara zuwa gidan mai ginin tukwane, na gan shi yana aiki a na’urar ginin tukwanen.
Then I went down to the potter’s house, and, behold, he wrought a work on the wheels.
4 Amma tukunyar da yake ginawa ta lalace a hannuwansa, sai mai ginin tukwanen ya sāke gina wata tukunya dabam, yana gyara ta yadda ya ga dama.
And the vessel that he made of clay was marred in the hand of the potter: so he made it again another vessel, as seemed good to the potter to make [it].
5 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Then the word of the LORD came to me, saying,
6 “Ya gidan Isra’ila, ashe, ba zan yi da ku yadda mai ginin tukwanen nan yake yi ba?” In ji Ubangiji. “Kamar yumɓu a hannun mai ginin tukwane, haka kuke a hannuna, ya gidan Isra’ila.
O house of Israel, cannot I do with you as this potter? saith the LORD. Behold, as the clay [is] in the potter’s hand, so [are] ye in mine hand, O house of Israel.
7 A duk lokacin da na yi shela cewa za a tumɓuke, a kakkarya a kuma hallaka wata al’umma ko mulki,
[At what] instant I shall speak concerning a nation, and concerning a kingdom, to pluck up, and to pull down, and to destroy [it; ]
8 in wannan al’ummar da na yi wa gargaɗi ta tuba daga muguntarta, sai in janye in kuma fasa kawo mata masifar da na yi niyya aukar mata.
If that nation, against whom I have pronounced, turn from their evil, I will repent of the evil that I thought to do unto them.
9 In kuma wani lokaci na yi shela cewa za a gina wata al’umma ko mulki a kuma kafa ta,
And [at what] instant I shall speak concerning a nation, and concerning a kingdom, to build and to plant [it; ]
10 in ta yi mugunta a gabana ba tă kuwa yi mini biyayya ba, sai in janye alherin da na yi niyya in yi mata.
If it do evil in my sight, that it obey not my voice, then I will repent of the good, wherewith I said I would benefit them.
11 “Yanzu fa, sai ka faɗa wa mutanen Yahuda da waɗanda suke zaune a Urushalima, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa ga shi! Ina shirya muku masifa ina ƙirƙiro dabara a kanku. Saboda haka ku juya daga mugayen hanyoyinku, kowannenku, ku canja hanyoyinku da kuma ayyukanku.’
Now therefore go to, speak to the men of Judah, and to the inhabitants of Jerusalem, saying, Thus saith the LORD; Behold, I frame evil against you, and devise a device against you: return ye now every one from his evil way, and make your ways and your doings good.
12 Amma za su amsa su ce, ‘Ba amfani. Za mu ci gaba da shirye-shiryenmu; kowannenmu zai bi taurin muguwar zuciyarsa.’”
And they said, There is no hope: but we will walk after our own devices, and we will every one do the imagination of his evil heart.
13 Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku tattambaya a cikin al’ummai. Wa ya taɓa jin irin wannan abu? Budurwa Isra’ila ta yi mugun abu mafi banƙyama.
Therefore thus saith the LORD; Ask ye now among the heathen, who hath heard such things: the virgin of Israel hath done a very horrible thing.
14 Dusar ƙanƙarar Lebanon ta taɓa rabuwa da kan duwatsun Lebanon? Ruwan mai sanyinsa daga rafuffukansa masu nesa sun taɓa daina gudu?
Will [a man] leave the snow of Lebanon [which cometh] from the rock of the field? [or] shall the cold flowing waters that come from another place be forsaken?
15 Duk da haka mutanena sun manta da ni; sun ƙone turare wa gumaka marasa amfani, waɗanda suka sa su tuntuɓe a al’amuransu a hanyoyin dā. Sun sa suka yi tafiya a ɓarayin hanyoyi a hanyoyin da ba a gina ba.
Because my people hath forgotten me, they have burned incense to vanity, and they have caused them to stumble in their ways [from] the ancient paths, to walk in paths, [in] a way not cast up;
16 Ƙasarsu za tă zama kufai, abin reni har abada; dukan waɗanda suka wuce za su yi mamaki su kaɗa kai.
To make their land desolate, [and] a perpetual hissing; every one that passeth thereby shall be astonished, and wag his head.
17 Kamar iska daga gabas zan warwatsa su a gaban abokan gābansu; zan juya musu bayana, ba zan nuna musu fuskata ba a ranar masifarsu.”
I will scatter them as with an east wind before the enemy; I will shew them the back, and not the face, in the day of their calamity.
18 Suka ce, “Zo mu shirya wa Irmiya maƙarƙashiya; gama koyarwar doka da firist ya yi ba za tă ɓace ba, haka ma shawara daga mai hikima da kuma magana daga annabawa. Saboda haka ku zo, mu fāɗa masa da harsunanmu kada mu saurari wani abin da zai faɗa.”
Then said they, Come, and let us devise devices against Jeremiah; for the law shall not perish from the priest, nor counsel from the wise, nor the word from the prophet. Come, and let us smite him with the tongue, and let us not give heed to any of his words.
19 Ka saurare ni, ya Ubangiji ka ji abin da masu zargina suke cewa!
Give heed to me, O LORD, and hearken to the voice of them that contend with me.
20 Ya kamata a sāka wa alheri da mugunta? Duk da haka sun haƙa mini rami. Ka tuna cewa na tsaya a gabanka na kuma yi magana a madadinsu don ka janye fushinka daga gare su.
Shall evil be recompensed for good? for they have digged a pit for my soul. Remember that I stood before thee to speak good for them, [and] to turn away thy wrath from them.
21 Saboda haka ka kawo wa’ya’yansu yunwa; ka miƙa su ga ikon takobi. Bari matansu su zama marasa’ya’ya da gwauraye; bari a kashe mazansu, a kuma kashe samarinsu da takobi a yaƙi.
Therefore deliver up their children to the famine, and pour out their [blood] by the force of the sword; and let their wives be bereaved of their children, and [be] widows; and let their men be put to death; [let] their young men [be] slain by the sword in battle.
22 Bari a ji kuka daga gidajensu sa’ad da ka kawo masu hari a kansu farat ɗaya, gama sun haƙa rami don su kama ni suka kuma kafa tarko wa ƙafafuna.
Let a cry be heard from their houses, when thou shalt bring a troop suddenly upon them: for they have digged a pit to take me, and hid snares for my feet.
23 Amma Ya Ubangiji, ka san duk maƙarƙashiyarsu, na neman su kashe ni. Kada ka gafarta musu laifofinsu ko ka shafe zunubansu daga gabanka. Bari a tumɓuke su a gabanka; ka yi da su sa’ad da kake fushi.
Yet, LORD, thou knowest all their counsel against me to slay [me: ] forgive not their iniquity, neither blot out their sin from thy sight, but let them be overthrown before thee; deal [thus] with them in the time of thine anger.

< Irmiya 18 >