< Luka 2 >

1 A waɗancan kwanaki, Kaisar Augustus ya ba da doka cewa ya kamata a yi ƙidaya a dukan masarautar Roma.
Now in those days, it came about that Caesar Augustus sent out a decree ordering that a census be taken of all the people living in the world.
2 (Wannan ce ƙidaya ta fari da aka yi a lokacin da Kwiriniyus yake gwamnar Suriya.)
This was the first census made while Quirinius was governor of Syria.
3 Sai kowa ya koma garinsa don a rubuta shi.
So everyone went to his own city to be registered for the census.
4 Saboda haka Yusuf ma ya haura daga Nazaret a Galili zuwa Yahudiya, ya tafi Betlehem garin Dawuda, don shi daga gida da kuma zuriyar Dawuda ne.
Joseph also went up from Galilee, from the city of Nazareth, to Judea, to the city of David which is called Bethlehem, because he was of the house and family line of David.
5 Ya tafi can don a rubuta shi tare da Maryamu, wadda aka yi masa alkawari zai aura, tana kuwa da ciki.
He went there to register along with Mary, who was engaged to him and was pregnant.
6 Yayinda suke can, sai lokacin haihuwar jaririn ya yi,
Now it came about that while they were there, the time came for her to deliver her baby.
7 ta kuwa haifi ɗanta na fari. Ta nannaɗe shi a zane ta kuma kwantar da shi cikin wani kwami, don ba su sami ɗaki a masauƙi ba.
She gave birth to a son, her firstborn child, and she wrapped him in long strips of cloth and laid him in a manger, because there was no room for them in the inn.
8 Akwai makiyaya masu zama a fili kusa da wurin, suna tsaron garkunan tumakinsu da dare.
There were shepherds in that region who were staying in the fields, guarding their flock at night.
9 Sai wani mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare su, ɗaukakar Ubangiji kuma ta haskaka kewaye da su, suka kuwa tsorata ƙwarai.
An angel of the Lord appeared to them, and the glory of the Lord shone around them, and they were filled with great fear.
10 Amma mala’ikan ya ce musu, “Kada ku ji tsoro. Na kawo muku labari mai daɗi na farin ciki mai yawa ne wanda zai zama domin dukan mutane.
Then the angel said to them, “Do not be afraid, because I bring you the good news that will bring great joy to all the people.
11 Yau a birnin Dawuda an haifa muku Mai Ceto; shi ne Kiristi Ubangiji.
Today a savior was born for you in the city of David! He is Christ the Lord!
12 Wannan zai zama alama a gare ku. Za ku tarar da jariri a nannaɗe a zane kwance a kwami.”
This is the sign that will be given to you: You will find a baby wrapped in strips of cloth and lying in a manger.”
13 Ba labari sai ga taron rundunar sama suka bayyana tare da mala’ikan, suna yabon Allah suna cewa,
Suddenly there was together with the angel a great, heavenly army praising God and saying,
14 “Ɗaukaka ga Allah a can cikin sama, a duniya kuma salama ga mutane waɗanda tagomashinsa yake bisansu.”
“Glory to God in the highest, and may there be peace on earth among people with whom he is pleased.”
15 Da mala’ikun suka bar su, su suka koma sama, sai makiyayan suka ce wa juna, “Mu je Betlehem mu ga wannan abin da ya faru, wanda Ubangiji ya sanar mana.”
It came about that when the angels had gone away from them into heaven, the shepherds said to each other, “Let us now go to Bethlehem, and see this thing that has happened, which the Lord has made known to us.”
16 Sai suka tafi da sauri, suka tarar da Maryamu da Yusuf, da kuma jaririn kwance a kwami.
They hurried there and found Mary and Joseph, and saw the baby lying in the manger.
17 Sa’ad da suka gan shi, sai suka baza maganar da aka gaya musu game da yaron,
After they had seen him, they made known what had been said to them about this child.
18 duk kuwa waɗanda suka ji wannan, suka yi mamaki a kan abin da makiyayan suka faɗa.
All who heard it were amazed at what was spoken to them by the shepherds.
19 Amma Maryamu ta riƙe dukan waɗannan abubuwa ta kuma yi ta tunaninsu a zuciyarta.
But Mary kept thinking about all the things she had heard, treasuring them in her heart.
20 Makiyayan kuwa suka koma, suna ɗaukaka suna kuma yabon Allah saboda dukan abubuwan da suka ji, suka kuma gani, yadda aka gaya musu.
The shepherds returned, glorifying and praising God for everything that they had heard and seen, just as it had been spoken to them.
21 A rana ta takwas, da lokaci ya yi da za a yi masa kaciya, sai aka ba shi suna Yesu, sunan da mala’ika ya ba shi kafin a yi cikinsa.
When it was the end of the eighth day, when he was circumcised, he was named Jesus, the name he had been given by the angel before he was conceived in the womb.
22 Da lokacin tsarkakewarsu bisa ga Dokar Musa ya cika, sai Yusuf da Maryamu suka ɗauke shi suka haura zuwa Urushalima don su miƙa shi ga Ubangiji
When the required number of days for their purification had passed, according to the law of Moses, Joseph and Mary brought him up to the temple in Jerusalem to present him to the Lord.
23 (yadda yake a rubuce a Dokar Ubangiji cewa, “Kowane ɗan fari, za a keɓe shi ga Ubangiji”),
As it is written in the law of the Lord, “Every male who opens the womb will be set apart to the Lord.”
24 don kuma su miƙa hadaya bisa ga abin da aka faɗa a Dokar Ubangiji cewa, “kurciyoyi biyu ko’yan tattabarai biyu.”
So they offered a sacrifice according to what was said in the law of the Lord, “a pair of doves or two young pigeons.”
25 To, akwai wani mutum a Urushalima mai suna Siman, shi mai adalci da kuma mai ibada. Yana jiran fansar Isra’ila, Ruhu Mai Tsarki kuwa yana tare da shi.
Behold, there was a man in Jerusalem, whose name was Simeon, and this man was righteous and devout. He was looking for the consolation of Israel, and the Holy Spirit was upon him.
26 An bayyana masa ta wurin Ruhu Mai Tsarki cewa ba zai mutu ba sai ya ga Kiristi na Ubangiji.
It had been revealed to him by the Holy Spirit that he would not see death before he had seen the Lord's Christ.
27 Da Ruhu ya iza shi, sai ya shiga cikin filin haikali. Sa’ad da iyayen suka kawo jaririn nan Yesu don su yi masa abin da al’adar Doka ta bukaci,
Led by the Spirit, Simeon came into the temple. When the parents brought in the infant Jesus, to do for him according to the custom of the law,
28 sai Siman ya karɓi yaron a hannuwansa ya yabi Allah, yana cewa,
he took him into his arms and praised God and he said,
29 “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kamar yadda ka yi alkawari, yanzu ka sallami bawanka lafiya.
“Now let your servant depart in peace, Lord, according to your word.
30 Gama idanuna sun ga cetonka,
For my eyes have seen your salvation,
31 wanda ka shirya a gaban dukan mutane,
which you have prepared in the presence of all peoples:
32 haske don bayyanawa ga Al’ummai da kuma ɗaukaka ga mutanenka Isra’ila.”
A light for revelation to the Gentiles and glory to your people Israel.”
33 Mahaifin yaron da kuma mahaifiyarsa suka yi mamaki abin da aka faɗa game da shi.
His father and mother were amazed at what was said about him.
34 Sa’an nan Siman ya sa musu albarka ya ce wa Maryamu mahaifiyarsa, “An ƙaddara yaron nan yă zama sanadin fāɗuwa da tashin mutane da yawa a Isra’ila, zai kuma zama alamar da mutane ba za su so ba,
Simeon blessed them and said to Mary his mother, “Behold, this child is appointed for the downfall and rising up of many people in Israel and for a sign that is rejected—
35 ta haka za a fallasa tunanin zukatan mutane da yawa. Ke ma, takobi zai soki zuciyarki.”
and a sword will pierce your own soul—so that the thoughts of many hearts may be revealed.”
36 Akwai wata annabiya ma, mai suna Anna, diyar Fanuwel, na kabilar Asher. Ta tsufa kutuf; ta yi zama da mijinta shekaru bakwai bayan sun yi aure,
A prophetess named Anna was there. She was the daughter of Phanuel from the tribe of Asher. She was very old. She had lived with her husband for seven years after her virginity,
37 ta kuwa zama gwauruwa sai da ta kai shekaru tamanin da huɗu. Ba ta taɓa barin haikali ba, tana sujada dare da rana, tana kuma azumi da addu’a.
and was a widow for eighty-four years. She never left the temple but was serving with fastings and prayers, night and day.
38 Tana haurawa wurinsu ke nan a wannan lokaci, sai ta yi wa Allah godiya ta kuma yi magana game da yaron nan ga dukan waɗanda suke sauraron fansar Urushalima.
At that very hour she came near to them and began giving thanks to God and she spoke about the child to everyone who had been waiting for the redemption of Jerusalem.
39 Bayan da Yusuf da Maryamu suka gama yin dukan abubuwan da Dokar Ubangiji ta bukaci, sai suka koma Galili suka tafi Nazaret garinsu.
When they had finished everything they were required to do according to the law of the Lord, they returned to Galilee, to their own town of Nazareth.
40 Yaron kuwa ya yi girma ya yi ƙarfi; ya cika da hikima, alherin Allah kuwa yana bisansa.
The child grew and became strong, increasing in wisdom, and the grace of God was upon him.
41 Kowace shekara, iyayen Yesu sukan je Urushalima don Bikin Ƙetarewa.
His parents went every year to Jerusalem for the Festival of the Passover.
42 Da Yesu ya cika shekaru goma sha biyu, sai suka tafi Bikin bisa ga al’ada.
When he was twelve years old, they again went up at the customary time for the feast.
43 Bayan Bikin, da iyayen suka kama hanya don su koma gida, sai Yesu, yaron nan, ya tsaya a Urushalima, ba da saninsu ba.
After they had stayed the full number of days for the feast, they began to return home. But the boy Jesus stayed behind in Jerusalem and his parents did not know it.
44 Su kuwa sun ɗauka yana tare da su, saboda haka, suka yi ta tafiya har na yini guda. Sa’an nan suka fara nemansa cikin’yan’uwansu da abokansu.
They assumed that he was with the group that was traveling with them, so they traveled a day's journey. Then they started looking for him among their relatives and friends.
45 Da ba su gan shi ba, sai suka koma Urushalima nemansa.
When they did not find him, they returned to Jerusalem and started looking for him there.
46 Bayan kwana uku, sai suka same shi a filin haikali zaune a tsakiyar malamai, yana sauraronsu yana kuma yi musu tambayoyi.
It came about that after three days, they found him in the temple, sitting in the middle of the teachers, listening to them and asking them questions.
47 Dukan waɗanda suka ji shi, suka yi mamakin fahimtarsa, da amsoshinsa.
All who heard him were amazed at his understanding and his answers.
48 Da iyayensa suka gan shi sai suka yi mamaki. Mahaifiyarsa ta ce masa, “Ɗana, don me ka yi mana haka? Ni da mahaifinka duk mun damu muna nemanka.”
When they saw him, they were astonished. His mother said to him, “Son, why have you treated us this way? Listen, your father and I have been anxiously searching for you.”
49 Sai ya ce, “Don me kuke nemana? Ba ku san cewa, dole in kasance a gidan Ubana ba?”
He said to them, “Why were you searching for me? Did you not know that I had to be about my Father's business?
50 Amma ba su fahimci abin da yake faɗin musu ba.
But they did not understand what he meant by those words.
51 Sai ya koma Nazaret tare da su, yana yi musu biyayya. Mahaifiyarsa kuma ta riƙe dukan waɗannan abubuwa a zuciyarta.
Then he went back home with them to Nazareth and was obedient to them. His mother treasured all these things in her heart.
52 Yesu kuwa ya yi girma, ya kuma ƙaru cikin hikima, ya kuma sami tagomashi a wurin Allah da mutane.
But Jesus continued to grow in wisdom and stature, and increased in favor with God and people.

< Luka 2 >