< 1 Samuels 10 >

1 Og Samuel tok en oljekrukke og helte den ut over hans hode, og han kysset ham og sa: Nu har Herren salvet dig til fyrste over sin arv.
Sai Sama’ila ya ɗauki’yar kwalabar mai, ya zuba man ɗin wa Shawulu a kansa, ya yi masa sumba yana cewa, “Ubangiji ya keɓe ka shugaba bisa gādonsa.
2 Når du idag går fra mig, skal du møte to menn ved Rakels grav på grensen av Benjamin i Selsah, og de skal si til dig: Aseninnene som du gikk ut for å lete efter, er funnet; din far tenker ikke mere på dem, men er nu urolig for eder og sier: Hvad skal jeg gjøre for å få min sønn igjen?
Sa’ad da ka rabu da ni yau, za ka sadu da mutum biyu kusa da kabarin Rahila a Zelza, a yankin Benyamin. Za su ce maka, ‘An sami jakunan da ka fita nema, yanzu haka mahaifinka ya bar damuwa kan jakunan ya koma damuwa a kanka, yana cewa, yaya zan gan ɗana?’
3 Og når du går videre derfra og kommer til Tabors ek, skal du der møte tre menn som er på vei op til Gud i Betel, en som bærer tre kje, og en som bærer tre brød, og en som bærer en skinnsekk med vin.
“Sa’an nan za ka ci gaba daga nan sai ka kai wajen babban itace na Tabor. Waɗansu mutum uku za su sadu da kai a hanyarsu zuwa wurin yin wa Allah sujada a Betel. Ɗaya yana ɗauke da’yan awaki uku, ɗaya yana ɗauke da burodi uku, ɗayan kuma yana ɗauke da salkar ruwan inabi.
4 De skal hilse på dig og gi dig to brød, og dem skal du ta imot.
Za su gaishe ka, su ba ka burodi biyu, kai kuwa sai ka karɓa.
5 Derefter kommer du til Guds Gibea, hvor filistrene har sine vaktposter; og når du kommer der til byen, skal du treffe på en flokk profeter som kommer ned fra haugen med harpe og tromme og fløite og citar foran sig, og selv er de i en profetisk henrykkelse.
“Bayan wannan, za ka tafi Gebiya ta Allah, inda sansanin Filistiyawa yake. Kana shiga garin, za ka sadu da jerin gwanon annabawa suna gangarowa daga tudu, ana kaɗa garaya, ana bugan ganguna, ana hura sarewa, ana kuma bugan molo, a gabansu, su kuma za su yi ta annabci.
6 Og Herrens Ånd skal komme over dig, så du skal gripes av profetisk henrykkelse likesom de og bli til et annet menneske.
Ruhun Ubangiji zai sauko a kanka da iko, za ka kuma yi annabci tare da su. Za a canja ka ka zama dabam.
7 Når du ser at disse tegn inntreffer, da gjør hvad du får leilighet til! For Gud er med dig.
Da zarar waɗannan alamu sun cika, sai ka aikata duk abin da kana iya yi gama Allah yana tare da kai.
8 Gå du før mig ned til Gilgal, så skal jeg komme ned til dig for å ofre brennoffer og takkoffer; syv dager skal du bie, inntil jeg kommer til dig, og da skal jeg la dig få vite hvad du skal gjøre.
“Ka sha gabana zuwa Gilgal. Lalle zan gangara wurinka domin in miƙa hadaya ta ƙonawa da hadayu na salama. Sai ka jira ni kwana bakwai sai na zo wurinka na kuma gaya maka abin da za ka yi.”
9 Da nu Saul vendte sig og gikk sin vei fra Samuel, da gav Gud ham et annet hjerte, og samme dag traff alle disse tegn inn.
Da Shawulu ya juya zai bar Sama’ila, sai Allah ya canja wa Shawulu zuciya, alamun nan kuwa suka cika a ranar.
10 Da de kom til Gibea, kom en flokk profeter ham i møte; da kom Guds Ånd over ham, og han blev grepet av profetisk henrykkelse midt iblandt dem.
Da suka iso Gibeya, jerin gwanon annabawa suka sadu da shi Ruhun Allah kuma ya sauko a kansa da iko, sai ya shiga yin annabci tare da su.
11 Og da alle de som kjente ham før, så at han var grepet av henrykkelse likesom profetene, da sa folket til hverandre: Hvad er det som har hendt med Kis' sønn? Er også Saul blandt profetene?
Sa’ad da dukan waɗanda suka san shi a dā suka gan shi yana annabci tare da annabawa, sai suka tambayi juna, suka ce, “Me ya faru da ɗan Kish? Shawulu ma yana cikin annabawa ne?”
12 Da svarte en mann derfra og sa: Hvem er da far til disse? Derfor er det blitt til et ordsprog: Er også Saul blandt profetene?
Wani mutumin da yake zama a can ya ce, “Wane ne kuma mahaifinsu?” Ta haka sai wannan ya zama karin magana cewa, “Shawulu ma yana cikin annabawa?”
13 Da hans profetiske henrykkelse hadde hørt op, kom han til offerhaugen,
Bayan da Shawulu ya gama annabci sai ya haura ya tafi tudu.
14 og Sauls farbror sa til ham og hans dreng: Hvor har I vært? Han svarte: Vi har vært ute og lett efter aseninnene, og da vi ikke så noget til dem, gikk vi til Samuel.
Sai ɗan’uwan mahaifin Shawulu ya tambaye shi da baransa ya ce, “Ina kuka je?” Shawulu ya ce, “Mun tafi neman jakuna, amma da ba mu same su ba sai muka tafi wurin Sama’ila.”
15 Da sa Sauls farbror: Kjære, fortell mig hvad Samuel sa til eder!
Ɗan’uwan mahaifin Shawulu ya ce, “Faɗa mini abin da Sama’ila ya ce maka.”
16 Saul svarte sin farbror: Han fortalte oss at aseninnene var funnet. Men det som Samuel hadde sagt om kongedømmet, fortalte han ham ikke.
Shawulu ya ce, “Ya tabbatar mana cewa an riga an sami jakuna.” Amma bai gaya wa ɗan’uwan mahaifinsa abin da Sama’ila ya ce game da sarauta ba.
17 Så kalte Samuel folket sammen til Herren, til Mispa.
Sama’ila ta tattara mutanen Isra’ila a gaban Ubangiji a Mizfa
18 Og han sa til Israels barn: Så sier Herren, Israels Gud: Jeg førte Israel op fra Egypten og fridde eder ut fra egypterne og fra alle de riker som undertrykte eder.
ya ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na fito da Isra’ila daga Masar, na kuma cece ku daga hannun Masarawa da dukan mulkokin da suka wahalshe ku.’
19 Men I har nu forkastet eders Gud, han som frelste eder ut av alle eders ulykker og trengsler, og sagt til ham: Nei, en konge skal du sette over oss! Så still eder nu frem for Herrens åsyn efter eders stammer og ætter!
Amma yanzu kun ƙi Allahnku wanda ya cece ku daga dukan masifu da wahaloli. Kuka ce, ‘Sam, a naɗa mana sarki.’ Saboda haka yanzu sai ku zo gaban Ubangiji kabila-kabila da iyali-iyali.”
20 Så lot Samuel alle Israels stammer gå frem, og loddet falt på Benjamins stamme.
Sa’ad da Sama’ila ya kawo dukan Isra’ila gaba, kabila-kabila, sai aka zaɓi kabilar Benyamin ta wurin jefa ƙuri’a.
21 Så lot han Benjamins stamme gå frem efter sine ætter, og loddet falt på Matris ætt, og derefter falt loddet på Saul, Kis' sønn. Og de lette efter ham, men kunde ikke finne ham.
Sai ya kawo kabilar Benyamin gaba, iyali-iyali, aka zaɓi iyalin Matri. A ƙarshe aka zaɓi Shawulu ɗan Kish. Amma da aka neme shi sai ba a same shi ba.
22 Da spurte de atter Herren: Er det kommet nogen annen hit? Herren svarte: Han holder sig skjult ved trosset.
Suka ƙara nemi bayani daga Ubangiji suka ce, “Mutumin ya zo nan kuwa?” Ubangiji ya ce, “I, ga shi can, ya ɓuya cikin kayayyaki.”
23 Da sprang de avsted og hentet ham derfra, og han gikk frem midt iblandt folket, og han var et hode høiere enn alt folket.
Suka ruga suka kawo shi. Da ya tsaya cikin mutane, sai ya fi kowa tsayi.
24 Og Samuel sa til alt folket: Her ser I ham som Herren har utvalgt! Det er ingen som han blandt alt folket. Da jublet alt folket og ropte: Kongen leve!
Sama’ila ya ce wa dukan mutane, “Kun ga wanda Ubangiji ya zaɓa ko? Ba wani kamar sa a cikin dukan mutane.” Sai mutane suka tā da murya suka ce, “Ran sarki yă daɗe.”
25 Så talte Samuel til folket om kongedømmets rett og skrev det op i en bok; den la han ned for Herrens åsyn. Derefter lot Samuel alt folket fare, hver til sitt hjem.
Sama’ila kuwa ya bayyana wa mutane ƙa’idodin sarauta. Ya rubuta su cikin littafi ya ajiye a gaban Ubangiji. Sa’an nan ya sallame mutane, kowa ya koma gidansa.
26 Saul drog og hjem til Gibea, og med ham fulgte den flokk hvis hjerte Gud hadde rørt ved.
Shawulu ma ya tafi gidansa a Gibeya tare da waɗansu jarumawan da Allah ya taɓa zuciyarsu.
27 Men nogen ugudelige mennesker sa: Hvad hjelp skal denne kunne gi oss? Og de ringeaktet ham og kom ikke med gaver til ham; men han lot som han ikke merket det.
Amma waɗansu’yan iska suka ce, “Yaya wannan mutum zai iya cetonmu?” Suka rena shi suka ƙi su kawo masa kyautai. Amma Shawulu bai ce uffam ba.

< 1 Samuels 10 >