< Yohanna 4 >

1 Yesu ya ji labari cewa Yahudawa sun ji cewa ya wuce Yohanna samun masu bi, yana kuma yin musu baftisma,
Therefore when the Lord knew that the Pharisees had heard that Jesus was gaining and baptizing more disciples than John
2 ko da yake ba Yesu ne yake baftismar ba, almajiransa ne.
(although Jesus Himself wasn’t baptizing, but His disciples were),
3 Da ya sami wannan labari, sai ya bar Yahudiya ya sāke koma Galili.
He left Judea, and went back towards Galilee.
4 To, ya zama dole yă bi ta Samariya.
He had to go through Samaria.
5 Sai ya zo wani gari a Samariya da ake ce da shi Saikar, kurkusa da filin da Yaƙub ya ba wa ɗansa Yusuf.
He came to a city of Samaria, called Sychar, near the parcel of ground that Jacob gave to his son Joseph,
6 Rijiyar Yaƙub kuwa tana can, Yesu kuwa, saboda gajiyar tafiya, sai ya zauna a bakin rijiyar. Wajen sa’a ta shida ne.
and Jacob’s well was there. Jesus therefore, being tired from His journey, sat down by the well. It was about the sixth hour.
7 Sa’ad da wata mutuniyar Samariya ta zo ɗiban ruwa, sai Yesu ya ce mata, “Ba ni ruwa in sha?”
A Samaritan woman came to draw water. Jesus said to her, “Please give me a drink.”
8 (Almajiransa kuwa sun shiga gari don sayi abinci.)
His disciples had gone into the town to buy food.
9 Sai mutuniyar Samariyar ta ce masa, “Kai mutumin Yahuda ne, ni kuwa mutuniyar Samariya ce. Yaya za ka roƙe ni ruwan sha?” (Don Yahudawa ba sa hulɗa da Samariyawa.)
The Samaritan woman therefore asked Him, “How is it that You, being a Jew, ask me for a drink, since I’m a Samaritan woman?” (For Jews have nothing to do with Samaritans.)
10 Yesu ya amsa mata ya ce, “Da kin san kyautar Allah, da kuma wanda yake roƙonki ruwan sha, da kin roƙe shi, shi kuwa da ya ba ki ruwan rai.”
Jesus answered her, “If you knew God’s gift, and who it is who says to you, ‘Please give me a drink,’ you would have asked Him, and He would have given you living water.”
11 Sai macen ta ce, “Ranka yă daɗe, ba ka da guga rijiyar kuwa tana da zurfi. Ina za ka sami wannan ruwan rai?
The woman said, “Sir, you have nothing to draw with and the well is deep. Where could you get this living water from?
12 Ka fi mahaifinmu Yaƙub ne, wanda ya ba mu rijiyar ya kuma sha daga ciki da kansa, haka ma’ya’yansa da kuma garkunan shanunsa da tumakinsa?”
Are You greater than our forefather Jacob, who gave us this well and who used to drink from it himself, as did also his sons and his flocks and herds?”
13 Yesu ya amsa ya ce, “Kowa ya sha wannan ruwa, zai sāke jin ƙishirwa,
Jesus answered her, “Everyone who drinks of this water will get thirsty again,
14 amma duk wanda ya sha ruwan da zan ba shi, ba zai ƙara jin ƙishirwa ba. Tabbatacce, ruwan da zan ba shi, zai zama masa maɓuɓɓugan ruwa da yake ɓuɓɓugowa har yă zuwa rai madawwami.” (aiōn g165, aiōnios g166)
but whoever drinks the water that I will give will never, ever get thirsty. The water that I will give will become in that person a fountain of water springing up into everlasting life.” (aiōn g165, aiōnios g166)
15 Sai macen ta ce masa, “Ranka yă daɗe, ka ba ni ruwan nan, don kada in ƙara jin ƙishirwa, in yi ta zuwa nan ɗiban ruwa.”
The woman said to him, “Sir, give me this water so that I won’t get thirsty and have to keep coming all the way here to draw water.”
16 Sai ya ce mata, “Je ki zo da mijinki.”
Jesus told her, “Go, call your husband, and come here.”
17 Sai ta amsa ta ce, “Ai, ba ni da miji.” Yesu ya ce mata, “Gaskiyarki da kika ce ba ki da miji.
The woman answered, “I have no husband.” Jesus told her, “You are right in saying, ‘I have no husband,’
18 Gaskiyar ita ce, kin auri maza biyar, wanda kuke tare yanzu kuwa ba mijinki ba ne. A nan kam kin yi gaskiya.”
for you have had five husbands, and the one you have now isn’t your husband. What you have said is quite true.”
19 Sai macen ta ce, “Ranka yă daɗe, ina gani kai annabi ne.
The woman said to Him, “Sir, I perceive that You are a prophet.
20 Kakanninmu sun yi sujada a dutsen nan, amma ku Yahudawa kun ce a Urushalima ne ya kamata a yi sujada.”
Our ancestors worshipped on this mountain, but you Jews say that the place where we must worship is in Jerusalem.”
21 Sai Yesu ya ce, “Uwargida, ina tabbatar miki, lokaci yana zuwa da ba za ku yi wa Uba sujada ko a dutsen nan, ko kuwa a Urushalima ba.
Jesus told her, “Woman, believe me, a time is coming when you will worship the Father neither in this mountain, nor in Jerusalem.
22 Ku Samariyawa ba ku san abin da kuke yi wa sujada ba; mu kuwa mun san abin da muke yi wa sujada, gama ceto daga Yahudawa yake.
You Samaritans worship what you don’t know. We worship what we know, for salvation is from the Jews.
23 Duk da haka, lokaci yana zuwa har ma ya riga ya yi, da masu sujada na gaskiya za su yi wa Uba sujada a Ruhu da kuma gaskiya, gama irin waɗannan masu sujada ne Uba yake nema.
A time is coming, and has now come, when the true worshipers will worship the Father in spirit and truth, for they are the kind of worshipers that the Father seeks.
24 Allah ruhu ne, masu yi masa sujada kuwa dole su yi masa sujada a ruhu, da gaskiya kuma.”
God is spirit, and those who worship Him must worship in spirit and truth.”
25 Macen ta ce, “Na san cewa Almasihu” (da ake ce da shi Kiristi) “yana zuwa. Sa’ad da ya zo kuwa, zai bayyana mana kome.”
The woman said to Him, “I know that the Messiah (who is called Christ) is coming. When He comes, He will explain everything to us.”
26 Sai Yesu ya ce, “Ni mai maganan nan da ke, Ni ne shi.”
Jesus told her, “I who speak to you am He.”
27 Suna gama magana ke nan sai almajiransa suka iso, suka yi mamakin ganin yana magana da mace. Amma ba wanda ya ce, “Me kake so?” Ko “Me ya sa kake magana da ita?”
Just then Jesus’ disciples returned. They were surprised to find him talking with a woman, but no one asked, “What do you want?” or “Why are you talking with her?”
28 Sai macen ta bar tulunta na ruwa, ta koma cikin gari ta ce wa mutane,
Then, leaving her water jar, the woman went back to the town and began telling the people,
29 “Ku zo, ku ga mutumin da ya gaya mini duk abin da na taɓa yi. Shin, ko shi ne Kiristi?”
“Come, see a man who told me everything that I ever did. Could this be the Christ?”
30 Sai suka fita daga garin suka nufa inda yake.
They went out of the city, and started to go to Him.
31 Ana cikin haka, sai almajiransa suka roƙe shi suka ce, “Rabbi, ci abinci mana.”
Meanwhile, the disciples urged Him, saying “Rabbi, eat something.”
32 Amma ya ce musu, “Ina da abincin da ba ku san kome a kai ba.”
He told them, “I have food to eat that you don’t know about.”
33 Sai almajiran suka ce wa juna, “Shin, ko wani ya kawo masa abinci ne?”
So the disciples asked one another, “Nobody brought Him anything to eat, did they?”
34 Yesu ya ce, “Abincina shi ne, in aikata nufin wannan da ya aiko ni, in kuma gama aikinsa.
Jesus told them, “My food is to do the will of Him who sent me, and to accomplish His work.
35 Ba kukan ce, ‘Sauran wata huɗu a yi girbi ba?’ Ina gaya muku, ku ɗaga idanu ku dubi gonaki! Sun isa girbi.
Don’t you say, ‘It’s still four months until the harvest’? Look, I tell you, lift up your eyes, and look at the fields! They are ripe for harvest.
36 Mai girbi na samun lada, yana kuma tara amfani zuwa rai madawwami, domin mai shuka da mai girbi su yi farin ciki tare. (aiōnios g166)
He who harvests is already receiving wages, and is gathering fruit for eternal life, so that he who plants and he who harvests may rejoice together. (aiōnios g166)
37 Karin maganan nan gaskiya ne cewa, ‘Wani da shuka, wani kuma da girbi.’
Thus the saying ‘One plants and another harvests’ is true.
38 Na aike ku girbin abin da ba ku yi aikinsa ba. Waɗansu sun yi aikin nan mai wahala, ku kuwa kun sami ladan aikinsu.”
I sent you to harvest that for which you didn’t labor. Others have labored, and you have entered into their labor.”
39 Samariyawa da yawa daga wannan gari suka gaskata da shi saboda shaidar macen da ta ce, “Ya gaya mini duk abin da na taɓa yi.”
Many Samaritans from that town believed in Jesus because of the woman’s testimony, “He told me everything that I ever did.”
40 To, da Samariyawa suka zo wurinsa, sai suka roƙe shi yă zauna da su, ya kuwa zauna kwana biyu.
So when the Samaritans arrived, they asked Him to stay with them, and He stayed there two days.
41 Saboda kalmominsa kuwa da yawa suka gaskata.
Many more believed because of His words.
42 Sai suka ce wa macen, “Yanzu kam mun gaskata, ba don abin da kika faɗa kawai ba; yanzu mun ji da kanmu, mun kuwa san cewa wannan mutum tabbatacce shi ne Mai Ceton duniya.”
They told the woman, “It’s no longer just because of what you said that we believe, for we have heard for ourselves, and we know that this is truly the Savior of the world, the Christ.”
43 Bayan kwana biyun nan sai ya bar can zuwa Galili.
After the two days, He departed from there and went to Galilee,
44 (To, Yesu kansa ya taɓa faɗa cewa annabi ba shi da daraja a ƙasarsa.)
for Jesus Himself testified that a prophet has no honor in his own country.
45 Da ya isa Galili, sai mutanen Galili suka marabce shi. Sun ga duk abin da ya yi a Urushalima a lokacin Bikin Ƙetarewa, gama su ma sun kasance a can.
When He arrived in Galilee, the Galileans welcomed Him. They had seen all that He had done in Jerusalem at the Passover Feast, for they had been there, too.
46 Sai ya sāke ziyarci Kana ta Galili inda ya juya ruwa ya zama ruwan inabi. Akwai wani ma’aikacin hukuma a can wanda ɗansa yake kwance da rashin lafiya a Kafarnahum.
Therefore He came back to Cana of Galilee, where He had made the water wine. There was a certain royal official, whose son was sick at Capernaum.
47 Da mutumin nan ya ji cewa Yesu ya isa Galili daga Yahudiya, sai ya je wurinsa ya roƙe shi yă zo yă warkar da ɗansa da yake bakin mutuwa.
When he heard that Jesus had come out of Judea into Galilee, he went to Him and begged Him to come down and heal his son, who was at the point of death.
48 Yesu ya ce masa, “Ku mutane, in ba kun ga alamu da abubuwan banmamaki ba, ba yadda za a yi ku ba da gaskiya.”
Jesus told him, “Unless you people see signs and wonders, you will never believe.”
49 Ma’aikacin hukuman ya ce, “Ranka yă daɗe, ka zo kafin ɗana yă mutu.”
The royal official said to Him, “Sir, come down before my child dies!”
50 Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ka tafi. Ɗanka zai rayu.” Mutumin kuwa ya amince da maganar da Yesu ya yi ya kuwa tafi.
Jesus told him, “Go in peace. Your son lives.” So the man believed the words that Jesus spoke to him, and he went his way.
51 Tun yana kan hanya, bayinsa suka tarye shi da labari cewa yaron yana warkewa.
As he was still going down the road, his servants met him, saying that his son was living.
52 Da ya tambayi lokacin da ɗansa ya sami sauƙi, sai suka ce masa, “Zazzaɓin ya sake shi jiya a sa’a ta bakwai.”
So he asked them the hour when he began to recover, and they told him, “Yesterday at the seventh hour, the fever left him.”
53 Sai mahaifin ya gane a daidai wannan lokaci ne Yesu ya ce masa, “Ɗanka zai rayu.” Saboda haka shi da dukan iyalinsa suka gaskata.
The father realized that it was at that hour that Jesus told him, “Your son lives,” and he himself believed, along with his whole household.
54 Wannan ce abin banmamaki ta biyu da Yesu ya yi, bayan zuwansa daga Yahudiya zuwa Galili.
This was the second sign that Jesus did, when He had come from out of Judea to Galilee.

< Yohanna 4 >