< Giobbe 9 >

1 Giobbe rispose dicendo:
Sai Ayuba ya amsa,
2 In verità io so che è così: e come può un uomo aver ragione innanzi a Dio?
“Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
3 Se uno volesse disputare con lui, non gli risponderebbe una volta su mille.
Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
4 Saggio di mente, potente per la forza, chi s'è opposto a lui ed è rimasto salvo?
Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
5 Sposta le montagne e non lo sanno, egli nella sua ira le sconvolge.
Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
6 Scuote la terra dal suo posto e le sue colonne tremano.
Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
7 Comanda al sole ed esso non sorge e alle stelle pone il suo sigillo.
Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
8 Egli da solo stende i cieli e cammina sulle onde del mare.
Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
9 Crea l'Orsa e l'Orione, le Pleiadi e i penetrali del cielo australe.
Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
10 Fa cose tanto grandi da non potersi indagare, meraviglie da non potersi contare.
Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
11 Ecco, mi passa vicino e non lo vedo, se ne va e di lui non m'accorgo.
Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
12 Se rapisce qualcosa, chi lo può impedire? Chi gli può dire: «Che fai?».
Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
13 Dio non ritira la sua collera: sotto di lui sono fiaccati i sostenitori di Raab.
Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
14 Tanto meno io potrei rispondergli, trovare parole da dirgli!
“Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
15 Se avessi anche ragione, non risponderei, al mio giudice dovrei domandare pietà.
Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
16 Se io lo invocassi e mi rispondesse, non crederei che voglia ascoltare la mia voce.
Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
17 Egli con una tempesta mi schiaccia, moltiplica le mie piaghe senza ragione,
Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
18 non mi lascia riprendere il fiato, anzi mi sazia di amarezze.
Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
19 Se si tratta di forza, è lui che dà il vigore; se di giustizia, chi potrà citarlo?
In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
20 Se avessi ragione, il mio parlare mi condannerebbe; se fossi innocente, egli proverebbe che io sono reo.
Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
21 Sono innocente? Non lo so neppure io, detesto la mia vita!
“Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
22 Per questo io dico: «E' la stessa cosa»: egli fa perire l'innocente e il reo!
Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
23 Se un flagello uccide all'improvviso, della sciagura degli innocenti egli ride.
Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
24 La terra è lasciata in balìa del malfattore: egli vela il volto dei suoi giudici; se non lui, chi dunque sarà?
Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
25 I miei giorni passano più veloci d'un corriere, fuggono senza godere alcun bene,
“Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
26 volano come barche di giunchi, come aquila che piomba sulla preda.
Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
27 Se dico: «Voglio dimenticare il mio gemito, cambiare il mio volto ed essere lieto»,
‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
28 mi spavento per tutti i miei dolori; so bene che non mi dichiarerai innocente.
duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
29 Se sono colpevole, perché affaticarmi invano?
Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
30 Anche se mi lavassi con la neve e pulissi con la soda le mie mani,
Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
31 allora tu mi tufferesti in un pantano e in orrore mi avrebbero le mie vesti.
duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
32 Poiché non è uomo come me, che io possa rispondergli: «Presentiamoci alla pari in giudizio».
“Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
33 Non c'è fra noi due un arbitro che ponga la mano su noi due.
In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
34 Allontani da me la sua verga sì che non mi spaventi il suo terrore:
wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
35 allora io potrò parlare senza temerlo, perché così non sono in me stesso.
Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.

< Giobbe 9 >