< Mattiyu 27 >

1 Da gari ya waye, duk manyan firistoci da dattawan jama'a suka shirya yadda zasu kulla makirci domin su kashe shi.
At daybreak all the chief priests and the elders of the people consulted together against Jesus, to bring about his death.
2 Suka daure shi, suka mika shi ga gwamna Bilatus.
They put him in chains and led him away, and gave him up to the Roman Governor, Pilate.
3 Sa'adda Yahuza, wanda ya bashe shi, ya ga an zartarwa Yesu hukuncin kisa, ya nemi tuba ya kuma mayar da azurfar talatin ga manyan firistocin da dattawan,
Then Judas, who betrayed him, seeing that Jesus was condemned, repented of what he had done, and returned the thirty pieces of silver to the chief priests and elders.
4 yace, “Na yi zunubi ta wurin cin amanar mara laifi.” Amma sukace, “Ina ruwan mu? Ka ji da shi da kanka?”
‘I did wrong in betraying a good man to his death,’ he said. ‘What has that to do with us?’ they replied. ‘You must see to that yourself.’
5 Sai ya jefar da kwandalolin azurfar a kasa cikin haikalin ya kuma bar su, ya tafi ya rataye kansa.
Judas flung down the pieces of silver in the Temple, and left; and went away and hanged himself.
6 Sai babban firist ya dauki kwandalolin azurfar ya ce, “Ba daidai bane bisa ga shari'a musa wannan cikin ma'aji, saboda kudin jini ne.”
The chief priests took the pieces of silver, but they said, ‘We must not put them into the Temple treasury, because they are blood-money.’
7 Sai suka tattauna al'amarin a tsakanin su, kudin kuma suka sayi filin maginin tukwane domin makabatar baki.
So, after consultation, they used it to buy the “Potter’s Field” as a burial ground for foreigners,
8 Dalilin wannan ne ake kiran wurin, “Filin jini” har yau.
and that is why that field is called the “Field of Blood” to this very day.
9 Sai abin da aka fada ta bakin annabi Irmiya ya cika, cewa, “Suka dauki tsabar azurfa talatin na farashin da mutanen Isra'ila suka sa a kansa,
Then it was that these words spoken by the prophet Jeremiah were fulfilled – “They took the thirty pieces of silver, the price set on him by the people of Israel,
10 suka bayar domin sayen filin mai tukwane, kamar yadda Ubangiji ya umarce ni.”
and gave them for the potter’s field, as the Lord commanded me.”
11 Sai Yesu ya tsaya a gaban gwamna, gwamna ya kuma tambaye shi, “Kai sarkin Yahudawa ne?” Yesu ya amsa, “Haka ka fada.”
Meanwhile Jesus was brought before the Roman Governor. ‘Are you the king of the Jews?’ asked the Governor. ‘It is true,’ answered Jesus.
12 Amma da manyan firistocin da dattawan suka zarge shi, bai ce komai ba.
While charges were being brought against him by the chief priests and elders, Jesus made no reply.
13 Sai Bilatus yace masa, “Baka ji dukan zarge-zargen da ake yi maka ba?”
Then Pilate said to him, ‘Don’t you hear how many accusations they are making against you?’
14 Amma bai ce masa ko kalma guda ba, sai gwamna yayi matukar mamaki.
Yet Jesus made no reply – not even a single word; at which the Governor was greatly astonished.
15 To lokacin bikin idi, al'adar gwamna ne ya saki mutum guda wanda jama'a suka zaba.
Now, at the feast, the Governor was accustomed to grant the people the release of any one prisoner whom they might choose.
16 A wannan lokacin suna da wani sanannen dan kurkuku mai suna Barabbas.
At that time they had a notorious prisoner called Barabbas.
17 To da suka tattaru, sai Bilatus yace masu, “Wa kuke so a sakar maku? Barabbas, ko Yesu wanda ake kira Almasihu?”
So, when the people had collected, Pilate said to them, ‘Which do you wish me to release for you? Barabbas? Or Jesus who is called “Christ”?’
18 Saboda ya san sun kawo shi ne domin kishi.
For he knew that it was out of jealousy that they had given Jesus up to him.
19 Da yake zaune a kujerar shari'a, matarsa ta aika masa cewa, “Ka fita sha'anin mutumin nan marar laifi. Saboda na sha wahala sosai a yau cikin mafarki saboda shi.”
While he was still on the Bench, his wife sent this message to him – ‘Do not have anything to do with that good man, for I have been very much troubled today in a dream because of him.’
20 A lokacin nan manyan firistoci da dattawa suka rinjayi ra'ayin jama'a suce a sakar masu da Barabbas, a kashe Yesu.
But the chief priests and elders persuaded the crowds to ask for Barabbas, and to kill Jesus.
21 Sai gwamna ya tambayesu, “Wa kuke so a sakar maku?” Sukace, “Barabbas.”
The Governor, however, said to them, ‘Which of these two do you wish me to release for you?’ ‘Barabbas,’ they answered.
22 Bilatus yace masu, “Me zan yi da Yesu wanda ake kira Almasihu?” Sai duka suka amsa, “A gicciye shi.”
‘What then,’ Pilate asked, ‘should I do with Jesus who is called “Christ?”’ ‘Crucify him,’ they all replied.
23 Sai yace, “Don me, wane laifi ya aikata?” Amma suka amsa da babbar murya, “A gicciye shi”
‘Why, what harm has he done?’ he asked. But they kept shouting furiously, ‘Crucify him!’
24 Amma da Bilatus ya ga ba zai iya komai ba don hargitsi zai iya barkewa, ya dauki ruwa ya wanke hannuwansa a gaban jama'a, yace, “Ba ni da laifi ga jinin mutumin nan marar laifi. Ku yi abin da kuka ga dama.”
When Pilate saw that his efforts were unavailing, but that, on the contrary, a riot was beginning, he took some water, and washed his hands in the sight of the crowd, saying as he did so, ‘I am not answerable for this bloodshed; you must see to it yourselves.’
25 Duka mutanen sukace, “Bari jininsa ya kasance a kan mu da 'ya'yan mu.”
And all the people answered, ‘His blood be on our heads and on our children’s!’
26 Sai ya sakar masu da Barabbas amma yayi wa Yesu bulala ya mika shi garesu domin su gicciye shi.
Then Pilate released Barabbas to them, but Jesus he had scourged, and gave him up to be crucified.
27 Sai sojojin gwamna suka dauki Yesu zuwa farfajiya suka kuma tara dukan rundunar sojoji.
After that, the Governor’s soldiers took Jesus with them into the Government house, and gathered the whole garrison round him.
28 Suka yi masa tumbur sa'annan suka sa masa jar alkyabba.
They stripped him, and put on him a red military cloak,
29 Sai suka yi masa rawanin kaya suka sa a kansa, suka kuma bashi sanda a hannunsa na dama. Suka rusuna a gabansa suna masa ba'a, suna cewa, “Ranka ya dade, Sarkin Yahudawa!”
and having twisted some thorns into a crown, put it on his head, and a rod in his right hand, and then, going down on their knees before him, they mocked him. ‘Long life to you, king of the Jews!’ they said.
30 Suka kuma tofa masa yawu, suka kwace sandar suka buga masa a ka.
They spat at him and, taking the rod, kept striking him on the head;
31 Bayan sun gama masa ba'a, suka cire masa alkyabbar suka sa masa kayansa, suka jagorance shi zuwa wurin da za a gicciye shi.
and, when they had left off mocking him, they took off the military cloak, and put his own clothes on him, and led him away to be crucified.
32 Da suka fito waje, sai suka iske wani Bakurame mai suna Saminu, wanda suka tilasta ya tafi tare dasu domin ya dauki gicciyen.
As they were on their way out, they came upon a man from Cyrene called Simon, and they compelled him to go with them to carry the cross.
33 Suka iso wani wuri da ake kira Golgotta, wanda ke nufin,”Wurin kwalluwa.”
On reaching a place named Golgotha (a place named from its likeness to a skull),
34 Suka bashi ruwan inabi da aka gauraya da wani abu mai daci. Amma da ya 'dan-'dana shi sai ya ki sha.
they gave him some wine to drink which had been mixed with gall; but after tasting it, Jesus refused to drink it.
35 Bayan da suka gicciye shi, suka kada kuri'a a kan rigarsa.
When they had crucified him, they divided his clothes among them by casting lots.
36 Suka kuma zauna suna kallonsa.
Then they sat down, and kept watch over him there.
37 A sama da kansa suka sa abinda ake tuhumarsa da ita a rubuce, “Wannan shine sarkin Yahudawa.”
Above his head they fixed the accusation against him written out – “THIS IS JESUS THE KING OF THE JEWS.”
38 An gicciye shi da 'yanfashi guda biyu, daya ta damansa dayan kuma ta hagunsa.
At the same time two robbers were crucified with him, one on the right, the other on the left.
39 Wadanda suke wucewa suna zaginsa, suna girgiza kai,
The passers-by railed at him, shaking their heads as they said,
40 suna kuma cewa, “Kai da kace zaka rushe haikali ka kuma gina shi a kwana uku, ka ceci kanka mana! In dai kai Dan Allah ne, ka sauko daga gicciyen!”
‘You who would “destroy the Temple and build one in three days,” save yourself! If you are God’s Son, come down from the cross!’
41 Ta haka ma manyan firistocin suka rika yi masa ba'a, tare da marubuta da shugabannin, suna cewa,
In the same way the chief priests, with the Teachers of the Law and elders, said in mockery,
42 “Ya ceci wasu amma ya kasa ceton kansa. Shi ne sarkin Isra'ila. Ya sauko mana daga kan gicciyen, sai mu ba da gaskiya gareshi.
‘He saved others, but he cannot save himself! He is the “king of Israel”! Why doesn’t he come down from the cross now, then we will believe in him.
43 Tun da ya yarda da Allah. Bari Allahn ya cece shi mana, saboda yace, “Ni dan Allah ne.”
He has trusted in God; if God wants him, let him deliver him now; for he said “I am God’s Son.”’
44 Hakan nan ma 'yanfashin guda biyu da aka gicciye su tare suka zage shi.
Even the robbers, who were crucified with him, insulted him in the same way.
45 To tun da tsakar rana sai duhu ya rufe kasar gaba daya har karfe uku na yamma.
After midday a darkness came over all the country, lasting until three in the afternoon.
46 Wajen karfe uku, Yesu ya tada murya mai karfi yace, “Eli, Eli lama sabaktani?” wanda ke nufin, “Allahna, Allahna, don me ka yashe ni?”
About three Jesus called out loudly, ‘Eloi, Eloi, lema sabacthani’ – that is to say, “My God, my God, why have you forsaken me?”
47 Da wadanda suke tsaye kusa suka ji haka, sai sukace, “Yana kiran Iliya.”
Some of those standing by heard this, and said, ‘The man is calling for Elijah!’
48 Nan take wani ya ruga da gudu ya dauki soso ya tsoma cikin ruwan inabi mai tsami ya soka kan sandar kara ya mika masa ya sha.
One of them immediately ran and took a sponge, and, filling it with common wine, put it on the end of a rod, and offered it to him to drink.
49 Sai sauran sukace, “Rabu da shi mu gani ko Iliya zai zo ya cece shi.”
But the rest said, ‘Wait and let us see if Elijah is coming to save him.’
50 Sai Yesu ya ta da murya mai karfi yayi kuka sai ya saki ruhunsa.
But Jesus, uttering another loud cry, gave up his spirit.
51 Sai labullen haikali ya yage gida biyu daga sama zuwa kasa. Kasa kuma ta girgiza, duwatsu suka farfashe.
Suddenly the Temple curtain was torn in two from top to bottom, the earth shook, the rocks were torn asunder,
52 Kaburbura suka bude, tsarkaka kuwa wadanda suke barci da yawa suka tashi.
the tombs opened, and the bodies of many of God’s people who had fallen asleep rose,
53 Suka fito daga kaburbura bayan tashinsa, suka shiga birni mai tsarki suka bayyana ga mutane da yawa.
and they, leaving their tombs, went, after the resurrection of Jesus, into the Holy City, and appeared to many people.
54 Da hafsan sojan da wadanda suke kallon Yesu suka ga girgizar kasar da abinda ya faru, suka ji tsoro kwarai sukace, “Hakika wannan Dan Allah ne”
The Roman centurion, and the men with him who were watching Jesus, on seeing the earthquake and all that was happening, became greatly frightened and exclaimed, ‘This must indeed have been God’s Son!’
55 Mata dayawa da suka bi Yesu daga Galili domin su lura da shi suka tsaya suna kallo daga nesa.
There were many women there, watching from a distance, who had accompanied Jesus from Galilee and had been attending on him.
56 A cikin su akwai Maryamu Magadaliya, Maryamu uwar Yesu da Yusufu, da uwar 'ya'yan Zabadi.
Among them were Mary of Magdala, Mary the mother of James and Joseph, and the mother of Zebedee’s sons.
57 Da yamma sai wani attajiri mutumin Armatiya ya zo, mai suna Yusufu wanda shi ma almajirin Yesu ne.
When evening had fallen, there came a rich man from Arimathea, named Joseph, who had himself become a disciple of Jesus.
58 Ya je wurin Bilatus ya roka a bashi jikin Yesu. Sai Bilatus ya umarta a bashi.
He went to see Pilate, and asked for the body of Jesus. Pilate ordered it to be given him.
59 Yusufu ya dauki jikin, ya rufe shi da likafani mai tsabta,
So Joseph took the body, and wrapped it in a clean linen sheet,
60 sai ya sa shi a cikin sabon kabarinsa da ya sassaka cikin dutse. Sai ya mirgina babban dutse a bakin kofar kabarin ya tafi.
and laid it in his newly made tomb which he had cut in the rock; and, before he left, he rolled a great stone against the entrance of the tomb.
61 Maryamu Magadaliya da dayan Maryamun suna nan zaune akasin kabarin.
Mary of Magdala and the other Mary remained behind, sitting in front of the grave.
62 Washegari, wato bayan ranar Shiri, Sai manyan firistoci da Farisawa suka taru tare da Bilatus.
The next day – that is, the day following the Preparation-day – the chief priests and Pharisees came in a body to Pilate, and said,
63 Sukace, “Mai gida, mun tuna lokacin da mayaudarin nan yake da rai, yace, “Bayan kwana uku zan tashi.”
‘Sir, we remember that, during his lifetime, that impostor said “I will rise after three days.”
64 Saboda haka, ka bada umarni a tsare kabarin na kwana uku. In ba haka ba almajiransa zasu zo su sace shi, kuma su ce wa mutane, “Ya tashi daga mattatu.” Kuma yaudarar karshe zata fi ta farko muni.”
So order the tomb to be made secure until the third day. Otherwise his disciples may come and steal him, and then say to the people “He has risen from the dead,” when the latest imposture will be worse than the first.’
65 Bilatus yace masu, “Ku dauki masu tsaro. Kuyi tsaro iyakar karfin ku.”
‘You may have a guard,’ was Pilate’s reply. ‘Go and make the tomb as secure as you can.’
66 Sai suka tafi suka tsare kabarin, suka hatimce dutsen, suka sa masu tsaro.
So they went and made the tomb secure, by sealing the stone, in presence of the guard.

< Mattiyu 27 >