< Salmenes 129 >

1 En sang ved festreisene. Meget har de trengt mig fra min ungdom av - så sie Israel -
Waƙar haurawa. Sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, bari Isra’ila yă ce,
2 meget har de trengt mig fra min ungdom av; men de har ikke fått overhånd over mig.
sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, amma ba su yi nasara a kaina ba.
3 Min rygg har plogmenn pløid, de har gjort sine furer lange.
Manoma sun nome bayana suka yi kunyoyinsu da tsayi.
4 Herren er rettferdig, han har avhugget de ugudeliges rep.
Amma Ubangiji mai adalci ne; ya’yantar da ni daga igiyoyin mugaye.
5 De skal bli til skamme og vike tilbake alle de som hater Sion,
Bari dukan waɗanda suke ƙin Sihiyona a juye da su baya da kunya.
6 de skal bli som gress på takene, som er visnet før det blir rykket op:
Bari su zama kamar ciyawa a kan rufi, wadda takan bushe kafin tă yi girma;
7 Høstmannen fyller ikke sin hånd, ei heller den som binder kornbånd, sitt fang.
da ita mai girbi ba ya iya cika hannuwansa, balle wanda yake tarawa yă cika hannuwansa.
8 Og de som går forbi, sier ikke: Herrens velsignelse være over eder, vi velsigner eder i Herrens navn!
Kada masu wuce su ce, “Albarkar Ubangiji ta kasance a kanku; muna sa muku albarka a cikin sunan Ubangiji.”

< Salmenes 129 >