< João 13 >

1 Ora, antes da festa da paschoa, sabendo Jesus que já era chegada a sua hora de passar d'este mando para o Pae, como havia amado os seus, que estavam no mundo, amou-os até ao fim.
Kamin bukin idin ketarewa, sa'adda Yesu ya san lokaci ya yi da zai tashi daga wannan duniya zuwa wurin Uba, da yake ya kaunaci nasa wadanda ke duniya- ya kaunace su har karshe.
2 E, acabada a ceia, tendo já o diabo insinuado no coração de Judas Iscariotes, filho de Simão, que o trahisse,
Iblis ya rigaya ya sa a zuciyar Yahuza Iskariyoti dan Saminu, ya bashe da Yesu.
3 Jesus, sabendo que o Pae tinha depositado nas suas mãos todas as coisas, e que havia saido de Deus e ia para Deus,
Ya san cewa Uba ya bada kome a hannunsa, kuma ya zo daga wurin Allah, kuma zai koma wurin Allah.
4 Levantou-se da ceia, tirou os vestidos, e, tomando uma toalha, cingiu-se.
Ya tashi daga cin abincin, ya tube tufafinsa, ya dauki tawul ya lullube kansa da shi.
5 Depois deitou agua n'uma bacia, e começou a lavar os pés aos discipulos, e a enxugar-lh'os com a toalha com que estava cingido.
Sa'an nan ya zuba ruwa a bangaji, ya fara wanke kafafun almajiran, yana shafe su da tawul din da ya lullube jikinsa da shi.
6 Approximou-se pois de Simão Pedro, e elle lhe disse: Senhor, tu lavas-me os pés a mim?
Ya zo wurin Bitrus Saminu, sai Bitrus ya ce masa,”Ubangiji, za ka wanke mani kafa?”
7 Respondeu Jesus, e disse-lhe: O que eu faço não o sabes tu agora, mas tu o saberás depois.
Yesu ya amsa ya ce, “Abin da nake yi ba za ka fahimce shi yanzu ba, amma daga baya za ka fahimta.”
8 Disse-lhe Pedro: Nunca me lavarás os pés. Respondeu-lhe Jesus: Se eu te não lavar, não tens parte comigo. (aiōn g165)
Bitrus ya ce masa, “Ba za ka taba wanke mani kafa ba.” Yesu ya amsa masa ya ce, “In ban wanke maka ba, ba ka da rabo da ni”. (aiōn g165)
9 Disse-lhe Simão Pedro: Senhor, não só os meus pés, mas tambem as mãos e a cabeça.
Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, ba kafafuna kadai za ka wanke ba, amma da hannayena da kaina.”
10 Disse-lhe Jesus: Aquelle que está lavado não necessita de lavar senão os pés, pois no mais todo está limpo. Ora vós estaes limpos, mas não todos.
Yesu ya ce masa, “Duk wanda ya yi wanka ba ya da bukata, sai dai a wanke kafafunsa, amma shi tsarkakakke ne baidaya; ku tsarkakakku ne, amma ba dukanku ba.”
11 Porque bem sabia elle quem o havia de trahir; por isso disse: Nem todos estaes limpos.
(Don Yesu ya san wanda zai bashe shi, shiyasa ya ce, “Ba dukanku ne ke da tsarki ba.”)
12 Depois que lhes lavou os pés, e tomou os seus vestidos, tornou-se a assentar á mesa, e disse-lhes: Entendeis o que vos tenho feito?
Bayan Yesu ya wanke masu kafafu, ya dauki tufafinsa ya zauna kuma, ya ce masu, “Kun san abin da na yi muku?
13 Vós me chamaes Mestre e Senhor; e dizeis bem, porque eu o sou:
kuna kirana, 'Malam, da Ubangiji,' kun fadi daidai, don haka Nake.
14 Pois se eu, Senhor e Mestre, vos lavei os pés, vós deveis tambem lavar os pés uns aos outros.
Idan ni Ubangiji da kuma mallam, na wanke maku kafafu, ya kamata kuma ku wanke wa junan ku kafafu.
15 Porque eu vos dei o exemplo, para que, como eu vos fiz, façaes vós tambem.
Gama na baku misali, saboda ku yi yadda na yi maku.
16 Na verdade, na verdade vos digo que não é o servo maior do que o seu senhor, nem o enviado maior do que aquelle que o enviou.
Lalle hakika ina gaya muku, bawa ba ya fi mai gidansa girma ba; dan aike kuma ba ya fi wanda ya aiko shi girma ba.
17 Se sabeis estas coisas, bemaventurados sois se as fizerdes.
Idan kun san wadannan abubuwa, ku masu albarka ne idan kun aikata su.
18 Não fallo de todos vós; eu bem sei os que tenho escolhido; mas para que se cumpra a Escriptura, que diz: O que come o pão comigo levantou contra mim o seu calcanhar.
Ba ina magana akan dukanku ba; Na san wadanda na zaba. Amma domin Nassi ya cika: 'Shi Wanda ya ci gurasata, ya tayar mani'.
19 Já agora vol-o digo, antes que aconteça, para que, quando acontecer, acrediteis que eu sou.
Ina fada maku wannan yanzu tun kafin haka ta faru domin sa'adda ta faru, ku gaskata Ni ne.
20 Na verdade, na verdade vos digo que, se alguem receber o que eu enviar, me recebe a mim, e quem me recebe a mim recebe aquelle que me enviou.
Hakika, hakika, Ina gaya maku, wanda ya karbi wanda na aiko, Ni ya karba, wanda kuma ya karbe ni, ya karbi wanda ya aiko ni.
21 Tendo Jesus dito isto, turbou-se em espirito, e testificou, e disse: Na verdade, na verdade vos digo que um de vós me ha de trahir.
Bayan Yesu ya fadi haka, ya damu a ruhu, ya yi shaida ya ce, “Lalle hakika, ina gaya muku cewa daya daga cikinku zai bashe ni.”
22 Então os discipulos olhavam uns para os outros, duvidando de quem elle fallava.
Almajiran suka kalli juna, suna juyayin ko akan wa yake magana.
23 Ora um de seus discipulos, aquelle a quem Jesus amava, estava reclinado no seio de Jesus.
Daya daga cikin almajiransa, wanda Yesu yake kauna, yana a teburi, jingine a kirjin Yesu.
24 Então Simão Pedro fez signal a este, para que perguntasse quem era aquelle de quem elle fallava.
Siman Bitrus ya ce wa almajirin, “ka fada mana ko akan wa ya ke magana.”
25 E, inclinando-se elle sobre o peito de Jesus, disse-lhe: Senhor, quem é?
Sai ya sake jingina a kirjin Yesu, ya ce masa, “Ubangiji, wanene?”
26 Jesus respondeu: É aquelle a quem eu der o bocado molhado. E, molhando o bocado, o deu a Judas Iscariotes, filho de Simão.
Sannan Yesu ya amsa, “Shine wanda zan tsoma gutsuren gurasa in ba shi.” Sannan bayan ya tsoma gurasar, sai ya ba Yahuza Dan Siman Iskariyoti.
27 E, após o bocado, entrou n'elle Satanás. Disse pois Jesus: O que fazes, fal-o depressa.
To bayan gurasar, sai shaidan ya shige shi, sai Yesu ya ce masa, “Abinda kake yi, ka yi shi da sauri.”
28 E nenhum dos que estavam assentados á mesa comprehendeu a que proposito lhe dissera isto;
Babu wani a teburin da ya san dalilin dayasa ya fada masa wannan.
29 Porque, como Judas tinha a bolsa, pensavam alguns que Jesus lhe tinha dito: Compra o que nos é necessario para a festa; ou que désse alguma coisa aos pobres.
Wadansu sun yi tsamanin cewa, tun da Yahuza ne ke rike da jakkar kudi, Yesu ya ce masa, “Ka sayi abinda muke bukata don idin”, ko kuma ya bada wani abu domin gajiyayyu.
30 E, tendo tomado o bocado, saiu logo. E era já noite.
Bayan Yahuza ya karbi gurasar, sai ya fita nan da nan. Da daddare ne kuwa.
31 Tendo elle pois saido, disse Jesus: Agora é glorificado o Filho do homem, e Deus é glorificado n'elle.
Bayan Yahuza ya tafi, Yesu ya ce, “Yanzu an daukaka Dan mutum, kuma an daukaka Allah a cikinsa.
32 Se Deus é glorificado n'elle, tambem Deus o glorificará em si mesmo, e logo o ha de glorificar.
Allah zai daukaka shi a cikin kansa, kuma zai daukaka shi nan da nan.
33 Filhinhos, ainda por um pouco estou comvosco. Vós me buscareis, e, como tinha dito aos judeos: Para onde eu vou não podeis vós ir: assim vol-o digo eu tambem agora.
'Ya'ya kanana, ina tare da ku na wani gajeren lokaci. Zaku neme ni, kuma kamar yadda na fadawa Yahudawa, 'in da zan tafi ba za ku iya zuwa ba.' Yanzu kuma na fada maku wannan.
34 Um novo mandamento vos dou: Que vos ameis uns aos outros, como eu vos amei a vós, que tambem vós uns a outros vos ameis.
Ina baku sabuwar doka, ku kaunaci juna; kamar yadda na kaunace ku, haka kuma ku kaunaci juna.
35 N'isto todos conhecerão que sois meus discipulos, se vós tiverdes amor uns aos outros.
Ta haka kowa zai san ku almajiraina ne, idan kuna kaunar juna.”
36 Disse-lhe Simão Pedro: Senhor, para onde vaes? Jesus lhe respondeu: Para onde eu vou não podes agora seguir-me, porém depois me seguirás.
Siman Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, ina za ka?” Yesu ya amsa ya ce, “Inda za ni, ba zaka iya bi na ba yanzu, amma zaka bini daga baya.”
37 Disse-lhe Pedro: Porque não posso seguir-te agora? Por ti darei a minha vida.
Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, don me ba zan iya binka a yanzu ba? Zan bada raina domin ka.”
38 Respondeu-lhe Jesus: Tu darás a tua vida por mim? Na verdade, na verdade te digo: não cantará o gallo emquanto me não tiveres negado tres vezes.
Yesu ya amsa ya ce, “Za ka bada ranka domina? Lalle hakika, ina gaya maka, kafin zakara ya yi cara zaka yi musu na sau uku.”

< João 13 >