< Salmi 119 >

1 BEATI coloro che sono intieri di via, Che camminano nella Legge del Signore.
Albarka ta tabbata ga waɗanda rayuwarsu ba ta da abin zargi, waɗanda suke tafiya bisa ga dokar Ubangiji.
2 Beati coloro che guardano le sue testimonianze, Che lo cercano con tutto il cuore;
Albarka ta tabbata ga waɗanda suke kiyaye ƙa’idodinsa suke kuma nemansa da dukan zuciyarsu.
3 [I quali] eziandio non operano iniquità; [Anzi] camminano nelle sue vie.
Ba sa yin wani abin da ba daidai ba; suna tafiya a hanyoyinsa.
4 Tu hai ordinato che i tuoi comandamenti Sieno strettamente osservati.
Ka shimfiɗa farillan da dole a yi biyayya da su.
5 Oh! sieno pure addirizzate le mie vie, Per osservare i tuoi statuti.
Kash, da a ce hanyoyina tsayayyu ne a yin biyayya da ƙa’idodinka mana!
6 Allora io non sarò svergognato, Quando io riguarderò a tutti i tuoi comandamenti.
Da ba zan sha kunya ba sa’ad da na lura da dukan umarnanka.
7 Io ti celebrerò con dirittura di cuore, Quando io avrò imparate le leggi della tua giustizia.
Zan yabe ka da zuciya ta gaskiya yayinda nake koyon dokokinka masu adalci.
8 Io osserverò i tuoi statuti; Non abbandonarmi del tutto.
Zan yi biyayya da ƙa’idodinka; kada ka yashe ni ɗungum.
9 Come renderà il fanciullo la sua via pura? Prendendo guardia [ad essa] secondo la tua parola.
Yaya matashi zai kiyaye hanyarsa da tsabta? Sai ta yin rayuwa bisa ga maganarka.
10 Io ti ho cercato con tutto il mio cuore; Non lasciarmi deviar da' tuoi comandamenti.
Na neme ka da dukan zuciyata; kada ka bar ni in kauce daga umarnanka.
11 Io ho riposta la tua parola nel mio cuore; Acciocchè io non pecchi contro a te.
Na ɓoye maganarka a cikin zuciyata don kada in yi maka zunubi.
12 Tu [sei] benedetto, o Signore; Insegnami i tuoi statuti.
Yabo ya tabbata gare ka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
13 Io ho colle mie labbra raccontate Tutte le leggi della tua bocca.
Da leɓunana na ba da labarin dukan dokokin da suka fito bakinka.
14 Io gioisco nella via delle tue testimonianze, Come per tutte le ricchezze [del mondo].
Na yi farin ciki da bin farillanka yadda mutum yakan yi farin ciki da arziki mai yawa.
15 Io ragiono de' tuoi comandamenti, E riguardo a' tuoi sentieri.
Na yi tunani a kan farillanka na kuma lura da hanyoyinka.
16 Io mi diletto ne' tuoi statuti; Io non dimenticherò le tue parole.
Na yi murna a cikin ƙa’idodinka; ba zan ƙyale maganarka ba.
17 Fa' del bene al tuo servitore, Ed io viverò, ed osserverò la tua parola.
Ka yi alheri ga bawanka, zan kuwa rayu; zan yi biyayya da maganarka.
18 Apri gli occhi miei, ed io riguarderò Le maraviglie della tua Legge.
Ka buɗe idanuna don in iya gani abubuwan banmamaki a cikin dokarka.
19 Io [son] forestiere in terra; Non nascondermi i tuoi comandamenti.
Ni baƙo ne a duniya; kada ka ɓoye mini umarnanka.
20 L'anima mia si stritola di affezione Alle tue leggi in ogni tempo.
Zuciyata ta ƙosa saboda marmari don dokokinka koyaushe.
21 Tu sgridi i superbi maledetti Che deviano da' tuoi comandamenti.
Ka tsawata wa masu fariya, waɗanda suke la’anta waɗanda kuma suka kauce daga umarnanka.
22 Togli d'addosso a me il vituperio e lo sprezzo; Perciocchè io ho guardate le tue testimonianze.
Ka cire mini ba’a da reni, gama ina kiyaye farillanka.
23 Eziandio, [mentre] i principi sedevano, e ragionavano contro a me, Il tuo servitore ha meditato ne' tuoi statuti.
Ko da yake masu mulki sun zauna tare suna ɓata mini suna, bawanka zai yi tunani a kan ƙa’idodinka.
24 Ed anche le tue testimonianze [sono] i miei diletti [Ed] i miei consiglieri.
Farillanka ne abin farin cikina; su ne mashawartana.
25 L'anima mia è attaccata alla polvere; Vivificami secondo la tua parola.
An kwantar da ni ƙasa cikin ƙura; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
26 Io [ti] ho narrate le mie vie, e tu mi hai risposto; Insegnami i tuoi statuti.
Na ba da labari hanyoyina ka kuma amsa mini; ka koya mini ƙa’idodinka.
27 Fammi intender la via de' tuoi comandamenti, Ed io ragionerò delle tue maraviglie.
Bari in gane koyarwar farillanka; sa’an nan zan yi tunani a kan abubuwan banmamakinka.
28 L'anima mia stilla di cordoglio; Sollevami secondo le tue parole.
Raina ya gaji da baƙin ciki; ka ƙarfafa ni bisa ga maganarka.
29 Rimuovi da me la via della menzogna; E fammi dono della tua Legge.
Ka kiyaye ni daga hanyoyin ruɗu; ka yi mini alheri ta wurin dokokinka.
30 Io ho scelta la via della verità; Io [mi] son proposte le tue leggi.
Na zaɓi hanyar gaskiya; na sa zuciyata a kan dokokinka.
31 Io mi son tenuto alle tue testimonianze; Signore, non lasciar che io sia confuso.
Na riƙe farillanka kankan, ya Ubangiji; kada ka sa in sha kunya.
32 Correrò nella via de' tuoi comandamenti, Quando tu mi avrai allargato il cuore.
Ina gudu a kan hanyar umarnanka, gama ka’yantar da zuciyata.
33 Insegnami, Signore, la via de' tuoi statuti; Ed io la guarderò [infino] al fine.
Ka koya mini Ya Ubangiji, don in bi ƙa’idodinka; sa’an nan zan kiyaye su har ƙarshe.
34 Dammi intelletto, ed io guarderò la tua Legge; E l'osserverò con tutto il cuore.
Ka ba ni ganewa, zan kuwa kiyaye dokarka in kuma yi biyayya da ita da dukan zuciyata.
35 Conducimi per lo sentiero de' tuoi comandamenti; Perciocchè io mi diletto in esso.
Ka bi da ni a hanyar umarnanka, gama a can zan sami farin ciki.
36 Inchina il mio cuore alle tue testimonianze, E non a cupidigia.
Ka juye zuciyata wajen farillanka ba wajen riba ta sonkai ba.
37 Storna gli occhi miei, che non riguardino a vanità; Vivificami nelle tue vie.
Ka juye idanuna daga abubuwa marasa amfani; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
38 Attieni la tua parola al tuo servitore, Il quale [è tutto] intento al tuo timore.
Ka cika alkawarinka ga bawanka, saboda a ji tsoronka.
39 Rimuovi [da me] il mio vituperio, del quale io temo; Perciocchè le tue leggi [son] buone.
Ka kawar da shan kunyar da nake tsoro, gama dokokinka nagari ne.
40 Ecco, io desidero affettuosamente i tuoi comandamenti; Vivificami nella tua giustizia.
Ina marmarin farillanka ƙwarai! Ka kiyaye raina cikin adalcinka.
41 Ed avvenganmi le tue benignità, o Signore; [E] la tua salute, secondo la tua parola.
Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zo gare ni, ya Ubangiji, cetonka bisa ga alkawarinka;
42 Ed io risponderò a colui che mi fa vituperio; Perciocchè io mi confido nella tua parola.
sa’an nan zan amsa wa masu cin mutuncina, gama na dogara ga maganarka.
43 E non ritrarmi del tutto dalla bocca la parola della verità; Perciocchè io spero nelle tue leggi.
Kada ka ƙwace maganarka daga bakina, gama na sa zuciyata a dokokinka.
44 Ed io osserverò la tua Legge del continuo, In sempiterno.
Kullayaumi zan yi biyayya da dokokinka, har abada abadin.
45 E camminerò al largo; Perciocchè io ho ricercati i tuoi comandamenti.
Zan yi ta yawo a sake gama na nemi farillanka.
46 E parlerò delle tue testimonianze davanti ai re, E non sarò svergognato.
Zan yi maganar farillanka a gaban sarakuna ba kuwa za a kunyata ni ba,
47 E mi diletterò ne' tuoi comandamenti, I quali io amo.
gama ina farin ciki da umarnanka saboda ina ƙaunarsu.
48 Ed alzerò le palme delle mie mani a' tuoi comandamenti, i quali io amo; E mediterò ne' tuoi statuti.
Na ɗaga hannuwana ga umarnanka, waɗanda nake ƙauna, ina kuma tunani a kan ƙa’idodinka.
49 Ricordati della parola [detta] al tuo servitore, Sopra la quale tu mi hai fatto sperare.
Tuna da maganarka ga bawanka, gama ka ba ni bege.
50 Questa [è] la mia consolazione nella mia afflizione, Che la tua parola mi ha vivificato.
Ta’aziyyata cikin wahalata ita ce alkawarinka yana kiyaye raina.
51 I superbi mi hanno grandemente schernito; [Ma] io non mi sono stornato dalla tua Legge.
Masu fariya suna yi mini ba’a ba tare da an hana su ba, amma ban rabu da dokar ba.
52 Signore, io mi son ricordato de' tuoi giudicii ab antico; E mi son consolato.
Na tuna da dokokinka na tun dā, ya Ubangiji, na kuwa sami ta’aziyya a cikinsu.
53 Tremito mi occupa, per gli empi Che abbandonano la tua Legge.
Fushi ya kama ni saboda mugaye, waɗanda suka keta dokokinka.
54 I tuoi statuti sono stati i miei cantici Nella dimora de' miei pellegrinaggi.
Ƙa’idodinka su ne kan waƙata a duk inda na sauka.
55 O Signore, di notte io mi son ricordato del tuo Nome, Ed ho osservata la tua Legge.
Da dare na tuna da sunanka, ya Ubangiji, zan kuwa kiyaye dokarka.
56 Questo mi è avvenuto, Perciocchè io ho guardati i tuoi comandamenti.
Wannan shi ne na saba yi, ina yin biyayya da farillanka.
57 Il Signore [è] la mia parte; Io ho detto di osservare le tue parole.
Kai ne rabona, ya Ubangiji; na yi alkawarin in kiyaye maganarka.
58 Io ti ho supplicato con tutto il cuore; Abbi pietà di me, secondo la tua parola.
Na nemi fuskarka da dukan zuciyata; ka yi mini alheri bisa ga alkawarinka.
59 Io ho fatta ragione delle mie vie; Ed ho rivolti i miei piedi alle tue testimonianze.
Na lura da hanyoyina na kuma mayar da matakaina ga farillanka.
60 Io mi sono affrettato, e non mi sono indugiato D'osservare i tuoi comandamenti.
Zan gaggauta ba zan ɓata lokaci ba in yi biyayya da umarnanka.
61 Schiere d'empi mi hanno predato; [Ma però] non ho dimenticata la tua Legge.
Ko da yake mugaye sun ɗaura ni da igiyoyi, ba zan manta da dokokinka ba.
62 Io mi levo a mezzanotte, per celebrarti, Per le leggi della tua giustizia.
Da tsakar dare nakan tashi in gode maka saboda dokokinka masu adalci.
63 Io [son] compagno di tutti quelli che ti temono, Ed osservano i tuoi comandamenti.
Ni aboki ne ga duk mai tsoronka, ga duk wanda yake bin farillanka.
64 Signore, la terra è piena della tua benignità; Insegnami i tuoi statuti.
Duniya ta cika da ƙaunarka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
65 Signore, tu hai usata beneficenza inverso il tuo servitore, Secondo la tua parola.
Ka yi wa bawanka alheri bisa ga maganarka, ya Ubangiji.
66 Insegnami buon senno ed intendimento; Perciocchè io credo a' tuoi comandamenti.
Ka koya mini sani da kuma hukunci mai kyau, gama na gaskata a umarnanka.
67 Avanti che io fossi afflitto, io andava errando; Ma ora osservo la tua parola.
Kafin in sha wahala na kauce, amma yanzu ina biyayya da maganarka.
68 Tu [sei] buono e benefattore; Insegnami i tuoi statuti.
Kai nagari ne, kuma abin da kake yi yana da kyau; ka koya mini ƙa’idodinka.
69 I superbi hanno acconciate delle bugie contro a me; [Ma] io con tutto il cuore guarderò i tuoi comandamenti.
Ko da yake masu fariya sun shafe ni da ƙarairayi, na kiyaye farillanka da dukan zuciyata.
70 Il cuor loro è condenso come grasso; [Ma] io mi diletto nella tua Legge.
Zukatansu sun yi tauri da kuma marasa tausayi amma ina farin ciki a dokarka.
71 Egli [è stato] buono per me, che io sono stato afflitto; Acciocchè io impari i tuoi statuti.
Ya yi kyau da na sha wahala don in koyi ƙa’idodinka.
72 La Legge della tua bocca mi [è] migliore Che le migliaia d'oro e d'argento.
Doka daga bakinka ya fi mini daraja fiye da azurfa da zinariya guda dubu.
73 Le tue mani mi hanno fatto e formato; Dammi intelletto, ed io imparerò i tuoi comandamenti.
Hannuwanka ne suka yi suka kuma siffanta ni; ka ba ni ganewa don in koyi umarnanka.
74 Quelli che ti temono mi vedranno, e si rallegreranno; Perciocchè io ho sperato nella tua parola.
Bari waɗanda suke tsoronka su yi farin ciki sa’ad da suke gan ni, gama na sa zuciyata a maganarka.
75 O Signore, io so che i tuoi giudicii [non sono altro che] giustizia; E [che ciò che] mi hai afflitto [è stato] fedeltà.
Ya Ubangiji na sani, cewa dokokinka masu adalci ne, kuma cikin aminci ka hore ni.
76 Deh! [sia] la tua benignità per consolarmi, Secondo la tua parola, [detta] al tuo servitore.
Bari ƙaunarka marar ƙarewa tă yi mini ta’aziyya, bisa ga alkawarinka ga bawanka.
77 Avvenganmi le tue misericordie, acciocchè io viva; Perciocchè la tua Legge [è] ogni mio diletto.
Bari tausayinka yă zo mini don in rayu, gama dokarka ce farin cikina.
78 Sien confusi i superbi, perciocchè a torto mi sovvertono; [Ma] io medito ne' tuoi comandamenti.
Bari masu girman kai su sha kunya saboda abubuwa marasa kyau da suke yi mini ba dalili; amma zan yi tunani a kan farillanka.
79 Rivolgansi a me quelli che ti temono. E quelli che conoscono le tue testimonianze.
Bari waɗanda suke tsoronka su juya gare ni, waɗanda suka gane da farillanka.
80 Sia il mio cuore intiero ne' tuoi statuti; Acciocchè io non sia confuso.
Bari zuciyata ta kasance marar abin zargi wajen ƙa’idodinka, don kada in sha kunya.
81 L'anima mia vien meno dietro alla tua salute; Io spero nella tua parola.
Raina ya tafke da marmari don cetonka, amma na sa zuciyata a maganarka.
82 Gli occhi miei vengono meno dietro alla tua parola, Dicendo: Quando mi consolerai tu?
Idanuna sun gaji, suna jiran alkawarinka; Na ce, “Yaushe za ka ta’azantar da ni?”
83 Perciocchè io son divenuto come un otro al fumo; E [pur] non ho dimenticati i tuoi statuti.
Ko da yake ni kamar salkar ruwan inabi ne a cikin hayaƙi, ban manta da ƙa’idodinka ba.
84 Quanti [hanno da essere] i giorni del tuo servitore? Quando farai giudicio sopra quelli che mi perseguitano?
Har yaushe bawanka zai yi ta jira? Yaushe za ka hukunta masu tsananta mini?
85 I superbi mi hanno cavate delle fosse; Il che non [è] secondo la tua Legge.
Masu girman kai sun haƙa mini rami, sun ƙetare dokarka.
86 Tutti i tuoi comandamenti [son] verità; Essi mi perseguitano a torto; soccorrimi.
Dukan umarnanka abin dogara ne; ka taimake ni, gama mutane suna tsananta mini ba dalili.
87 Mi hanno pressochè distrutto ed atterrato; [Ma] io non ho abbandonati i tuoi comandamenti.
Sun kusa gama da ni a duniya, amma ban bar bin farillanka ba.
88 Vivificami secondo la tua benignità, Ed io osserverò la testimonianza della tua bocca.
Ka kiyaye raina bisa ga ƙaunarka, zan kuwa yi biyayya da farillan bakinka.
89 O Signore, la tua parola [è] in eterno; Ella è stabile ne' cieli.
Maganarka, ya Ubangiji madawwamiya ce; tana nan daram a cikin sammai.
90 La tua verità [è] per ogni età; Tu hai stabilita la terra, ed ella sta ferma.
Amincinka yana cin gaba cikin dukan zamanai; ka kafa duniya ta kuma dawwama.
91 [Il cielo e la terra] stanno anche oggi fermi, per li tuoi ordini, Perciocchè ogni cosa [è] al tuo servigio.
Dokokinka sun dawwama har yă zuwa yau, gama dukan abubuwa suna maka hidima.
92 Se la tua Legge [non fosse stata] ogni mio diletto, Io già sarei perito nella mia afflizione.
Da ba don dokarka ce farin cikina ba, da na hallaka a cikin azabana.
93 Giammai non dimenticherò i tuoi comandamenti; Perciocchè per essi tu mi hai vivificato.
Ba zan taɓa manta da farillanka ba, gama ta wurinsu ne ka kiyaye raina.
94 Io [son] tuo, salvami; Perciocchè io ho ricercati i tuoi comandamenti.
Ka cece ni, gama ni naka ne; na yi ƙoƙarin neman farillanka.
95 Gli empi mi hanno atteso, per farmi perire; [Ma] io ho considerate le tue testimonianze.
Mugaye suna jira su hallaka ni, amma zan yi ta tunani a kan farillanka.
96 Io ho veduto che tutte le cose le più perfette hanno fine; Ma il tuo comandamento [è] d'una grandissima distesa.
Ga duk cikakke na ga kāsawa; amma umarnanka ba su da iyaka.
97 Oh! quanto amo la tua Legge! Ella [è] la mia meditazione di tutti i giorni.
Kash, ga yadda nake ƙaunar dokarka! Ina tunani a kanta dukan yini.
98 [Per] li tuoi comandamenti tu mi rendi più savio che i miei nemici; Perciocchè [quelli] in perpetuo [sono] miei.
Umarnanka suna sa in zama mai hikima fiye da abokan gābana, gama kullum suna tare da ni.
99 Io son più intendente che tutti i miei dottori; Perciocchè le tue testimonianze [son] la mia meditazione.
Ina da ganewa sosai fiye da dukan malamaina, gama ina tunani a kan farillanka.
100 Io son più avveduto che i vecchi; Perciocchè io ho guardati i tuoi comandamenti.
Ina da ganewa fiye da dattawa, gama ina biyayya da farillanka.
101 Io ho rattenuti i miei piedi da ogni sentiero malvagio; Acciocchè io osservi la tua parola.
Na kiyaye ƙafafuna daga kowace muguwar hanya domin in yi biyayya da maganarka.
102 Io non mi sono stornato dalle tue leggi; Perciocchè tu mi hai ammaestrato.
Ban rabu da dokokinka ba, gama kai da kanka ne ka koya mini.
103 Oh! quanto son dolci le tue parole al mio palato! [Son più dolci] che miele alla mia bocca.
Ɗanɗanon maganarka akwai zaki, sun ma fi zuma zaki a bakina!
104 Io son divenuto avveduto per li tuoi comandamenti; Perciò, odio ogni sentiero di falsità.
Na sami ganewa daga farillanka; saboda haka ina ƙin kowace hanyar da ba daidai ba.
105 La tua parola [è] una lampana al mio piè, Ed un lume al mio sentiero.
Maganarka fitila ce ga ƙafafuna haske kuma a kan hanyata.
106 Io ho giurato, e l'atterrò, Di osservare le leggi della tua giustizia.
Na yi rantsuwa na kuma tabbatar da shi, cewa zan bi dokokinka masu adalci.
107 Io son sommamente afflitto; O Signore, vivificami secondo la tua parola.
Na sha wahala sosai; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga maganarka.
108 Deh! Signore, gradisci le offerte volontarie della mia bocca, Ed insegnami le tue leggi.
Ka karɓi yabon bakina da nake yi da yardar rai, ya Ubangiji, ka kuwa koya mini dokokinka.
109 Io ho l'anima mia del continuo in palma di mano; E pur non ho dimenticata la tua Legge.
Ko da yake kullum ina riƙe da raina a hannuwana, ba zan manta da dokarka ba.
110 Gli empi mi hanno tesi de' lacci; E pur non mi sono sviato da' tuoi comandamenti.
Mugaye sun kafa mini tarko, amma ban kauce daga farillanka ba.
111 Le tue testimonianze [son] la mia eredità in perpetuo; Perciocchè esse [son] la letizia del mio cuore.
Farillanka su ne gādona har abada; su ne farin cikin zuciyata.
112 Io ho inchinato il mio cuore a mettere in opera i tuoi statuti, In perpetuo, infino al fine.
Zuciyata ta shirya a kan kiyaye ƙa’idodinka har ƙarshe.
113 Io odio i discorsi; Ma amo la tua Legge.
Na ƙi mutane masu baki biyu, amma ina ƙauna dokarka.
114 Tu [sei] il mio nascondimento, ed il mio scudo; Io spero nella tua parola.
Kai ne mafakata da garkuwata; na sa zuciyata a maganarka.
115 Ritraetevi da me, maligni; Ed io guarderò i comandamenti del mio Dio.
Ku rabu da ni, ku masu aikata mugunta, don in kiyaye umarnan Allahna!
116 Sostienmi, secondo la tua parola, ed io viverò; E non rendermi confuso della mia speranza.
Ka raya ni bisa ga alkawarinka, zan kuwa rayu; kada ka bari a gwale sa zuciyata.
117 Confortami, ed io sarò salvato; E riguarderò del continuo a' tuoi statuti.
Ka riƙe ni za a kuma cece ni; kullayaumi zan ɗauka ƙa’idodinka da muhimmanci.
118 Tu calpesti tutti quelli che si sviano da' tuoi statuti; Perciocchè la lor frode [è] una cosa falsa.
Ka ki dukan waɗanda suka kauce daga ƙa’idodinka, gama yaudararsu banza ne.
119 Tu riduci al niente tutti gli empi della terra, [come] schiume; Perciò io amo le tue testimonianze.
Dukan mugayen duniya ka zubar kamar datti; saboda haka nake ƙaunar farillanka.
120 La mia carne si raccapriccia tutta per lo spavento di te; Ed io temo de' tuoi giudicii.
Naman jikina na rawan jiki don tsoronka; na cika da tsoron dokokinka.
121 Io ho fatto ciò che è diritto e giusto; Non abbandonarmi a quelli che mi oppressano.
Na aikata abin da yake mai adalci da kuma daidai; kada ka ni a hannun masu danne ni.
122 Da' sicurtà per lo tuo servitore in bene, [E] non [lasciar] che i superbi mi oppressino.
Ka tabbatar da lafiyar bawanka; kada ka bar masu girman kai su danne ni.
123 Gli occhi miei vengono meno dietro alla tua salute, Ed alla parola della tua giustizia.
Idanuna sun gaji, da jiran cetonka, da jiran alkawarinka mai adalci.
124 Opera inverso il tuo servitore secondo la tua benignità, Ed insegnami i tuoi statuti.
Ka yi da bawanka bisa ga ƙaunarka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
125 Io [son] tuo servitore; dammi intelletto; Acciocchè io possa conoscere le tue testimonianze.
Ni bawanka ne, ka ba ni fahimi don in gane farillanka.
126 [Egli è] tempo che il Signore operi; Essi hanno annullata la tua Legge.
Lokaci ya yi da za ka yi wani abu, ya Ubangiji; ana karya dokarka.
127 Perciò io amo i tuoi comandamenti più che oro; Anzi più che oro finissimo.
Saboda ina ƙaunar umarnanka fiye da zinariya, kai, fiye da zinariya zalla,
128 Perciò approvo, come diritti, tutti i tuoi comandamenti intorno ad ogni cosa; [Ed] odio ogni sentiero di menzogna.
saboda kuma ina lura da dukan farillanka da kyau, na ƙi kowace hanyar da ba daidai ba.
129 Le tue testimonianze [son] cose maravigliose; Perciò l'anima mia le ha guardate.
Farillanka masu banmamaki ne; saboda haka nake yin biyayya da su.
130 La dichiarazione delle tue parole allumina, [E] dà intelletto a' semplici.
Fassarar maganganunka sukan ba da haske; sukan ba da ganewa ga marar ilimi.
131 Io ho aperta la bocca, ed ho ansato; Perciocchè io ho bramati i tuoi comandamenti.
Ina hakkin da bakina a buɗe, ina marmarin umarnanka.
132 Riguarda a me, ed abbi pietà di me, Secondo ch'è ragionevole [di fare] inverso quelli che amano il tuo Nome.
Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, yadda kullum ka yi wa waɗanda suke ƙaunar sunanka.
133 Ferma i miei passi nella tua parola; E non [lasciare] che alcuna iniquità signoreggi sopra me.
Ka bi da sawuna bisa ga maganarka; kada ka bar zunubi yă mallake ni.
134 Riscuotimi dall'oppressione degli uomini; Ed io osserverò i tuoi comandamenti.
Ka fanshe ni daga mutane masu danniya, don in yi biyayya da farillanka.
135 Fa' rilucere il tuo volto sopra il tuo servitore;
Ka sa fuskarka ta haskaka a kan bawanka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
136 Ed insegnami i tuoi statuti. Ruscelli d'acque mi scendono giù dagli occhi; Perciocchè la tua Legge non è osservata.
Hawaye suna malalowa daga idanuna kamar rafi, gama ba a biyayya da dokarka.
137 O Signore, tu [sei] giusto, E i tuoi giudicii [son] diritti.
Mai adalci ne kai, ya Ubangiji, dokokinka kuma daidai ne.
138 Tu hai strettamente comandata la giustizia, E la verità delle tue testimonianze.
Farillan da ka shimfiɗa masu adalci ne; su kuma abin dogara ne ƙwarai.
139 Il mio zelo mi consuma; Perciocchè i miei nemici hanno dimenticate le tue parole.
Kishina ya cinye ni ɗungum, gama abokan gābana sun yi biris da maganganunka.
140 La tua parola [è] sommamente purgata; E però il tuo servitore l'ama.
An gwada alkawuranka sarai, bawanka kuwa yana ƙaunarsu.
141 Io [son] piccolo e sprezzato; [Ma però] non ho dimenticati i tuoi comandamenti.
Ko da yake ni ba kome ba ne an kuwa rena ni, ba na manta da farillanka.
142 La tua giustizia [è] una giustizia eterna, E la tua Legge [è] verità.
Adalcinka dawwammame ne dokar kuma gaskiya ce.
143 Tribolazione e distretta mi hanno colto; [Ma] i tuoi comandamenti [sono] i miei diletti.
Wahala da damuwa suna a kaina, amma umarnanka su ne farin cikina.
144 Le tue testimonianze sono una giustizia eterna; Dammi intelletto, ed io viverò.
Farillanka daidai ne har abada; ka ba ni ganewa don in rayu.
145 Io ho gridato con tutto il cuore; rispondimi, Signore; [Ed] io guarderò i tuoi statuti.
Na yi kira da dukan zuciyata; ka amsa mini, ya Ubangiji, zan kuwa yi biyayya da ƙa’idodinka.
146 Io ti ho invocato; salvami, Ed io osserverò le tue testimonianze.
Na yi kira gare ka; ka cece ni zan kuwa kiyaye farillanka.
147 Io mi son fatto avanti all'alba, ed ho gridato; Io ho sperato nella tua parola.
Na tashi kafin fitowar rana na kuma yi kukan neman taimako; na sa zuciyata a maganarka.
148 Gli occhi miei prevengono le vigilie [della notte]. Per meditar nella tua parola.
Ban rufe idanuna ba dukan dare, don in yi tunani a kan alkawuranka.
149 Ascolta la mia voce, secondo la tua benignità; O Signore, vivificami, secondo che tu hai ordinato.
Ka ji muryata bisa ga ƙaunarka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga dokokinka.
150 Quelli che vanno dietro a scelleratezza, E si sono allontanati dalla tua Legge, si sono accostati [a me].
Waɗanda suke ƙirƙiro mugayen dabaru suna nan kusa, amma suna nesa da dokarka.
151 O Signore, tu [sei] vicino; E tutti i tuoi comandamenti [son] verità.
Duk da haka kana kusa, ya Ubangiji, kuma dukan umarnanka gaskiya ne.
152 Gran tempo è che io so [questo] delle tue testimonianze, Che tu le hai stabilite in eterno.
Tun tuni na koyi daga farillanka cewa ka kafa su su kasance har abada.
153 Riguarda alla mia afflizione, e tramme[ne] fuori; Perciocchè io non ho dimenticata la tua Legge.
Ka dubi wahalata ka cece ni, gama ban manta da dokarka ba.
154 Dibatti la mia lite, e riscuotimi; Vivificami, secondo la tua parola.
Ka kāre manufata ka kuma fanshe ni, ka cece rai na kamar yadda ka alkawarta!
155 La salute [è] lungi dagli empi; Perciocchè non ricercano i tuoi statuti.
Ceto yana nesa da mugaye, gama ba sa neman ƙa’idodinka.
156 Le tue misericordie [son] grandi, Signore; Vivificami secondo ciò che hai ordinato.
Tausayinka da girma yake, ya Ubangiji; ka kiyaye raina bisa ga dokokinka.
157 I miei persecutori ed i miei nemici [son] molti; [Ma] io non mi sono deviato dalle tue testimonianze.
Maƙiya masu yawa ne suke tsananta mini, amma ban rabu da farillanka ba.
158 Io ho veduti i disleali, e ne ho sentita gran noia; Perciocchè non osservano la tua parola.
Na dubi marasa aminci da ƙyama, gama ba sa yin biyayya da maganarka.
159 Vedi quanto amo i tuoi comandamenti! Signore, vivificami, secondo la tua benignità.
Dubi yadda nake ƙaunar farillanka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga ƙaunarka.
160 La somma della tua parola [è] verità; E tutte le leggi della tua giustizia [sono] in eterno.
Dukan maganganunka gaskiya ne; dukan dokokinka masu adalci madawwami ne.
161 I principi m'hanno perseguitato senza cagione; Ma il mio cuore ha spavento della tua parola.
Masu mulki suna tsananta mini ba dalili, amma zuciyata na rawan jiki game da maganarka.
162 Io mi rallegro per la tua parola, Come una persona che avesse trovate grandi spoglie.
Ina farin ciki da alkawarinka kamar yadda wani kan sami ganima mai girma.
163 Io odio ed abbomino la menzogna; [Ma] io amo la tua Legge.
Na ƙi ina kuma ƙyamar ƙarya amma ina ƙaunar dokarka.
164 Io ti lodo sette volte il dì, Per li giudicii della tua giustizia.
Sau bakwai a rana ina yabonka saboda dokokinka masu adalci.
165 Quelli che amano la tua Legge godono di molta pace; E non [vi è] alcuno intoppo per loro.
Waɗanda suke ƙaunar dokarka suna da babban salama, kuma babu abin da zai sa su yi tuntuɓe.
166 Signore, io ho sperato nella tua salute; Ed ho messi in opera i tuoi comandamenti.
Ina jiran cetonka, ya Ubangiji, ina kuma bin umarnanka.
167 L'anima mia ha osservate le tue testimonianze; Ed io le ho grandemente amate.
Ina biyayya da farillanka, gama ina ƙaunarsu ƙwarai.
168 Io ho osservati i tuoi comandamenti, e le tue testimonianze; Perciocchè tutte le mie vie [sono] nel tuo cospetto.
Ina biyayya da farillanka da kuma koyarwarka, gama dukan hanyoyina sanannu ne gare ka.
169 Pervenga il mio grido al tuo cospetto, o Signore; Dammi intelletto, secondo la tua parola.
Bari kukata ta zo gare ka, ya Ubangiji; ka ba ni ganewa bisa ga maganarka.
170 Venga la mia supplicazione in tua presenza; Riscuotimi, secondo la tua parola.
Bari roƙona yă zo gabanka; ka cece ni bisa ga alkawarinka.
171 Le mie labbra sgorgheranno lode, Quando tu mi avrai insegnati i tuoi statuti.
Bari leɓunana su cika da yabonka, gama ka koya mini ƙa’idodinka.
172 La mia lingua ragionerà della tua parola; Perciocchè tutti i tuoi comandamenti [son] giustizia.
Bari harshena yă rera game da maganarka, gama dukan umarnanka masu adalci ne.
173 Siami in aiuto la tua mano; Perciocchè io ho eletti i tuoi comandamenti.
Bari hannunka yă kasance a shirye don yă taimake ni, gama na zaɓi farillanka.
174 Signore, io ho desiderata la tua salute; E la tua Legge [è] ogni mio diletto.
Ina marmarin cetonka, ya Ubangiji, dokarka kuwa ita ce farin cikina.
175 Viva l'anima mia, ed ella ti loderà; E soccorranmi i tuoi ordinamenti.
Bari in rayu don in yabe ka, bari kuma dokokinka su raya ni.
176 Io vo errando, come una pecora smarrita; cerca il tuo servitore; Perciocchè io non ho dimenticati i tuoi comandamenti.
Na kauce kamar ɓatacciyar tunkiya. Ka nemi bawanka, gama ban manta da umarnanka ba.

< Salmi 119 >