< غزل غزلها 3 >

شبانگاه در بستر خود او را که جانم دوست می دارد طلبیدم. او را جستجو کردم امانیافتم. ۱ 1
Dare farai a kan gadona na nemi wanda zuciyata take ƙauna; na neme shi amma ban same shi ba.
گفتم الان برخاسته، در کوچه‌ها و شوارع شهر گشته، او را که جانم دوست می‌دارد خواهم طلبید. او را جستجو کردم اما نیافتم. ۲ 2
Zan tashi yanzu in zagaya gari, in ratsa titunansa da dandalinsa; zan nemi wanda zuciyata take ƙauna. Saboda haka na neme shi, amma ban same shi ba.
کشیکچیانی که در شهر گردش می‌کنند مرایافتند. گفتم که «آیا محبوب جان مرا دیده‌اید؟» ۳ 3
Masu tsaro suka gamu da ni yayinda suke kai kawo a cikin birni, sai na ce, “Kun ga mini wanda zuciyata take ƙauna?”
از ایشان چندان پیش نرفته بودم که او را که جانم دوست می‌دارد یافتم. و او را گرفته، رها نکردم تابه خانه مادر خود و به حجره والده خویش درآوردم. ۴ 4
Rabuwata da su ke nan sai na sami wanda zuciyata take ƙauna. Na riƙe shi, ban yarda yă tafi ba sai da na kawo shi gidan mahaifiyata, zuwa ɗakin wadda ta yi cikina.
‌ای دختران اورشلیم، شما را به غزالها وآهوهای صحرا قسم می‌دهم که محبوب مرا تاخودش نخواهد بیدار مکنید و برمینگیزانید. ۵ 5
’Yan matan Urushalima, ku yi mini alkawari da bareyi da ƙishimai na jeji. Ba za ku tā da ko ku farka ƙauna ba sai haka ya zama lalle.
این کیست که مثل ستونهای دود از بیابان برمی آید وبه مر و بخور و به همه عطریات تاجران معطراست؟ ۶ 6
Wane ne wannan mai zuwa daga hamada kamar tunnuƙewar hayaƙi, cike da ƙanshin turaren mur da lubban da aka yi da kayan yajin’yan kasuwa?
اینک تخت روان سلیمان است که شصت جبار از جباران اسرائیل به اطراف آن می‌باشند. ۷ 7
Duba! Abin ɗaukar Solomon ne, jarumawa sittin suke rakiya, zaɓaɓɓun sojojin Isra’ila,
همگی ایشان شمشیر گرفته و جنگ آزموده هستند. شمشیر هر یک به‌سبب خوف شب بر رانش بسته است. ۸ 8
dukansu suna saye da takobi dukansu ƙwararru ne a yaƙi, kowanne da takobinsa a rataye a gefensa, a shirye don abubuwan bantsoro na dare.
سلیمان پادشاه تخت روانی برای خویشتن از چوب لبنان ساخت. ۹ 9
Sarki Solomon ya yi wa kansa abin ɗauka; ya yi shi da katako daga Lebanon.
ستونهایش را از نقره و سقفش را از طلا وکرسی‌اش را از ارغوان ساخت، و وسطش به محبت دختران اورشلیم معرق بود. ۱۰ 10
An yi sandunansa da azurfa, aka yi ƙasarsa da zinariya. An lulluɓe wurin zaman da zanen shunayya,’yan matan Urushalima sun yi mata irin yayen da ake yi na ƙauna.
‌ای دختران صهیون، بیرون آیید و سلیمان پادشاه راببینید، با تاجی که مادرش در روز عروسی وی ودر روز شادی دلش آن را بر سر وی نهاد. ۱۱ 11
Fito, ku’yan matan Sihiyona, ku ga Sarki Solomon yana saye da rawani, rawanin da mahaifiyarsa ta naɗa masa, a ranar aurensa, a ranar da zuciyarsa ta yi farin ciki.

< غزل غزلها 3 >