< Salmi 148 >

1 Lodate il Signore dai cieli, lodatelo nell'alto dei cieli. Alleluia.
Yabi Ubangiji. Yabi Ubangiji daga sammai, yabe shi a bisa sammai.
2 Lodatelo, voi tutti, suoi angeli, lodatelo, voi tutte, sue schiere.
Yabe shi, dukanku mala’ikunsa, yabe shi, dukanku rundunarsa na sama.
3 Lodatelo, sole e luna, lodatelo, voi tutte, fulgide stelle.
Yabe shi, rana da wata, yabe shi, dukanku taurari masu haskakawa.
4 Lodatelo, cieli dei cieli, voi acque al di sopra dei cieli.
Yabe shi, ku bisa sammai da kuma ku ruwan bisa sarari.
5 Lodino tutti il nome del Signore, perché egli disse e furono creati.
Bari su yabi sunan Ubangiji, gama ya umarta aka kuwa halicce su.
6 Li ha stabiliti per sempre, ha posto una legge che non passa.
Ya sa su a wurarensu har abada abadin; ya ba da umarnin da ba zai taɓa shuɗe ba.
7 Lodate il Signore dalla terra, mostri marini e voi tutti abissi,
Yabi Ubangiji daga duniya, ku manyan halittun teku da kuma dukan zurfafan teku,
8 fuoco e grandine, neve e nebbia, vento di bufera che obbedisce alla sua parola,
walƙiya da ƙanƙara, dusar ƙanƙara da gizagizai, hadirin iskar da suke biyayya da umarnansa,
9 monti e voi tutte, colline, alberi da frutto e tutti voi, cedri,
ku duwatsu da dukan tuddai, itatuwa masu’ya’ya da dukan al’ul,
10 voi fiere e tutte le bestie, rettili e uccelli alati.
namun jeji da dukan dabbobin gida, ƙanana halittu da tsuntsaye masu firiya,
11 I re della terra e i popoli tutti, i governanti e i giudici della terra,
sarakunan duniya da dukan al’ummai, ku sarakuna da dukan masu mulkin duniya,
12 i giovani e le fanciulle, i vecchi insieme ai bambini
samari da’yan mata, tsofaffi da yara.
13 lodino il nome del Signore: perché solo il suo nome è sublime, la sua gloria risplende sulla terra e nei cieli.
Bari su yabi sunan Ubangiji, gama sunansa ne kaɗai mafi ɗaukaka; darajarsa ta fi ƙarfin duniya da sammai.
14 Egli ha sollevato la potenza del suo popolo. E' canto di lode per tutti i suoi fedeli, per i figli di Israele, popolo che egli ama. Alleluia.
Ya tayar wa mutanensa ƙaho, yabon dukan tsarkakansa, na Isra’ila, mutanen da suke kurkusa da zuciyarsa. Yabi Ubangiji.

< Salmi 148 >