< Zabura 77 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Na Asaf. Zabura ce. Na yi kuka ga Allah don taimako; na yi kuka ga Allah don yă ji ni.
For the Chief Musician. To Jeduthun. A Psalm by Asaph. My cry goes to God! Indeed, I cry to God for help, and for him to listen to me.
2 Sa’ad da nake cikin damuwa, na nemi Ubangiji; da dare na miƙa hannuwa ba gajiya raina kuma ya ƙi yă ta’azantu.
In the day of my trouble I sought the Lord. My hand was stretched out in the night, and didn’t get tired. My soul refused to be comforted.
3 Na tuna da kai, ya Allah, na kuma yi nishi; na yi nishi, ƙarfina kuwa duk ya raunana. (Sela)
I remember God, and I groan. I complain, and my spirit is overwhelmed. (Selah)
4 ka hana idanuna rufewa; na damu ƙwarai har ba na iya magana.
You hold my eyelids open. I am so troubled that I can’t speak.
5 Na yi tunani kwanakin da suka wuce, shekarun da suka wuce da daɗewa;
I have considered the days of old, the years of ancient times.
6 na tuna da waƙoƙina da dare. Zuciyata ta yi nishi, ƙarfina kuwa ya nemi yă sani.
I remember my song in the night. I consider in my own heart; my spirit diligently inquires:
7 “Ubangiji zai ƙi ne har abada? Ba zai taɓa nuna alherinsa kuma ba?
“Will the Lord reject us forever? Will he be favorable no more?
8 Ƙaunarsa marar ƙarewa ta ɓace ke nan har abada? Alkawarinsa ya kāsa ke nan a dukan lokaci?
Has his loving kindness vanished forever? Does his promise fail for generations?
9 Allah ya manta yă yi jinƙai? Cikin fushinsa ya janye tausayinsa ne?” (Sela)
Has God forgotten to be gracious? Has he, in anger, withheld his compassion?” (Selah)
10 Sai na yi tunani, “Zan yi roƙo saboda wannan, shekarun da Mafi Ɗaukaka ya miƙa hannunsa na dama.”
Then I thought, “I will appeal to this: the years of the right hand of the Most High.”
11 Zan tuna da ayyukan Ubangiji; I, zan tuna mu’ujizanka na tun dā.
I will remember the LORD’s deeds; for I will remember your wonders of old.
12 Zan yi tunani a kan dukan ayyukanka in lura da dukan manyan abubuwan da ka aikata.
I will also meditate on all your work, and consider your doings.
13 Hanyoyinka, ya Allah, masu tsarki ne. Wanda allah ne yake da girma kamar Allahnmu?
Your way, God, is in the sanctuary. What god is great like God?
14 Kai ne Allahn da yakan aikata mu’ujizai; ka nuna ikonka a cikin mutane.
You are the God who does wonders. You have made your strength known among the peoples.
15 Da hannunka mai ƙarfi ka fanshi mutanenka, zuriyar Yaƙub da Yusuf. (Sela)
You have redeemed your people with your arm, the sons of Jacob and Joseph. (Selah)
16 Ruwaye sun gan ka, ya Allah, ruwaye sun gan ka suka firgita; zurfafan gaske sun girgiza.
The waters saw you, God. The waters saw you, and they writhed. The depths also convulsed.
17 Gizagizai sun sauko da ruwa, sararin sama suka buga tsawa; kibiyoyinka suka yi ta kai komo da walƙiya.
The clouds poured out water. The skies resounded with thunder. Your arrows also flashed around.
18 Aka ji tsawanka a cikin guguwa, walƙiyarka ta haskaka duniya; duniya ta yi rawar jiki ta girgiza.
The voice of your thunder was in the whirlwind. The lightnings lit up the world. The earth trembled and shook.
19 Hanyarka ta bi ta cikin teku, hanyarka ta bi cikin manyan ruwaye, duk da haka ba a ga sawunka ba.
Your way was through the sea, your paths through the great waters. Your footsteps were not known.
20 Ka bi da mutanenka kamar garke ta hannun Musa da Haruna.
You led your people like a flock, by the hand of Moses and Aaron.

< Zabura 77 >