< Mark 6 >

1 Jisua'n ha mun hah a mâka, a omna ngâi khopui tieng a se nôka, a ruoisingei khomin an jûi tita.
Ya bar su ya zo garinsu, almajiransa su ka biyo shi.
2 Sabbathnin chu Synagog taka mi a minchua. Mahan mi tamtak an oma; male a chongril hah an riet lehan anrêngin kamâm aom tatak an tia, “Hi mi hin hi ngei nâm hih kho renga mo a man hi?” an tia. “A kôm, khoi vârna mo pêkin aom hih? Kho angin mo sininkhêlngei a sin thei hi?
Sa'adda ranar Asabar tazo ya shiga cikin masujada ya yi koyarwa. Mutane da yawa da su ka ji koyarwarsa su ka yi mamaki, suka ce daga ina ya sami irin wannan koyarwar? Wacce irin hikima ce Allah ya ba shi haka? Wadanne irin ayyukan al'ajibi ya ke yi da hannuwansa?
3 Mary nâipasal, mistri sin ngâi, a lâibungngei khom Jacob, Joseph, Juda le Simon ngei nimak mo? A sarnungei khom ei kôma an om ngâi nimak ngei mo?” an tia. Male chu ama hah an hengpai zoia.
Wannan ba kafintan nan ba ne dan Maryamu, dan'uwan Yakubu da Yosi da Yahuza da Saminu? Ba ga 'yan'uwan sa 'yan mata mu na tare da su ba? Ba su ji dadi ba a ransu saboda Yesu.
4 Jisua'n an kôm, “Dêipungei chu an omna ngâi khopui le a sûngsuokngei le a insûngmingei lâia tiloiin chu muntina an jâ ngei ngâi a tia.”
Yesu ya ce, “Annabi ba ya rasa daraja sai a gidansa da garinsa da cikin danginsa.”
5 Ha muna han chu mi damloi ngei tômte chunga a kutngei minngamin a mindam tiloiin chu ite sininkhêlngei sin thei khâi mak.
Bai iya yin wani aikin al'ajibi a wurin ba sai dai mutane kadan marasa lafiya ya dorawa hannu ya warkar da su.
6 Mingei han taksônna an dôn loi sikin a jâmminzal sabaka. Hanchu Jisua'n ha revêla khuongei han a chai titira, mingei ha a minchu tira.
Rashin bangaskiyarsu ya ba shi mamaki. Sai ya tafi cikin kauyuka na kewaye da su ya yi ta koyarwa.
7 Ruoisi sômleinik ngei hah a koi mintûp ngeia inik, inikin a tîrsuoka. Ratha saloingei chunga rachamneina a pêk ngeia,
Ya kira almajiransa su goma sha biyu, ya aike su biyu-biyu, ya ba su iko a kan aljanu,
8 male an kôm, “Nin khuolchaina khiengrol tiloiin chu ite vâipôl khom, kutdo choli khom, nin pepngeia sum khom chôi no roi.
ya dokace su kada su dauki komai tare da su domin wannan tafiya, sai dai sanda kadai. Kada su dauki abinci ko jaka ko kudi a cikin aljihunsu,
9 Kebunngei chu bun ungla, hannirese, kâncholi inshak chu chôi no roi” tiin chong a pêk ngeia.
sai dai su sa takalmi kadai, kada su sa taguwa biyu a jikinsu.
10 Amananâkin an kôm, “Nangni an lei modômna ina han om ungla ma mun hah nin mâk, mâka chu madên han om tit roi.
Ya ce da su, idan ku ka shiga wani gida sai ku zauna a gidan har lokacin da za ku tashi.
11 Hanchu tu khopui khom mingeiin nangni an modôm noa, nin chong an rangâi nônchu mâkrak ungla, nin ke rabab akop ngei hah không liei roi. Maha anni rangin inning roi tina nîng atih.”
Idan ku ka je wani gari aka ki karbar ku, ku karkabe kurar da ke kafufunku ta zama shaida kan mutanen garin.
12 Masikin an sea, male mingeiin an sietnangei renga an insîr theina rangin thurchi an misîra.
Sai suka tafi suka yi ta shela ga mutane cewa su tuba daga zunubansu.
13 Ramkhoringei tamtak an rujûl pâia, male damloi tamtak ngei olive sariek an pola an mindam ngei zoi.
Sun fitar da aljanu da yawa, suka shafawa mutane da yawa mai suka warkar da su.
14 Hanchu Jisua riming muntina ânthang zit zoi sikin Rêng Herod'n a lei rieta. Mingei senkhatin chu, “Baptispu John hah a hong ring nôk zoi! Masika han hi sininkhêlngei sin theina ranak hi a dôn ani,” an tia.
Sarki Hirudus ya ji wannan, gama sunan Yesu ya zama sananne a wurin kowa da kowa. Wadansu suna cewa Yahaya mai yin baftisma ne ya tashi daga matattu shi ya sa ake yin wadannan ayyukan al'ajibi ta wurinsa.
15 Nikhomrese, adangngeiin chu, “Ama hih Elijah ani” an tia. Midangngei an ti nôk chu “Tiena dêipungei angin, ama hih dêipu inkhat ani” an tia.
Wadansu kuma suna cewa, “Iliya,” Har yanzu wadansu suna cewa daya “daga cikin annabawa ne na da can.”
16 Mahah a lei rieta, Herod'n chu, Baptispu John ani! “A lu ka tana nikhomrese, a hong ring nôk ani!” a tia.
Sa'adda Hirudus ya ji wannan sai ya ce, “Yahaya wanda na fillewa kai shine ya tashi.”
17 Herod lelên John hah a minsûra, khitbelin jêl ina a lei khum ani. Herod'n ma anga a thona chu, Herodias hi a nâipa Philip lômnu nikhomsenla a lômnu a minchang sika ani.
Saboda Hirudus ne ya sa aka kama Yahaya aka kulle shi a kurkuku saboda Hirodiya( matar Filibus dan'uwansa), domin ya aure ta.
18 John'n Herod kôm, “Na nâipa lômnu in ne neipui nôk hih Balam nimak!” tiin a lei ril tit ngâia.
Saboda Yahaya ya gaya wa Hirudus cewa bai halarta ya auri matar dan'uwansa ba.
19 Masikin Herodias han John a mumâka that ngêt rang a bôka hannirese, Herod sikin that thei maka.
Sai ita Hirodiya ta yi kudurin ta kashe Yahaya amma bai yiwu ba.
20 Herod'n John hah mi sa le mi inthieng ani ti a riet sikin a chia, masikin a mojôk ngâi ani. John chongril a riet racham asân injêlpui ngâi khomsenla, a chongril rangâi rang a nuom ngâi ani.
Domin Hirudus yana jin tsoron Yahaya, domin ya sani shi mai adalci ce, mai tsarki kuma. Domin haka Hirudus bai so wani abu ya faru da Yahaya ba, amma ya kan fusata idan ya ji wa'azin yahaya. Duk da haka da fari ciki yakan saurare shi.
21 Azoinataka chu Herod suokni ahong tungin chu, sorkar ulienngei, râlmi ulienngei le Galilee rama mi lienngei rangin bukhalâi otna a minsûka, ha ni han chu Herodias'n chuminrên a mana.
Amma sai dama ta samu inda Hirodiya za ta iya yin abin da ta ke so ta yi. A lokacin kewayowar ranar haihuwar sa, sai Hirudus ya shirya liyafa domin manyan da ke aiki tare da shi a cikin gwamnatin sa, da shugabannin da ke cikin Galili.
22 Herodias nâinupang a hong lûta, a lâma, Herod le a khuolmingei râiaminsân pe ngei oka. Masikin rêngpa han nupangte kôm han, “Imo dôn rang nu nuom? Nu nuom tak nang pêk ki tih” a tia.
Diyar Hirodiya ta zo ta yi masu rawa, rawarta kuwa tagamshi Hirudus da bakinsa. Sarki ya ce da yarinyar, “ki tambayi duk abin da ki ke so ni kuwa zan ba ki shi”.
23 Chonginkhâm tamtak dônin a kôm, “Kho khoi khom mi ni zong kai chu ke rêngram phalkhat tena khom nang pêk rangin chong kên khâm!” a tia.
Ya rantse mata da cewa”Ko menene ki ka ce ki na so, ko da rabin mulkina ne”
24 Masikin nupangte hah a jôka, a nû kôm, “Imo mo ko zong rang?” tiin a va rekela. A nu'n, “Baptispu John lu” tiin a thuona.
Sai ta fita ta je ta tambayi mamarta, “me zan ce ya bani?” Sai ta ce kan Yahaya Mai Yin Baftisma.
25 Nupangte hah innottakin a kîra, rêngpa kôm han, “Atûn Baptispu John a lu mâirânga mi ni pêk rangin ku nuom” tiin a zonga.
Sai ta dawo da sauri cikin dakin taro wurin sarki ta ce da shi, “Ina so ka ba ni kan Yahaya Mai Yin Baftisma a cikin tire.”
26 Masikin rêngpa hah ân ngûikhak zoia, aniatachu a khuolmingei makunga inkhâmnangei a lei tho sika han mângti thei khâi maka.
Sarki ya damu kwarai, amma saboda ya yi alkawari ga kuma ofisoshinsa, ba dama ya ce a'a.
27 Masikin rêngpa han a rungpu inkhat a tîr kelena, John lu hong lâk rangin chong a pêka. Rungpu han ânphêt kelena, male jêl ina a sea. John lu ava tana;
Sai sarki ya aiki wani soja ya ba shi ummurni ya je ya kawo kan Yahaya. Sojan ya je ya fillo kan sa daga cikin kurkuku.
28 hanchu mâirânga a hong chôia, nupangte kôm a pêka, nupangte han a nû kôm ava pêk zoia.
Ya kawo kan a cikin tire ya ba yarinyar, yarinyar kuma ta kai wa mamarta.
29 Ma roi hah a ruoisingeiin an riet lehan an honga, John ruok hah an chôia, male an phûm zoi.
Da almajiran su ka ji labari, suka zo suka dauki gawarsa suka rufe a cikin kabari.
30 Tîrtonngei hah an kîr nôka male Jisua an intongpuia, male an sintho murdi le an minchu sai murdi Jisua kôm an rila.
Almajiran suka zo wurin Yesu, suka fada masa dukkan abin da suka yi da abin da suka koyar.
31 Mingei ha ase le ahong an tam rai sikin Jisua le a ruoisingei chu bunêk zora luo man mak ngeia. Masikin an kôm, “Tho ei theivaia ei om theina rangin mun senkhata chomola nin inngam theina rang muna se rei u” a tia.
Sai ya ce da su “ku je cikin kebabben wuri domin ku huta kadan,” domin mutane suna ta kaiwa da komowa, ba su sami damar hutawa ba balle su ci abinci
32 Masikin mun inthimngangna panin an theiviekin rukuonga an se zoia.
Sai suka tafi kebabben wuri a cikin jirgin ruwa su kadai.
33 Nikhomrese, mingei tamtakin an selâi an mua, anni ngei ti an riet kelena; masikin khopuingei murdi renga mingei hah tâng tieng renga an tânna, Jisua le a ruoisingei hah an lei chomtan ngeia.
Amma mutane da yawa sun gansu suna tafiya sun kuma gane su, sai suka fito daga cikin dukan garuruwa da gudu har su ka kai wurin kafin su zo.
34 Jisua hah rukuong renga a juong chum lehan, loko tamtak a mu ngeia, male belri a hôlpu boi angin an ni sikin, anni ngei rangin a mulungrîla inriengmuna leh asipa. Masikin neinun tamtak ngei a minchu ngei phut zoi.
Sa'adda suka zo bakin gaba Yesu ya ga taron mutane da yawa sai ya ji tausayinsu domin sun yi kamar tumakin da ba da mai kiwo. Sai ya cigaba da koya masu abubuwa da yawa.
35 Kholoi ahongni lehan, a ruoisingei hah Jisua kôm an honga, male a kôm, “Mahi mun inthimngang ke ania, nisa khom ase ok zoia.
Sa'adda yamma ta yi, almajiran sa suka zo suka ce da shi, “wurinnan kebabben wuri ne kuma ga lokaci ya tafi.
36 Mingei hih tîr pai ngei inla, male akôl kienga loingeia mo, khuongeia mo, anninanâkin an sâkruo imakhat an rochôk theina rangin” an tia.
Ka sallami mutanen nan domin su shiga cikin garuruwa da kauyuka da ke kusa domin su sayi abin da zasu ci.
37 Jisua'n an kôm, “Nangnin sâkruo imakhat pêk ngei roi,” tiin a thuon ngeia. Annin a kôm, “Anni ngei vâi theina rangin vâipôl chunga duli razannik kin va thâm rangin nu nuom mo?” tiin an rekela.
Amma sai ya ba su amsa ya ce,”Ku ku basu abinci su ci mana”. Sai suka ce da shi, “ma iya zuwa mu sawo gurasa ta sule dari biyu mu basu su ci?”
38 Masikin Jisua'n an kôm, “Vâipôl kho dôr mo nin dôn? Se ungla, va en roi” tiin a rekel ngeia. An dôn dôr hah an riet lehan, “Vâipôl rangnga le nga inik” tiin an rila.
Sai ya ce dasu, “Dunkulen gurasa guda nawa kuke dasu? Kuje ku gani.” Dasuka gano sai suka ce da shi, dunkule biyar ne da kifi guda biyu.”
39 Hanchu Jisua'n mingei nâm hah apâl apâlin sensâi ungla, durba chunga min sung ngei rangin ruoisingei a ril ngeia.
Sai ya ba da umarni mutanen su dukka su zauna a kan danyar ciyawa.
40 Masikin mingei hah apâl apâlin, raza khat pâlin le sômrangnga pâlin an min sung ngeia.
Suka zauna kungiya kungiya wadansu su dari wadansu hamsin.
41 Hanchu Jisua'n vâipôl rangnga ngei le nga inik hah a lâka, invân tieng tangin Pathien kôm râisânchong a rila. Vâipôl hah a khoia, mingei hah sem pe ngei rangin a ruoisingei kuta a pêk ngeia. Nga khom hah anrêngin sem ngei rangin a pêk ngei sa zoi.
Sai ya dauki dunkulen gurasa guda biyar da kifi guda biyu, ya ta da kansa sama, yasa albarka, ya kakkarya dunkulen gurasan, ya ba almajiran domin su rabawa taron jama'a duka.
42 Mitinin an sâka male an khop chita.
Dukansu suka ci suka koshi.
43 Hanchu an sâk minieng vâipôl hâr le nga ronôi hah tabong sômleinik ruoisingeiin an rût min sipa.
Suka tattara gutsattsarin gurasar suka cika kwanduna guda goma sha biyu da gutsattsarin da kuma gutsattsarin kifin.
44 A vâi ngei mijôn hah mi ulien kai isâng rangnga an ni.
Mutanen da suka ci gurasar sun kai mutum dubu biyar.
45 Lokongei a minchîn suole harenghan varâl tienga Bethsaida khuoa, a motona lei se rangin a ruoisingei rukuonga a min chuong ngeia.
Nan da nan ya ce almajiran sa su hau jirgin ruwa su yi gaba kafin ya zo, su je Baitsaida. Shi kuma ya tsaya domin ya sallami taron mutanen.
46 Mingei hah chonghoiin a mathân suole chu chubaitho rangin muol chunga a se zoia.
Bayan da suka tafi shi kuma ya hau kan dutse domin ya yi addu'a.
47 Kholoi ahongni lehan, rukuong hah dîl ânlâina taka aoma, Jisua chu atheivaiin tânga han aoma.
Har yamma ta yi jirgin ruwan ya na tsakiyar rafi shi kuma yana kan tudu shi kadai.
48 Phâivuo hah anôk tieng asêm sikin, a ruoisingeiin an rukuong jâp hah an mulungjîng okin a mua; masikin jîng kôlinsaluom rangtôn dîl chunga lônin an tieng a hong pana, anni ngei khêlpai rang angin aoma,
Ya gansu suna wahala gama iska ta hana su tafiya. Wajan karfe hudu na asuba sai ya tawo wurin su yana tafiya a kan ruwa, yana so ya wuce gaban su.
49 hannirese anni han tui chunga a lôn an mua. “Mirluoi kêng ani!” tiin an mindonna, male an iniek raka.
Sa'adda suka gan shi ya na tafiya a kan ruwa suka yi tsammani fatalwa ce, suka yi ihu,
50 Ama an mu lehan an rêngin an rathatâka. Harenghan Jisua'n an kôm, “Hâitakin om roi!” ama'n, “Keima ke ki ni, chi no roi!” a tipe ngeia.
gama su duka sun gan shi, tsoro ya kama su. Sai nan da nan ya yi magana dasu ya ce, “Ku karfafa ni ne! kada ku ji tsoro!''
51 Hanchu an kôm rukuonga han a chuong sa zoia, male phâivuo hah amonga. Ruoisingei chu an kamâm sabaka,
Ya shiga cikin jirgin ruwan tare dasu, sai iska ta dena bugawa. Sai suka yi mamaki kwarai.
52 mi isâng rangnga a vâina roi aomtie diktak hah an rietthei loi sikin; an mulungbôkngei han amanphâk loi ani.
Gama basu gane batun dunkulen ba. Maimakon haka, sai zukatansu suka taurare.
53 Dîl râl an inkânna, Genesaret rama an tunga, mahan an rukuong an thunga.
Sa'adda suka haye su zo kasar Janisarita suka sa wa jirgin sarka.
54 Rukuong renga an chuma, mingeiin harenghan Jisua ani ti an riet kelena.
Su na fitowa daga cikin jirgin kenan, mutane suka gane cewa Yesu ne.
55 Ha ram pumpuia mingei hah an hong tân leta; a omna an rietna tena a kôm damloingei an jâmphera jâl pumin an hong rojôna.
Mutane suka ruga cikin yankin su, suka kawo marasa lafiya a bisa shinfidun su zuwa wurinsa, dukan inda suka ji yana zuwa.
56 Male Jisua a sena muntina, khuongeia mo, khopuingeia mo, loingeia mo, bazar munngeia khom damloingei an hong tuonga, a puonmor luo tôn thei rangin phalna an ngênna. Male a tôn ngei murdi chu an dam pak ani.
Ko ina ya shiga birni da kauye, ko a cikin kasar sukan kawo marasa lafiya a kasuwanni suna rokonsa su taba ko da habar rigarsa, dukan wadanda suka taba kuwa suka warke.

< Mark 6 >