< Luka 13 >

1 A lokacin, wadansu mutane suka gaya masa game da galilawa wadanda Bilatus ya gauraye jininsu da hadayunsu.
En ce même temps, quelques personnes, qui se trouvaient là, racontèrent à Jésus ce qui était arrivé aux Galiléens, dont Pilate avait mêlé le sang à celui de leurs sacrifices.
2 Sai Yesu ya amsa masu yace “Kuna tsammani wadannan Galilawa sun fi duk sauran Galilawan zunubi ne, da suka sha azaba haka?
Jésus, prenant la parole, leur dit: Pensez-vous que ces Galiléens fussent de plus grands pécheurs que tous les autres Galiléens, parce qu'ils ont souffert ainsi?
3 A'a, ina gaya maku. In ba ku tuba ba, dukanku za ku halaka kamarsu.
Non? vous dis-je; mais si vous ne vous repentez, vous périrez tous pareillement.
4 Ko kuwa mutane goma sha takwas din nan da suna Siluwam wadanda hasumiya ta fado a kansu ta kashe su, kuna tsamani sun fi duk sauran mutanen Urushalima laifi ne?
Ou bien, ces dix-huit personnes, sur qui la tour de Siloé est tombée et qu'elle a tuées, pensez-vous qu'elles fussent plus coupables que tous les autres habitants de Jérusalem?
5 Ina gaya maku ba haka bane. Amma duk wanda ya ki tuba, dukanku za su hallaka”
Non, vous dis-je; mais si vous ne vous repentez, vous périrez tous également.
6 Yesu ya fada wannan misali, “Wani mutum yana da baure wanda ya shuka a garkar inabinsa sai ya zo neman 'ya'yan itacen amma bai samu ba.
Il disait aussi cette parabole: Un homme avait un figuier planté dans sa vigne; il vint y chercher du fruit et n'en trouva point.
7 Sai mutumin ya ce wa mai kula da garkar, “ka ga, shekara uku kenan nake zuwa neman 'ya'yan wannan baure, amma ban samu ba. A sare shi. Yaya za a bar shi ya tsare wurin a banza?
Alors il dit au vigneron: Voilà trois ans que je viens chercher du fruit à ce figuier et que je n'en trouve pas. Coupe-le; pourquoi occupe-t-il la terre inutilement?
8 Sai mai lura da garkar ya amsa yace, 'Ka dan ba shi lokaci kadan in yi masa kaftu in zuba masa taki.
Le vigneron lui répondit: Seigneur, laisse-le encore cette année; je creuserai tout autour et j'y mettrai du fumier.
9 In yayi 'ya'ya shekara mai zuwa to, amma in bai yi 'ya'ya ba sai a sare shi!”'
Peut-être qu'à l'avenir il portera du fruit; sinon tu le feras couper.
10 Wata rana Yesu yana koyarwa a wata majami' a ran Asabaci.
Jésus enseignait dans une synagogue un jour de sabbat.
11 Sai, ga wata mace a wurin shekarunta goma sha takwas tana da mugun ruhu, duk ta tankware, ba ta iya mikewa.
Or, il y avait là une femme possédée d'un esprit qui la rendait infirme depuis dix-huit ans; elle était courbée et ne pouvait pas du tout se redresser.
12 Da Yesu ya gan ta, sai ya kira ta ya ce mata, an warkar da ke daga wannan cuta.”
Jésus, la voyant, l'appela et lui dit: Femme, tu es délivrée de ton infirmité;
13 Sai Yesu ya dora hannunsa a kanta, nan da nan sai ta mike a tsaye ta fara daukaka Allah.
et il lui imposa les mains. A l'instant, elle se redressa, et elle se mit à rendre gloire à Dieu.
14 Amma shugaban majami'a yayi fushi domin Yesu yayi warkarwa a ranar Asabaci. Sai shugaban ya amsa yace wa jama'a, “Akwai ranaku shida da ya kamata a yi aiki. Ku zo domin a warkar da ku amma ba ranar Asabaci ba.”
Alors le chef de la synagogue, indigné de ce que Jésus avait fait cette guérison un jour de sabbat, prit la parole et, dit à la foule: Il y a six jours pendant lesquels on doit travailler venez donc ces jours-là pour être guéris, et non pas le jour du sabbat.
15 Amma Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Munafukai! Ashe kowannenku ba ya kwance Jakinsa ko Sa daga turkensa ya kai shi banruwa ran Asabaci?
Mais le Seigneur lui répondit: Hypocrites, chacun de vous, le jour du sabbat, ne détache-t-il pas de la crèche son boeuf ou son âne pour le mener boire?
16 Ashe wannan 'yar gidan Ibrahim, wanda shaidan ya daure ta shekara goma sha takwas, wato ba za a iya kwance ta a ranar Asabaci kenan ba?
Et cette fille d'Abraham, que Satan tenait liée depuis dix-huit ans, ne fallait-il pas la délivrer de ce lien le jour du sabbat?
17 Da ya fada wadannan abubuwa, dukansu da suka yi adawa da shi suka kunyata, duk taron kuwa suka yi ta farin ciki da abubuwa masu daraja da yayi.
Comme il parlait ainsi, tons ses adversaires étaient confus, et tout le peuple se réjouissait de toutes les choses glorieuses qu'il accomplissait.
18 Sai Yesu ya ce, “Yaya za a misalta mulkin Allah, kuma da me zan kwatanta shi?
Et Jésus disait donc: A quoi ressemble le royaume de Dieu, et à quoi le comparerai-je?
19 Yananan kamar kwayar mastad, wanda wani mutum ya dauka ya jefa ta a lambunsa, ta kuma yi girma ta zama gagarumin itace, har tsuntsaye suka yi shekarsu a rassanta.”
Il est semblable à un grain de moutarde, qu'un homme a pris et a jeté dans son jardin; il a poussé, il est devenu un arbre et les oiseaux du ciel ont fait leurs nids dans ses branches.
20 Ya sake cewa, “Da me zan kwatanta mulkin Allah?
Il dit encore: A quoi comparerai-je le royaume de Dieu?
21 Yana kamar yisti wanda wata mace ta dauka ta cuda da mudu uku na garin alkama don ya kumburar da shi.”
Il est semblable à du levain qu'une femme prend, et qu'elle mêle à trois mesures de farine, pour faire lever toute la pâte.
22 Yesu ya ziyarci kowanne birni da kauye, a hanyar sa ta zuwa Urushalima yana koyar da su.
Jésus traversait les villes et les villages, en enseignant, tandis qu'il se dirigeait vers Jérusalem.
23 Sai wani ya ce masa, “Ubangiji, wadanda za su sami ceto kadan ne?” Sai ya ce masu,
Quelqu'un lui demanda: Seigneur, n'y a-t-il qu'un petit nombre de gens qui soient sauvés? Il leur répondit:
24 “Ku yi kokari ku shiga ta matsatsiyar kofa, domin na ce maku, mutane dayawa za su nemi shiga amma ba za su iya shiga ba.
Efforcez-vous d'entrer par la porte étroite; car je vous le déclare, il y en a beaucoup qui chercheront à entrer, et ils ne le pourront pas.
25 In dai maigida ya riga ya tashi ya rufe kofa, sannan za ku tsaya a waje kuna kwankwasa kofar kuna cewa, 'Ubangiji, Ubangiji, bari mu shiga ciki'. Sai ya amsa yace maku, 'Ni ban san ku ba ko daga ina ku ka fito.'
Et quand le maître de la maison se sera levé et aura fermé la porte, et que vous, qui serez restés dehors, vous vous mettrez à frapper et à dire: Seigneur, ouvre-nous! — il vous répondra: Je ne sais d'où vous êtes.
26 Sannan za ku ce, 'Mun ci mun sha a gabanka, ka kuma yi koyarwa a kan titunanmu.'
Alors vous vous mettrez à dire: Nous avons mangé et bu en ta présence, et tu as enseigné sur nos places publiques.
27 Amma zai amsa ya ce, “Ina gaya maku, ban san ko daga ina ku ka fito ba, ku tafi daga wurina, dukanku masu aikata mugunta!'
Et il répondra: Je vous le dis, je ne sais d'où vous êtes; retirez-vous de moi, vous tous, ouvriers d'iniquité!
28 Za a yi kuka da cizon hakora a lokacin da kun ga Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu da dukan annabawa a mulkin Allah amma ku-za a jefar da ku waje.
C'est là qu'il y aura des pleurs et, des grincements de dents, quand vous verrez Abraham, Isaac et Jacob, et tous les prophètes, dans le royaume de Dieu, et que vous serez jetés dehors.
29 Za su zo daga gabas, yamma, kudu, da arewa, za su ci a teburin abinci a mulkin Allah.
Il en viendra de l'Orient et de l'Occident, du Nord et du Midi, qui se mettront à table dans le royaume de Dieu.
30 Ku san da wannan, na karshe za su zama na farko, na farko kuma za su zama na karshe.”
Et voici qu'il y en a des derniers qui seront les premiers; et il y en a des premiers qui seront les derniers.
31 Nan take, wadansu farisiyawa suka zo suka ce masa, “Ka tafi daga nan domin Hirudus yana so ya kashe ka.”
A ce moment-là, quelques pharisiens vinrent lui dire: Pars, éloigne-toi d'ici Hérode veut te faire mourir.
32 Yesu ya ce, “Ku tafi ku gaya wa dilan nan cewa, 'Duba, na fitar da aljanu, ina warkarwa yau da gobe, kuma a rana ta uku kuwa zan gama aiki na.'
Il leur répondit: Allez dire à ce renard que je chasse les démons. J'opère des guérisons aujourd'hui et demain, et le troisième jour j'achève ma vie.
33 Ko da kaka, dole ne in ci gaba da tafiyata yau, da gobe, da kuma jibi, don bai dace a kashe annabi nesa da Urushalima ba.
Mais il faut que je marche aujourd'hui, demain, et le jour suivant, parce qu'il ne convient pas qu'un prophète périsse hors de Jérusalem.
34 Urushalima, Urushalima masu kisan annabawa, masu jifan wadanda aka aiko gare ku. Sau nawa ne ina so in tattara 'ya'yanki kamar yadda kaza take tattara 'ya'yanta a cikin fukafukanta, amma ba ki so wannan ba.
Jérusalem, Jérusalem, toi qui tues les prophètes et qui lapides ceux qui te sont envoyés, combien de fois j'ai voulu rassembler tes enfants, comme une poule rassemble sa couvée sous ses ailes, et vous ne l'avez pas voulu!
35 Duba, an yashe gidanki. Ina kwa gaya maku ba za ku kara ganina ba sai ran da kuka ce, 'Albarka ta tabbata ga mai zuwa da sunan Ubangiji.'”
Voici que votre demeure vous sera laissée dans l'abandon. Et je vous déclare que vous ne me verrez plus, jusqu'à ce que vous disiez: «Béni soit celui qui vient au nom du Seigneur!»

< Luka 13 >