< Salmi 74 >

1 Maschil di Asaf O DIO, perchè [ci] hai scacciati in perpetuo? [Perchè] fuma l'ira tua contro alla greggia del tuo pasco?
Maskil na Asaf. Me ya sa ka ƙi mu har abada, ya Allah? Me ya sa fushinka yake a kan tumakin kiwonka?
2 Ricordati della tua raunanza, [la quale] tu acquistasti anticamente; Della tribù della tua eredità [che] tu riscotesti; Del monte di Sion, nel quale tu abitasti.
Ka tuna da mutanen da ka saya tun da daɗewa, kabilar gādonka, wadda ka fansa, Dutsen Sihiyona, inda ka zauna.
3 Muovi i passi verso le ruine perpetue, [Verso] tutto il male [che] i nemici han fatto nel [luogo] santo.
Ka juye sawunka wajen waɗannan madawwamin kufai, dukan wannan hallakar da abokin gāba ya yi wa wuri mai tsarki.
4 I tuoi nemici han ruggito in mezzo del tuo Tempio; [Vi] hanno poste le loro insegne [per] segnali.
Maƙiyanka sun yi ruri a inda ka sadu da mu; suka kakkafa tutotinsu a matsayin alamu.
5 [Ciò] sarà noto; come chi, [levando] ad alto delle scuri, Le avventa contro a un cespo di legne;
Sun yi kamar mutane masu wāshin gatura don yanka itatuwa a kurmi.
6 Così ora hanno essi, con iscuri e martelli, Fracassati tutti quanti gl'intagli di quello.
Sun ragargaje dukan sassaƙar katako da gatura da kuma gudumarsu.
7 Hanno messi a fuoco e fiamma i tuoi santuari, Hanno profanato il tabernacolo del tuo Nome, [gettandolo] per terra.
Suka ƙone wurinka mai tsarki ƙurmus; suka ƙazantar da mazaunin Sunanka.
8 Hanno detto nel cuor loro: Prediamoli tutti quanti; Hanno arsi tutti i luoghi delle raunanze di Dio in terra.
Suna cewa a zukatansu, “Za mu murƙushe su sarai!” Suka ƙone ko’ina aka yi wa Allah sujada a ƙasar.
9 Noi non veggiam [più] i nostri segni; Non [vi è] più profeta, E non abbiam con noi alcuno che sappia infino a quando.
Ba a ba mu wata alama mai banmamaki ba; ba sauran annabawan da suka ragu, kuma babu waninmu da ya sani har yaushe wannan zai ci gaba.
10 Infino a quando, o Dio, oltraggerà l'avversario? Il nemico dispetterà egli il tuo Nome in perpetuo?
Har yaushe abokan gāba za su yi mana ba’a, ya Allah? Maƙiya za su ci gaba da ɓata sunanka har abada ne?
11 Perchè ritiri la tua mano e la tua destra? Non lasciare ch'ella ti dimori più dentro al seno.
Me ya sa ka janye hannunka, hannunka na dama? Ka fid da shi daga rigarka ka hallaka su!
12 Ora Iddio già ab antico [è] il mio Re. Il quale opera salvazioni in mezzo della terra.
Amma kai, ya Allah, kai ne sarki tun da daɗewa; ka kawo ceto a kan duniya.
13 Tu, colla tua forza, spartisti il mare; Tu rompesti le teste delle balene nelle acque.
Kai ne ka raba teku ta wurin ikonka; ka farfashe kawunan dodo a cikin ruwaye.
14 Tu fiaccasti i capi del leviatan, E li desti per pasto al popolo de' deserti.
Kai ne ka murƙushe kawunan dodon ruwa ka kuma ba da shi yă zama abinci ga halittun hamada.
15 Tu facesti scoppiar fonti e torrenti; Tu seccasti fiumi grossi.
Kai ne ka bubbuɗe maɓulɓulai da rafuffuka; ka busar da koguna masu ruwa.
16 Tuo [è] il giorno, tua eziandio [è] la notte; Tu hai ordinata la luna e il sole.
Yini naka ne, dare kuma naka ne; ka kafa rana da wata.
17 Tu hai posti tutti i termini della terra; Tu hai formata la state ed il verno.
Kai ne ka kafa dukan iyakokin duniya; ka yi rani da damina.
18 Ricordati di questo: che il nemico ha oltraggiato il Signore, E che il popolo stolto ha dispettato il tuo Nome.
Ka tuna da yadda abokin gāba ya yi maka ba’a, ya Ubangiji, yadda wawaye suka ɓata sunanka.
19 Non dare alle fiere la vita della tua tortola; Non dimenticare in perpetuo la raunanza de' tuoi poveri afflitti.
Kada ka ba da ran kurciyarka ga namun jeji; kada ka manta har abada da rayukan mutanenka masu shan azaba.
20 Riguarda al Patto, Perciocchè i luoghi tenebrosi della terra sono ripieni di ricetti di violenza.
Ka kula da alkawarinka, domin akwai tashin hankali a kowane lungu mai duhu na ƙasar.
21 Non ritornisene il misero indietro svergognato; [Fa' che] il povero afflitto e il bisognoso lodino il tuo Nome.
Kada ka bar waɗanda ake danniya su sha kunya; bari matalauta da mabukata su yabe sunanka.
22 Levati, o Dio, dibatti la tua lite; Ricordati dell'oltraggio che ti è fatto tuttodì dallo stolto.
Ka tashi, ya Allah, ka kāre muradinka; ka tuna yadda wawaye suka yi maka ba’a dukan yini.
23 Non dimenticar le grida de' tuoi nemici; Lo strepito di quelli che si levano contro a te sale del continuo [al cielo].
Kada ka ƙyale surutan ban haushi na maƙiyanka, ihun abokan gābanka, waɗanda suke ci gaba da yi.

< Salmi 74 >