< Yohanna 2 >

1 Bayan kwana uku, akwai aure a Kana ta Galili, mahaifiyar Yesu kuma tana wurin.
E no terceiro dia houve um casamento em Caná da Galileia; e a mãe de Jesus estava ali.
2 An gayyaci Yesu da almajiransa zuwa auren.
E também Jesus foi convidado com seus discípulos ao casamento.
3 Da ruwan inabin ya kare, maihafiyar Yasu tace masa, “basu da ruwan inabi.”
E tendo faltado vinho, a mãe de Jesus lhe disse: Não têm vinho.
4 Yesu yace mata, “Mace, me yasa kika zo wurina? Lokaci na bai yi ba tukuna”.
Jesus lhe disse: O que eu tenho contigo, mulher? A minha hora ainda não chegou.
5 Maihafiyarsa tace wa ma'aikatan, “Ku yi duk abin da yace maku.”
Sua mãe disse aos serventes: Fazei tudo quanto ele vos disser.
6 To akwai randunan ruwa na dutse guda shidda a wurin wadanda Yahudawa ke amfani da su domin al'adansu na tsarkakewa, kowace zata iya daukar durom guda.
E estavam ali postos seis vasos de pedra, conforme à purificação dos judeus, em cada uma cabiam duas ou três metretas. )
7 Yesu yace masu, “Cika randunan da ruwa”. Sai suka cika randunan makil.
Disse-lhes Jesus: Enchei estes vasos com água. E encheram-nas até encima.
8 Sai yace wa ma'aikatan, “Ku diba daga ciki ku kai wa shugaban biki.” Sai suka yi hakannan.
E disse-lhes: Agora tirai, e a levai ao mestre de cerimônia. Então levaram.
9 Shugaban bikin ya dandana ruwan da ya zama ruwan inabin, amma bai san inda ya fito ba (amma ma'aikatan wadanda suka jawo ruwan sun sani). Sai ya kira ango
E quando o mestre de cerimônia experimentou a água feita vinho (sem saber de onde era, porém os serventes que haviam tirado a água sabiam), o mestre de cerimônia chamou o noivo,
10 yace masa, “Kowane mutum yakan raba ruwan inabi mai kyau da farko, kafin mai arhar bayan an shanye mai kyaun. Amma kai ka ajiye mai kyaun sai yanzu.”
E disse-lhe: Todos põem primeiro o vinho bom, e quando [os convidados] já [estão] bêbados, então [se dá] o pior; [porém] tu guardaste o bom vinho até agora.
11 Wannan alama ta farko ce da Yesu yayi a Kana ta Galili, ya kuma bayyana daukakarsa, almajiransa kuma suka gaskata da shi.
Este princípio de sinais Jesus fez em Caná da Galileia, e manifestou sua glória; e seus discípulos creram nele.
12 Bayan wannan, Yesu, da mahaifiyarsa, da 'yan'uwansa da almajiransa suka tafi Kafarnahum, kuma suka zauna can wasu 'yan kwanaki.
Depois disto desceu a Cafarnaum, ele e sua mãe, seus irmãos, e seus discípulos, e ficaram ali não muitos dias.
13 To idin ketarewa na Yahudawa ya kusato, Yesu kuwa ya wuce zuwa Urushalima.
E estava perto a Páscoa dos judeus, e Jesus subiu a Jerusalém.
14 Ya iske wadanda suke sayar da shanu da tumaki da tantabaru, masu canjin kudi kuma na zaune a wurin.
E achou no Templo os que vendiam bois, ovelhas, e pombas, e os cambistas sentados.
15 Sai yayi tsumingiya da igiyoyi ya kore su duka daga cikin haikalin, duk da tumakin da shanun. Sai ya watsar da sulallan masu canjin kudin ya birkitar da teburansu.
E tendo feito um açoite com cordas, lançou todos para fora do Templo, assim como as ovelhas, e os bois; e espalhou o dinheiro dos cambistas, e virou as mesas.
16 Yace wa masu sayar da tantabaru, “Ku fitar da wadannan abubuwa daga nan. Ku daina maida gidan Ubana wurin kasuwanci.”
E aos que vendiam pombas, disse: Tirai isto daqui; e não torneis a casa de meu Pai uma casa de comércio!
17 Almajiransa suka tuna a rubuce yake, “Himma domin gidanka za ta cinye ni.”
E lembraram-se seus discípulos que está escrito: O zelo de tua casa me tem me devorado.
18 Sai shugabannin Yahudawa suka amsa suka ce masa, “Wace alama za ka nuna mana, da shike kana yin wadannan abubuwan?”
Responderam pois os Judeus, e disseram-lhe: Que sinal nos mostras de que fazes estas coisas?
19 Yesu ya amsa, “Ku rushe wannan haikali, kuma a cikin kwana uku zan gina shi.”
Respondeu Jesus, e disse-lhes: Derrubai este Templo, e em três dias o levantarei.
20 Sai shugabanin Yahudawa suka ce, “An dauki shekaru arba'in da shidda kamin a gama gina wannan haikalin, za ka dau kwanaki uku kadai wajen gina shi?”
Os judeus, pois, disseram: [Durante] quarenta e seis anos este Templo foi edificado, e tu o levantarás tu em três dias?
21 Amma yana nufin haikali na jikinsa ne.
Porém ele falava do Templo de seu corpo.
22 Bayan da aka tashe shi daga matattu, sai almajiransa suka tuna ya fadi haka, suka kuma ba da gaskiya ga nassi da wannan kalami da Yesu ya fada.
Portanto, quando ressuscitou dos mortos, seus discípulos se lembraram que ele lhes tinha dito isto; e creram na Escritura, e na palavra que Jesus tinha [lhes] dito.
23 Kuma, da yana Urushalima a idin ketarewa, a lokacin idin, mutane da yawa suka gaskata ga sunansa, sa'adda suka ga alamun da ya yi.
E estando ele em Jerusalém pela páscoa, na festa, muitos creram em seu nome, ao verem os sinais que ele fazia.
24 Amma Yesu bai yadda da su ba domin ya san su duka,
Mas o mesmo Jesus a si mesmo não confiava neles, porque conhecia a todos.
25 saboda baya bukatar wani ya shaida masa game da mutum, domin ya san abinda ke cikin sa.
E não necessitava de que alguém [lhe] desse testemunho de ser humano algum, pois ele bem sabia o que havia no [interior do] ser humano.

< Yohanna 2 >