< Zabura 7 >

1 Wani shiggayiyon ta Dawuda, wanda Ya Rera wa Ubangiji game da Kush mutumin Benyamin. Ya Ubangiji Allahna, na zo neman mafaka a wurinka; ka cece ni ka kuɓutar da ni daga dukan waɗanda suke bi na,
Shiggaion of David, which he sang unto the LORD, concerning the words of Cush the Benjamite. O LORD my God, in thee do I put my trust: save me from all them that persecute me, and deliver me:
2 in ba haka ba za su yayyage ni kamar zaki su ɓarke ni kucu-kucu ba tare da wani da zai cece ni ba.
Lest he tear my soul like a lion, rending [it] in pieces, while [there is] none to deliver.
3 Ya Ubangiji Allahna, in na yi kuskure aka kuwa sami laifi a hannuwana,
O LORD my God, if I have done this; if there be iniquity in my hands;
4 in na yi mugunta ga wanda yake zaman lafiya da ni ko kuwa ba da wani dalilin cuci abokin gābana,
If I have rewarded evil unto him that was at peace with me; (yea, I have delivered him that without cause is mine enemy: )
5 to, bari abokin gābana yă bi yă kuma cim mini; bari yă tattake raina a ƙasa ya sa in kwana a ƙura. (Sela)
Let the enemy persecute my soul, and take [it; ] yea, let him tread down my life upon the earth, and lay mine honour in the dust. (Selah)
6 Ka tashi, ya Ubangiji, cikin fushinka; ka tashi gāba da fushin abokan gābana. Ka farka, Allahna, ka umarta adalci.
Arise, O LORD, in thine anger, lift up thyself because of the rage of mine enemies: and awake for me [to] the judgment [that] thou hast commanded.
7 Bari taron mutane su taru kewaye da kai. Ka yi mulki a bisansu daga bisa;
So shall the congregation of the people compass thee about: for their sakes therefore return thou on high.
8 bari Ubangiji mai shari’ar mutane. Ka shari’anta ni Ya Ubangiji, bisa ga adalcina, bisa ga mutuncina, ya Mafi Ɗaukaka.
The LORD shall judge the people: judge me, O LORD, according to my righteousness, and according to mine integrity [that is] in me.
9 Ya Allah mai adalci, wanda yake binciken tunani da zukata, ka kawo ƙarshen rikicin mugaye ka kuma sa adalai su zauna lafiya.
Oh let the wickedness of the wicked come to an end; but establish the just: for the righteous God trieth the hearts and reins.
10 Garkuwata shi ne Allah Mafi Ɗaukaka, wanda yake ceton masu tsabtar zuciya.
My defence [is] of God, which saveth the upright in heart.
11 Allah alƙali ne mai adalci, Allahn da yakan bayyana fushinsa kowace rana.
God judgeth the righteous, and God is angry [with the wicked] every day.
12 In mutum bai tuba ba, Allah zai wasa takobinsa; zai tanƙware yă kuma ɗaura bakansa.
If he turn not, he will whet his sword; he hath bent his bow, and made it ready.
13 Ya shirya makamansa masu dafi; ya shirya kibiyoyinsa masu wuta.
He hath also prepared for him the instruments of death; he ordaineth his arrows against the persecutors.
14 Wanda yake da cikin mugunta ya kuma ɗauki cikin damuwa yakan haifi ƙarya.
Behold, he travaileth with iniquity, and hath conceived mischief, and brought forth falsehood.
15 Wanda ya haƙa rami yakan fāɗa cikin ramin da ya haƙa.
He made a pit, and digged it, and is fallen into the ditch [which] he made.
16 Damuwar da ya ja yakan sāke nannaɗe a kansa; fitinarsa takan sauka a kansa.
His mischief shall return upon his own head, and his violent dealing shall come down upon his own pate.
17 Zan gode wa Ubangiji saboda adalcinsa zan kuma rera yabo ga sunan Ubangiji Mafi Ɗaukaka.
I will praise the LORD according to his righteousness: and will sing praise to the name of the LORD most high.

< Zabura 7 >