< Irmiya 18 >

1 Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji.
Parole adressée à Jérémie de la part de l’Eternel et conçue en ces termes:
2 “Ka gangara zuwa gidan mai ginin tukwane, a can zan ba ka saƙona.”
"Lève-toi et descends dans la maison du potier, c’est là que je te ferai entendre mes paroles."
3 Sai na gangara zuwa gidan mai ginin tukwane, na gan shi yana aiki a na’urar ginin tukwanen.
Je descendis dans la maison du potier, et voici, il était occupé à façonner l’ouvrage au tour.
4 Amma tukunyar da yake ginawa ta lalace a hannuwansa, sai mai ginin tukwanen ya sāke gina wata tukunya dabam, yana gyara ta yadda ya ga dama.
Or, quand le vase qu’il façonnait se trouvait manqué, ainsi qu’il arrive à l’argile sous la main du potier, il se mettait à en faire un nouveau vase, comme c’était le bon plaisir du potier d’agir.
5 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Alors la parole de l’Eternel me fut adressée en ces termes:
6 “Ya gidan Isra’ila, ashe, ba zan yi da ku yadda mai ginin tukwanen nan yake yi ba?” In ji Ubangiji. “Kamar yumɓu a hannun mai ginin tukwane, haka kuke a hannuna, ya gidan Isra’ila.
"Est-ce que je ne pourrai pas agir à votre égard, ô maison d’Israëldit l’Eternelà la façon de ce potier? Certes, vous êtes sous ma main comme l’argile sous la main du potier, ô maison d’Israël!
7 A duk lokacin da na yi shela cewa za a tumɓuke, a kakkarya a kuma hallaka wata al’umma ko mulki,
Tantôt j’exprime contre un peuple et un royaume la menace d’extirper, de renverser et de détruire.
8 in wannan al’ummar da na yi wa gargaɗi ta tuba daga muguntarta, sai in janye in kuma fasa kawo mata masifar da na yi niyya aukar mata.
Mais que ce peuple, ainsi menacé par moi, se repente de ses fautes, je change d’avis quant aux calamités que j’avais l’intention de lui infliger.
9 In kuma wani lokaci na yi shela cewa za a gina wata al’umma ko mulki a kuma kafa ta,
Tantôt j’énonce au sujet d’un peuple et d’un royaume la promesse de bâtir et de planter.
10 in ta yi mugunta a gabana ba tă kuwa yi mini biyayya ba, sai in janye alherin da na yi niyya in yi mata.
Mais qu’il fasse ce qui déplaît à mes yeux en refusant d’écouter ma voix, je rétracte le bien que j’avais promis de lui faire.
11 “Yanzu fa, sai ka faɗa wa mutanen Yahuda da waɗanda suke zaune a Urushalima, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa ga shi! Ina shirya muku masifa ina ƙirƙiro dabara a kanku. Saboda haka ku juya daga mugayen hanyoyinku, kowannenku, ku canja hanyoyinku da kuma ayyukanku.’
Et maintenant parle donc aux gens de Juda et aux habitants de Jérusalem en ces termes: "Voici, je prépare contre vous des malheurs et nourris contre vous des projets! Abandonnez donc tous votre mauvaise conduite et amendez vos voies et vos oeuvres!"
12 Amma za su amsa su ce, ‘Ba amfani. Za mu ci gaba da shirye-shiryenmu; kowannenmu zai bi taurin muguwar zuciyarsa.’”
Mais ils riposteront! "Peine perdue! Car nous voulons suivre nos idées, agir chacun au gré des penchants de notre coeur qui est mauvais."
13 Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku tattambaya a cikin al’ummai. Wa ya taɓa jin irin wannan abu? Budurwa Isra’ila ta yi mugun abu mafi banƙyama.
C’Est pourquoi ainsi parle l’Eternel: Interrogez donc les nations: qui a ouï pareille chose? La vierge d’Israël a commis d’horribles excès!
14 Dusar ƙanƙarar Lebanon ta taɓa rabuwa da kan duwatsun Lebanon? Ruwan mai sanyinsa daga rafuffukansa masu nesa sun taɓa daina gudu?
Est-ce que la neige du Liban disparaît des roches en plein champ? Est-ce qu’elles tarissent, les eaux venant de loin fraîches et rapides?
15 Duk da haka mutanena sun manta da ni; sun ƙone turare wa gumaka marasa amfani, waɗanda suka sa su tuntuɓe a al’amuransu a hanyoyin dā. Sun sa suka yi tafiya a ɓarayin hanyoyi a hanyoyin da ba a gina ba.
Pourtant mon peuple m’a oublié pour encenser de vaines idoles; on les a fait trébucher dans leurs vraies voies, ces routes des temps antiques, pour les amener sur d’autres routes, sur des chemins non frayés.
16 Ƙasarsu za tă zama kufai, abin reni har abada; dukan waɗanda suka wuce za su yi mamaki su kaɗa kai.
Et ainsi ils font de leur pays une désolation, un objet d’éternelles railleries: quiconque passe dans le voisinage est stupéfait et hoche la tête.
17 Kamar iska daga gabas zan warwatsa su a gaban abokan gābansu; zan juya musu bayana, ba zan nuna musu fuskata ba a ranar masifarsu.”
Tel que le vent d’est, je les disperserai devant l’ennemi; c’est de dos et non de face que je les verrai au jour de leur désastre.
18 Suka ce, “Zo mu shirya wa Irmiya maƙarƙashiya; gama koyarwar doka da firist ya yi ba za tă ɓace ba, haka ma shawara daga mai hikima da kuma magana daga annabawa. Saboda haka ku zo, mu fāɗa masa da harsunanmu kada mu saurari wani abin da zai faɗa.”
Alors ils dirent: "Allons, montons une cabale contre Jérémie; car la loi ne sera pas perdue faute de prêtre, ni l’expérience faute de sage, ni l’éloquence faute de prophète. Allons, frappons-le avec notre langue, et ne prêtons l’oreille à aucune de ses paroles."
19 Ka saurare ni, ya Ubangiji ka ji abin da masu zargina suke cewa!
Prête-moi ton oreille, ô Eternel, et entends les discours de mes adversaires.
20 Ya kamata a sāka wa alheri da mugunta? Duk da haka sun haƙa mini rami. Ka tuna cewa na tsaya a gabanka na kuma yi magana a madadinsu don ka janye fushinka daga gare su.
Le bien se paie-t-il par le mal, qu’ils aient creusé une fosse à mon intention? Rappelle-toi comme je me tenais devant toi pour plaider leur cause, en vue de détourner d’eux ta colère.
21 Saboda haka ka kawo wa’ya’yansu yunwa; ka miƙa su ga ikon takobi. Bari matansu su zama marasa’ya’ya da gwauraye; bari a kashe mazansu, a kuma kashe samarinsu da takobi a yaƙi.
Aussi, livre leurs enfants en proie à la famine, précipite-les sous le tranchant de l’épée. Que leurs femmes soient privées de leurs enfants et réduites au veuvage, les époux étant enlevés par la mort et les jeunes gens tués par le glaive dans le combat!
22 Bari a ji kuka daga gidajensu sa’ad da ka kawo masu hari a kansu farat ɗaya, gama sun haƙa rami don su kama ni suka kuma kafa tarko wa ƙafafuna.
Qu’on entende des cris d’effroi sortir de leurs maisons, quand soudain tu feras fondre sur eux des troupes armées, puisqu’ils ont creusé une fosse pour s’emparer de moi et dissimulé des pièges sous mes pas!
23 Amma Ya Ubangiji, ka san duk maƙarƙashiyarsu, na neman su kashe ni. Kada ka gafarta musu laifofinsu ko ka shafe zunubansu daga gabanka. Bari a tumɓuke su a gabanka; ka yi da su sa’ad da kake fushi.
Mais toi, ô Seigneur, tu connais toutes leurs machinations meurtrières contre moi; ne pardonne point leur crime et ne laisse pas s’effacer devant toi leur iniquité. Puissent-ils s’effondrer sous tes yeux! Sévis contre eux à l’heure de ta colère.

< Irmiya 18 >