< Mika 3 >

1 Og jeg sa: Hør, I Jakobs høvdinger og I dommere for Israels hus! Er det ikke eders sak å vite hvad rett er?
Sa’an nan na ce, “Ku kasa kunne, ku shugabannin Yaƙub, ku masu mulkin gidan Isra’ila. Ya kamata ku san shari’a,
2 I som hater det gode og elsker det onde, I som flår huden av dem og kjøttet av deres ben,
ku da kuke ƙin abu mai kyau kuke ƙaunar mugunta, ku da kuke feɗe mutanena kuke tuge nama daga ƙasusuwansu;
3 I som eter mitt folks kjøtt og river huden av dem og knuser deres ben og breder dem ut likesom i en gryte og som kjøtt i en panne.
ku da kuke cin naman mutanena, ku feɗe fatar jikinsu kuke kakkarya ƙasusuwansu, kuke yayyanka su gunduwa-gunduwa kamar naman da za a toya, kamar naman da za a sa a dafa.”
4 Da skal de rope til Herren, men han skal ikke svare dem; han skal skjule sitt åsyn for dem på den tid for deres onde gjerningers skyld!
Sa’an nan za su kira ga Ubangiji, amma ba zai amsa musu ba. A wannan lokaci zai ɓoye fuskarsa daga gare su saboda irin muguntar da suka yi.
5 Så sier Herren om de profeter som fører mitt folk vill, som roper når de har noget å tygge med sine tenner: Fred! Men mot den som intet gir dem i deres munn, roper de ut en hellig krig.
Ga abin da Ubangiji ya faɗa, “Game da annabawa masu ɓad da mutanena, in wani ya ciyar da su, sai su ce akwai ‘salama’ amma in bai ciyar da su ba, a shirye suke su kai masa hari.
6 Derfor skal det bli natt for eder uten syner, og mørke uten spådom; solen skal gå ned over profetene, og dagen bli sort over dem.
Saboda haka dare yana zuwa a bisanku, ba tare da wahayi ba, kuma duhu, ba tare da duba ba. Rana za tă fāɗi wa annabawa, yini kuma zai zama musu duhu.
7 Seerne skal skamme sig, og spåmennene blues; de skal tilhylle skjegget alle sammen; for det kommer intet svar fra Gud.
Masu gani za su ji kunya, masu duba kuma za su ji taƙaici. Dukansu za su rufe fuskokinsu gama ba amsa daga Allah.”
8 Men jeg, jeg er full av kraft ved Herrens Ånd og full av rett og styrke til å vidne for Jakob om hans overtredelse og for Israel om hans synd.
Amma game da ni, ina cike da iko ta wurin Ruhun Ubangiji da kuma adalci da ƙarfi, don a sanar da Yaƙub laifofinsa, ga Isra’ila kuma zunubinsa.
9 Hør dette, I høvdinger over Jakobs hus og I dommere for Israels hus, I som avskyr rett og gjør det kroket alt det som er bent,
Ku ji wannan, ku shugabannin gidan Yaƙub, ku masu mulkin gidan Isra’ila, ku da kuke ƙyamar gaskiya, kuka karkatar duk abin da yake na gaskiya;
10 I som bygger Sion med blod og Jerusalem med urett!
kuka gina Sihiyona ta wurin zub da jini, Urushalima kuma ta wurin mugunta.
11 Dets høvdinger dømmer for gave, dets prester lærer for betaling, og dets profeter spår for penger, og enda stoler de på Herren og sier: Er ikke Herren midt iblandt oss? Det kommer ingen ulykke over oss.
Hukunce-hukuncen shugabannin ƙasar na cin hanci ne, firistocinta kuma suna koyarwa don a biya su, annabawanta kuwa suna yin annabci don neman kuɗi. Duk da haka suna jingina a kan Ubangiji suna cewa, “Ba Ubangiji yana tare da mu ba? Ba bala’in da zai zo mana.”
12 Derfor skal for eders skyld Sion pløies som en aker, og Jerusalem skal bli til grusdynger, og tempelberget til skogbakker.
Don haka, saboda ku, za a nome Sihiyona kamar gona, Urushalima kuma ta zama tarin juji, tudun haikali kuwa zai zama kurmin ƙayayyuwa.

< Mika 3 >