< Job 18 >

1 Y respondió Baldad Sujita, y dijo:
Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2 ¿Cuándo pondréis fin a las palabras? Entendéd, y después hablemos.
“Yaushe za ka gama maganganun nan? Ka dawo da hankalinka sa’an nan za mu iya yin magana.
3 ¿Por qué somos tenidos por bestias? ¿en vuestros ojos, somos viles?
Don me muke kamar shanu a wurinka, ka ɗauke mu mutanen wofi?
4 Oh tú que despedazas tu alma con tu furor, ¿será dejada la tierra por tu causa, y serán traspasadas las peñas de su lugar?
Kai da ka yayyage kanka don haushi, za a yashe duniya saboda kai ne? Ko kuma duwatsu za su matsa daga wurinsu?
5 Ciertamente la luz de los impíos será apagada, y la centella de su fuego no resplandecerá.
“An kashe fitilar mugu; harshen wutarsa ya daina ci.
6 La luz se oscurecerá en su tienda, y su candil se apagará sobre él.
Wutar cikin tentinsa ta zama duhu; fitilar da take kusa da shi ta mutu.
7 Los pasos de su potencia serán acortados, y su mismo consejo le echará a perder.
Ƙarfin takawarsa ya ragu; dabararsa ta ja fāɗuwarsa.
8 Porque red será echada en sus pies, y sobre red andará.
Ƙafafunsa sun kai shi cikin raga, yana ta yawo a cikin ragar.
9 Lazo prenderá su calcañar: esforzará contra él a los sedientos.
Tarko ya kama ɗiɗɗigensa; tarko ya riƙe shi kam.
10 Su cuerda está escondida en la tierra, y su orzuelo sobre la senda.
An ɓoye masa igiya da za tă zarge shi a ƙasa; an sa masa tarko a kan hanyar da zai bi.
11 De todas partes le asombrarán temores; y con sus mismos pies le ahuyentarán.
Tsoro duk ya kewaye shi ta kowane gefe yana bin shi duk inda ya je.
12 Su fuerza será hambrienta, y a su costilla estará aparejado quebrantamiento.
Masifa tana jiransa; bala’i yana shirye yă fāɗa masa a lokacin da zai fāɗi.
13 Comerá los ramos de su cuero, y el primogénito de la muerte tragará sus miembros.
Ya cinye wani sashe na gaɓar jikinsa; ɗan fari na mutuwa ya cinye ƙafafunsa.
14 Su confianza será arrancada de su tienda, y le harán llevar al rey de los espantos.
An yage shi daga zaman lafiyar da yake yi a cikin tentinsa aka sa shi tsoro sosai.
15 En su misma tienda morará como si no fuese suya: piedrazufre será esparcida sobre su morada.
Wuta ta cinye tentinsa; farar wuta ta rufe wurin da yake zama.
16 Abajo se secarán sus raíces, y arriba serán cortados sus ramos.
Jijiyoyinsa sun bushe a ƙasa rassansa sun mutu a sama.
17 Su memoria perecerá de la tierra, y no tendrá nombre por las calles.
An manta da shi a duniya; ba wanda yake ƙara tunawa da shi.
18 De la luz será lanzado a las tinieblas, y será echado del mundo.
An tura shi daga cikin haske zuwa cikin duhu, an kore shi daga duniya.
19 No tendrá hijo ni nieto en su pueblo, ni sucesor en sus moradas.
Ba shi da’ya’ya ko zuriya cikin mutanensa, ba sauran wanda yake a raye a wurin da ya taɓa zama.
20 Sobre su día se espantarán los por venir, y a los antiguos tomarán pavor.
Mutanen Yamma suna mamakin abin da ya faru da shi; tsoro ya kama mutanen gabas.
21 Ciertamente tales son las moradas del impío, y este es el lugar del que no conoció a Dios.
Ba shakka haka wurin zaman mugun mutum yake, haka wurin zaman wanda bai san Allah ba yake.”

< Job 18 >